AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE
“Kul na haneki da wanna tinanin Dan Babu inda Zaki….
Karbe zancen Abdul yayi da cewa
“Har sai kin fada? Ni hauka nakeyi zanje da ita gurinsa”
Tana Jin Hakan ta Bata fuska tana komawa jikin dadah din ta kwanta tana kokarin fara Hawaye Hafiz Dake gefen Babbah Yana rubuta text yace
“Kina tsiyayo Hawaye a gurin Nan saina fasa ruwan idonki Daya muga karshen hawayen rainin wayo.”
Katsesa babba yayi da cewa
“Ba zataiba ta fasa”
Maida kallansa yayi kan Ameenatoun Yana cewa
“Mayar da abinki yar budurwan gidan Babbah tare zamu dubosa idan naje ai kaman kinje ne ko??”
Gyada Kai tayi tana mayar da hawayenta tana hararan inda Hafiz yake zaune Yana jifanta da tasa hararar me zafi Shima.
Saida sukai sallah sukaci abinci dayake Babbah baida gurin zuwa ranar sai suka fita tareda Abdul din Dan dubo Haroon din.
******Isarsu yayi daidai da isowan Alh Mam seelah Wanda tin a masaukin Haroon din ya tabbatarda Haroon Baya cikin cikakkiyar hankalinsa me amfani Dan kuwa duk kyau da tsananin tsadan hotel din ganin yayi ‘dan cikinsa jinin Seelahs yafi karfin zama yayi rayuwa a gurin Amma sbd ba shine ya kawosa ba abinda ya kawosa yafi wannan mahimmanci a yanzu.
Babban abinda yasa yake fatan ganawar gaske suyi budaddiyar wasika da Haroon din shine yasan Lameenu akan lamari na faduwa bayada hakuri,
Bayason abinda zai Saka Lameenu ya kasa hakurin dazai iya aikata wani abin batareda saninsu ba Dan idan har zaisa abibiya lamuran Haroon din batareda saninsa ba zai iya rashin hakurin yin wani abun batareda saninsa ba haka zalika alkawarinsu ne dayake yawo a jininsu Dan zuciyarsu kowa ya shiga hanyar shiga tsakaninsu da arzikinsu ciresa sukeyi daga hanyar kwata kwata Dan haka yake buqatan Saka hankali acikin tosashiyar kwakwalwan Haroon din idan ba Hakan ba zai barwa lameenu kulawa da komai Wanda yasan me Hakan ke nufi.
Su babbah ne suka Riga Mam din isowa Dan haka ko ganinsa Basu samu yi ba Yana bedroom dinsa Dayake suite ne yake rayuwa a ciki saiga shigowan siddeeq a gaba Alh Mam seelah din da securities dinsa duk a tsaye bakin Kofar dakin ya shigo siddeeq ya rufe kofar Yana biyo bayansa cikin tsananin girmamawa.
Yaya Abdul na ganin Hakan ya miqe a natse daga inda yake zaune Shima cikin nuna girmamawa Yana masa barka da zuwa cikeda nutsuwa.
Babbah ma miqewan yayi Yanawa mahaifin Haroon din barka da zuwa a mutunce suna kallan juna sbd kowannensu sai fuskan tayi masa kama da Wanda ya sani Amma sbd kada su kure juna da kallo sai kowannensu ya Dan dauke kallansa Dad din Yana amsa gaisuwan a mutunce Shima Dan Daman shi mutum ne Daya iya taku da mu’amalantar mutane shiyasa SEELAHs sukeda mutunci sosai a idanuwan mutane sbd iya tafiyan da lamuransa.
Yanda suka gaisa a mutunce Babu girman Kai ko nuna musu banbanci ya Saka su Babbah din sukai masa sallama suka tafiyarsu Dan Basu guri da ‘dansa batareda Haroon din ya fito ba Dan abinda Basu saniba Haroon din Yana jinsu Amma bazai iya fitowa a halinda yake ciki ba su gansa.
Saida suka fice siddeeq yaje rakasu kafin Haroon din ya fito hannuwansa na tsananin rawa kansa a qasa idanuwansa jajir Babu kyan Gani hakama a jiqe yake da zufa Mai tsananin gaske,
Babu inda yakejin azaba me tsananin gaske kaman a tsakiyar kansa da kirjinsa,
Jin muryan Dad dinsa a dakin ya karasa karya dukkanin Wani karfin halinsa shiyasa ya kasa fitowa Saida su Babbah suka fice Dan ganinsa a wannan halin na mafi Munin rauni zai karya zuciyoyinsu akansa gameda Basu auren macen da bayajin zai iya rayuwar Nan Babu ita su kuwa Ayanda suke tsananin kaunar Ameenatunsu bayajin zasu taba bawa Wanda bazai iya tsayuwa a gaban mahaifinsa bama ya dago kansa aurenta sbd tinanin bazai iya Bata kariya ba ko kare martabarta.
Hannuwansa Dake rawa sosai kaman zasu qanqame yayi Baya dasu Yana kasa dagowa har lokacin kansa Juyewa yake Neman yi.
Zuba masa nasa jajayen idanuwan Mam yaji Yana kallansa sbd baisan ma me zai fara dashi ba sbd baqin ciki da damuwa me tsananin gaske Dan Shima Yana tsaka me wuyar da baisan ta inda zai fara bullowa zancen ba.
Tsadaddiyar wayarsa Daya ajiye gefensa bayan ya zauna ya miqa hannu ya dauka tareda kunnawa ya Nemo hoton Ameenatou ya ajiyewa Haroon din kan centr table Dake gabansa batareda yace komai ba tukuna.
Haroon Daya kasa motsawa bare magana dago jajayen idanuwansa yayi ya Kalli wayar da Dad din ya ajiye masa idanuwan suka sauka akan hoton Ameenatou Dake bayyane a ciki tana murmushi sanye da hijab din islamiya.
Mummunan bugawa kirjinsa yayi ya dago idanuwan da sauri sai alokacin ya Kalli Dad din da Shima shi yake kalla Yana kokarin karantar yanayinsa.
Hannuwansa Dake tsananin rawa ya sake kankamewa Yana sake kallan Dad din da kyau kafin ya Bude bakinsa Dake rawa da muryan Dake bayyanarda tashin hankalin dayafi wanda yake ciki yace
“Dad Kayi hakuri na…..
Katsesa Dad din yayi da cewa
“Ka manta mace ce ta Raba Dan uwanka da mahaifinsa rabuwa ta har abada?
Ka manta matsalolin rayuwar da muke cikinsu duka ayanzu duk sbd macen da Dan uwanka ya so ne fiyeda kansa da ni mahaifinsa?
Wasu Hawaye ne masu tsananin zafi da radadi suka gangarowa Haroon Dan Bai taba tinanin samun kansa a cikin irin yanayin da Jamaal ya samu kansa ba,
Gwara kaddarar Jamaal sbd shi yanada jarumta da karfin zuciyarsa fuskantar duk Wanda zai shiga tsakaninsa da farin cikinsa matars wadda ya tsayawa har ranar karshenta harma a bayan ranta ya tsayawa macen dayake so da dukkanin zuciyarsa.
Wasu zafafan hawayen ne suka sake gangaro masa Yana rintse idanuwansa sbd Yana fatan inama wannan jarumtar zata shigesa ya tsaya akan macen dayakewa mugun son dayakejin yafi Wanda Dan uwansa yayiwa tasa macen.
Hawayen Dake zubawa daga idanuwan Haroon dinne masu bayyanarda tsananin radadin da zuciyarsa take ciki ya Saka Dad zubawa masa idanuwansa hankalinsa na Neman tashi Dan kuwa duk tsananin quncin da rayuwar Haroon din take ciki Bai taba zubar da Hawaye ba sai yanxu.
#MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
38
Ahankali Haroon din yayi qasa sbd kasa riqe jikinsa Dake kakkarwa sosai da yayi har lokacin idanuwansa na kan hoton Ameenatou Dake kan wayar Dad din Yana tsoron me Dad zeyi da hoton nata.
Zuciyar Dad Dake tsallen tafasa tana quna sosai akan abinda idanuwansa ke gane masa na azabbiyar Son yarinyar dayake hangowa a idanuwa da hawayen ‘dansa kwalli Daya daya rage a hannunsa.
Cikin sanyi da tattara nutsuwansa dan fahimtar komai yanda zai fishesa ya Kalli wayarsa shima tareda zubawa hoton Ameenatou idanuwansa zuciyarsa na shiga shakka da rarrabar tinani akan Aminta da ita ko sabanin Hakan sbd bazaiso tarihi ya Kuma maimaita kansa ba.
Dawo da kallansa yayi akan Haroon Yana dauke wayarsa daga kan table din yace