AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

Dayake bayason asan da Yana gurin ko makamancin Hakan ko securities Babu a gurin sbd guri ne da bazata taba tinanin samunsa agurin ba bare a biyosa.

Su kansu su BB Dake bibiyar Babbah ganin sojojine suka daukesa sai basuyi gangancin binsu ba sbd yanzu a ankare suke tinda Jamaal ya bayyana komai zai iya faruwa juyawa sukai Dan sanarda dasu Mam.

Haroon da Shima ya shigo da motarsa gurin yayi parking Yana ganin motar Dad Omar data Jamaal a gurin bayan Kuma yaga lokacinda sojojin suka ajiye babba suka fice take kirjinsa ya sake daukan nauyi Yana bugawa Dan haka Kai tsaye ya wuto ciki Shima.

Babba ne yafara maganarsa Kai tsaye da cewa

“Meyasa ka gayyato Haroon anan??
Kanason yasan ko Kai din wanene?
Kanason yasan kaine asalin mahaifin AMEENATOU wadda ka tsallake ka bari ranar da aka haifeta????

Cak Haroon ya tsaya bakin Kofar batareda ya qasara shigowa ba sbd gagaruman kalaman Babbah da suka shiga kunnuwansa.
#MAMUH
#DR JEEY SEELAH
#AMEENATOU SEELAH
#UNEXPECTED
#CRAXYLOVE
#ROMANCE
#DEEP
#LA HOT

 

*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
52
Dip yaji jinsa Dan ganinsa na Neman daukewa sbd tsananin girgiza da rikewan abinda kunnuwansa suka ji.

Hannunsa Daya iya dagowa da kyar ya bubbuga kunnensa Dan Jinsa Daya dauke take ya dawo idanuwansa da Basu koma daidai ba suna sake rikidewa Dan Bai taba jinsa cikin mummunan tashin hankalin dayake Jin kansa a daidai wannan lokacin ba idan har AMEENATOU dinsa itace jinin Dad Omar din dasu Dad da shi kansa suka ringa dakon nema a tsawon shekarun Nan.

Babbah kuwa da zuciyarsa har lokacin radadin gaske takeyi kallan Omar din yayi Yana cigaba da cewa

“Me kace akan Ameenatou din?
Zaka Nisanta damu sbd Bata kariya
To meyasa ka dawo?
Shin ka manta irin masifar da kusancin naka da ita zai iya jawowa?

Sanyi muryansa tayi jikinsa da bakinsa na rawa cikin mutuwar jiki yace

“Ameenatou itace hasken zuciyata da idaniyata,
Ameenatou itace walwala da farin cikin rayuwata data iyalina,
Ameenatou ita kadaice jinin jinina Danake Gani,
Ameenatou itace nake kallan tawa Ameenatu din a cikinta meyasa zaka dawo Omar?
Meyasa zaka dawo daidai lokacinda take gap da samun farin cikin rayuwarta?
Omar na rokeka da Allah ka koma inda ka fito batareda kowa yasan alaqar da muke da ita dakai ba,
Ameenatou batasan tayaya zata fara karban cewan ga mahaifinta ba a tsaye gabanta wani ne ba ni ba….

Su kansu sirikanta Babu ta yanda Rana tsaka a ranar daurin auren kawai ace musu wani ne mahaifinta ba Wanda suke tinanin sun karba auren a hannunsa ba,

Hakama sanar dasu Hakan dole muna buqatan yimusu qarin bayanin yanda Akai tabar hannun mahaifinta ta dawo nawa hannun,
A wannan gabar me zamu ce musu?
Me zamu sanar musu?
Cewa zamuyi anyiwa mahaifiyarta kisan gilla a gaban idanuwanmu aka yanka cikinta da cikin wata Tara a jikinta????
Ce musu zamuyi a hannuna jininta ya tsayaye Ina kallo ta sadaukar da rayuwarta ta haife cikin jikinta bayan yankan wuqar daya Huda cikinta da kirjinta???
Ce musu zamuyi a wannan ranar da aka haifeta ka tsallake ta ka barta duk akan ana bibiyar rayuwarka zaa hallaka ka??

Jamaal Da kusan Shima mutuwar tsayen yayi sbd shock da tarin mamaki da hada sauran bayanan dayaji a bakinsu Dad da bakinsu ayau din komai Yana haduwa acikin kansa Amma Jin irin kisan da Akaiwa Aminatu a bakin babban ya Sakasa rintse idanuwansa Yana Jin kaman jiri zai daukesa,

Meyake faruwa a duniyar Nan da suke ciki ne?
Wane irin buri ne da son duniya ya Saka su Dad shiga wannan mummunan qazamiyar kaddarar ta kashe kashe irin na zallan rashin Imani????
Bayan irin kisan da sukaiwa Aminatu matar Omar din mahaifiyar Ameenatoun ahakan suke sake bibiyan rayuwarta Baji ba Gani Dan su qarasa aikin da Basu qarasaba shekaru….. innalillahi wainna ilaihirrajiun,
Innalillahi wainna ilaihirrajiun?

Omar shiru yayiwa Babbahn idanuwansa jajir Yana Jin zantukansa na shigarsa suna dawo masa da komai tareda yanka zuciyarsa.

Ahmed ne ya katse babban cikin radadin zuciya da kasa dannewa da cewa

“Duk wannan abin da kake fada akan rabuwarsa da gujewansa tareda bawa Ameenatou kariyan da Kai da tasa sadaukarwan zasu tashi duka ne a banza Dan da hannuwanka gasunan zaka miqawa wainda ke bibiyan rayuwar tasa da tata ita a bainar jamaa gobe..
Da kanka zakai kirari ka dabawa kanka wuqa sbd su sirikan da kake magana sune jinin Omar din Kuma sune masu Neman jinin nasa.

Wani kallo Babbah ya juyo Yana yiwa Ahmed kafin ya mayar da kallansa kan Jamaal da Daya kasa kallan kowannensu Idanuwansa jajir Yana rintse su sbd kunyar abinda duk ake fada ana magana ne akan rashin Imani da Barnar mahaifin Daya haifesa.

Kan Omar Babbah ya mayar da kallansa Yana Jin zufa na tsiyayowa har ta cikin kansa da kunnuwansa Dan haka ya zare hular kansa yayi wurgi da ita Yana cewa

“Omar me nake ji?
Me yake faruwa?
Menene yake Kuma Shirin faruwa?
Shin balain ne ya dawo da masifar kokuwa wace balain ce take Shirin dawowa??
Meye hadinka da SEELAHs???

Kallansu yakeyi Daya bayan Daya a rude Yana Neman Karin bayani Dan kansa Neman Juyewa yakeyi da tashin hankali da tsoron abinda zai iya faruwa idan wani abu ya samu Ameenatou dinsa.

Omar ne ya dago tareda tashi tsaye Yana fuskantar babban idanuwansa jajir yace

“SEELAHs shine Nima nawa asalin sunan ba Jden ba?
Mamman seelah, Lameenu seelah, Omar seelah da Yan uwanmu biyu da suka rasu kasim da jamilu seelah Yan uwan jini muke,
Dukiya itace ta lalata jinin dayake yawo a jikin kowannenmu na alkawarin tsira tare mu mutu tare,

jinin yan uwanmu ne Daya zuba akan dukiyar ya gurbata dukiyar ta Saka mu samun Kanmu a mummunan halinda muke ciki a yanzu na bibiyan rayuwar Yan uwanmu Amma ka sani har abada bazan iya rabuwa da yata ba a yanzu kaman yanda nayi alkawarin Bata kariyar da ban samu bawa mahaifiyarta ba,

Ameenatou a yanzu itace babban abinda duk wani maqiyana yake Neman samu,
Ameenatou itace mukullin dayake riqe da duk wani abinda Dana mallaka,
Ameenatou itace mamallakiyar dukkanin tarin dukiyar Jden a rubuce Dan haka samunta a shine mafi farin cikin cikan burinsu,
Sanin wacece Ameenatou shine babbar hatsari da tashin hankalin da dukkaninmu zamu fuskanta Dan haka Babu maganar aurenta a goben Dan har abada bazasu taba Dena Neman ba har sai ranarda suka samu sanin waye magajin dukiyar jdens gaba dayanta.

A rubuce dukkanin dukiyata da abinda na mallaka nata ne,
Ahmed ya sani ayau Kai da Jamaal inason Kuma ku sheda Hakan sedai ku sani barin asan wacece ita shine karshen komai.

Kallan babbah Daya gama jiqewa da zufan gaske hankali tashi yayi kafin ya Kalli Ahmed ya zaune dashi ahankali ya fara zayyano masa asalin tarihinsu da komai tin daga barowansu gaban iyayensu har zuwa yanzu da suke maganar.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected