AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE
Dad Lameenu dayake cikin mawuyacin hali har lokacin dagowa yayi yace
“Yanda Babbah ke son ‘yarsa har abada bazai tabawa me tabin kwakwalwa auren yarsa ba kome zaayi kuwa Dan Haka takardun asibitinka kawai zamu basa a Daren ba sai gobe ba,
Maza ma ka fice ni ko ganinka Haroon a yanzu banason yi qaramin hawan jini yakeyi,
Ka cucemu Kaci amanar mu Kaci amanar kaunar da mahaifinka yake Maka.
Zuwa lokacin Haroon ba iya hannuwansa kadai ne suke rawa ba dukkanin jikinsa jijjiga yakeyi sosai hakama kansa tini yayi wani irin mugun nauyi Yana Neman inda zai fara bugasa bakinsa yakeson budewa Yayi magana Amma Dad Shima ko ganinsa bayason yi a lokacin sbd zai iya masa Baki idan Bai bar gurinba Dan haka Dad dinne ya fice Kai tsaye ko gabansa Baya Gani sbd Shima jininsa yayi mugun hawan Daya wuce misali.
Daqyar yakai kansa cikin gida yayi samansa ya shige bedroom dinsa Dan har lokacin Babu kowa a gidan Yan biki suna gurin bikin.
Dad Lameenu ma BB ne ya taimaka masa ya fice.
BB ne ya dawo office din ya kama Haroon daya qanqame gabaki Daya Yana rawan jiki sosai yakaisa har palonsa ya dawo ya rufe office din ya fice daga Mansion din.
Haroon rarrafawa yafara yi idanuwansa na ganin duhu da haske yafara kokarin Kai kansa bedroom Amma ya kasa sbd wani kifewa da yayi akan console mirror dayake hanyar bedroom din ya fado masa ya fashe.
Bugawa kansa keyi sosai hakama hannuwansa rawarsu ta tsananta sosai har tayi muni hakanan ya sake dafawa ya tashi cikin glass din Yana dafa Bango ya Isa kofar dakinsa yana shiga ya zube qasa Yana buga kansa sosai a tiles idanuwansa Dake rufe suna sake birkicewa.
Siddeeq kaman yasan abinda yake faruwa a mansion din ya dawo daukan Haroon sbd acanma Haroon jikinsa ya rikice zazzabi Mai karfin gaske da Bai taba yin irinsa ba ya rufesa Wanda ya bawa siddeeq tsoro hakama mum datake Kiran yayan nata Babu me dauka siddeeq din ta kira tanajin Jamaal ba lafiya taji hankalinta ya tashi Amma Kuma wannan Karan rashin daukan wayar Haroon yafi daga hankalinta fiyeda ciwon Jamaal Dan haka tace siddeeq ya dubo mata mansion din zuciyarta takasa samun nutsuwa.
Koda siddeeq ya Isa halinda ya samu Haroon yayi mugun girgizasa Dan Bai taba ganinsa a irin wannan mugun halinba duk tsananin ciwonsa kuwa.
Da gudun gaske ya qaraso inda yake ya tallafosa sedai Haroon din yayiwa kansa mummunan rauni jini Tako ina Dan haka a haukace ya daukosu gaba Dayansa ya fito dashi Bai tsaya wata wata ya Saka mota sbd ba qaramin munu lamarin yayi ba ya fice dashi zuwa asibitin SEELAHs din da gudun gaske.
Yana Isa aka karbi Haroon din da gaggawa Dan tini ya fice hayyacinsa Wani jijjiga kawai yakeyi sosai kaman me wani ciwon daban.
Fadan tashin hankalin da siddeeq ya shiga a wannan lokacin bamai yiyu bane sbd ya shiga tsoro Mai girma wannan Karan da ciwon Haroon din ga Jamaal a kwance ba lafiyan Shima.
Haroon sosai ya wahala cikin azaban ciwonsa Babu uwa Babu Uba Babu wani nasa sai siddeeq Wanda ya tsayu akansa har Saida ya dawo daidai sbd cikin qanqanin lokaci Allah ya mayar dashi kaman ba shine angon da zaa daurawa gobe ba.
Duk karfin zuciyarsa siddeeq sai dayaji tausayin Haroon ya karyasa sbd bayan dawowansa daidai Hawaye ne masu tsananin zafi da radadin zuciyan gaske suke gangaro masa batareda yace komaiba.
Sallan magrib siddeeq yake yaji daga can ya koma hotel ua dubo yanayin Jamaal Wanda ya Riga ya miqe haryayi wanka yayi Sallah
Siddeeq din na zuwa ya sanarwa da Jamaal halinda Haroon yake ciki.
Karban key Jamaal yayi shi kadai ya nufi asibitin gurin Dan uwansa.
Zuwansa asibitin Haroon na ganinsa hawayen tsananin kaunar Dan uwansa daya tabbatarda duk duniya ko mum dinsa Kila Baya kaunarsa yanda Jamaal din yake sonsa ne suka ciko idanuwansa suna gangarowa.
Jamaal Daya kasa masa maganar abinda ya faru ayau din sbd ganin yanayinsa daukansa yayi suka baro asibitin Babu me magana shiru kowa da abinda yake tinanin Amma dai shi Haroon zuciyarsa da jikinsa gaba Daya a Sanyaye suke sbd rayuwarsa yasan daga yau ta dena moruwa ne sbd aurensa dayasan har abada Dad bazasu taba barin ayi aurenba,
Rasa Ameenatou garesa tamkar zare control na tabin kwakwalwansa ne kaman yanda su Dad suka fada Dan haka idan har tabbas gobe ya tabbata ya rasa Ameenatou to ya cire Rai daga komawa daidai,
Yasan Jamaal da mahaifiyarsu zasu shiga tsananin qunci da baqin ciki akan Hakan Amma Shima kansa a yanzu yasan ko da auren Ameenatou ko Babu tabbas tabin kwakwalwa ne a tattare dashi me tashi Kuma me tsananin gaske.
Rintse idanuwansa yayi ahankali maganganun Dad da fushinsa da Bai taba Ganin irinsaba suna dawo masa a kunnuwansa take yaji ciwonsa na Neman sake dawowa ya dago jajayen idanuwansa ya Kalli Jamaal dayake tuqi a natse Shima zuciya da kansa duka a jagule da lissafi kala kala.
Cikin wata murya me sanyin gaske data Saka zuciyar JAMAAL sanyi akan fushi da bacin ran dayake ciki akansa
yace
“Jamaal,
Kayi mun alkawarin ganin na auri macen danake so matiqar ba Allah yariga yayi cewan ba matata bace,
Ko ban auri AMEENATOU a gobe ba Kai inason ka sheda itace macen danake so fiyeda komai a duniya bayan Kai da mum,
Son AMEENATOU wata jarabtace da Allah ya jarabceni da ita,
AMEENATOU itace macen da zanso har karshen rayuwata Kuma itace mace Daya da bayan ita Babu macen da Nima zan iya so.
Ko ban auri AMEENATOU ba bazan iya rabuwa da ita ba Dan haka Dan Allah Jamaal Karka bari su dadi su hanani samun farin cikin aurenta,
Aurenta shine Abu na karshe da zanzo kafin rayuwata tabar duniya…….
Shiru Jamaal yayi masa har suka Isa mansion ya shigo dashi har cikin harabar gidan wannan Karan shine da kansa ya fito motan tareda Dan uwansa dukkanin securities din gidan da sauran Jamaar dasuka dawo event suna harabar gidan mutuwar tsaye sukai ganin su biyun a tare Kuma kusan kamannin Babu Wanda zai iya banbancewa bayan raunikan Dake fuskan Haroon sai Kuma haske da jamaal yafisa sosai.
Mam da lameenu wainda suka Fito masallaci sallan ishai daqyar sbd radadin da zuciyoyinsu suke ciki mutuwar tsaye sukai lokacinda suka kawo su Jamaal dinma sun kawo cak kowannensu ya tsaya Mam ganin ‘yayan nasa a gabansa tare sai yaji zuciyarsa na narkewa da tsananin kauna da kewan kasancewa inuwa Daya dasu.
Lameenu kuwa kallo daya yayiwa jamaal yaji jininsa na son Hawa da sauri yai gaba
Shima Dad kafin kowannensu ya motsa ya gaidasa gaba yayi batareda ya waiwayosu ba ganin Haroon kawai Yana tafasa ransa.
Jamaal ajiye Haroon kawai yayi ya juya yabar gidan Kai tsaye gidan da zai Hadu da Dad Omar a daren ya wuce Yana kallan time.
Suma acan bangaren tin ana sallan ishai Yana fitowa masallaci Ahmed yayiwa Babbah abinda baisoba waton nuna masa power Kai tsaye sojoji ne suka daukesa daga kofar gidansa suka wuce dashi shi kuwa Haroon da Jamaal na ajiyesa ko zama baiyiba Shima ya fice gidan yayi gidansu Ameenatou Kai tsaye Yana Isa motar na wucewa da Babbah Dan haka ko gidan Bai shiga ba Shima yabi bayansu.
Sun isa da Babbah motar Jamaal ma na Isa Dan haka kusan da Ahmed din da Babbah dayake kallan Jamaal da dukkanin Idanuwansa da tsoro da shakka harma da fargaba tare suka shigo palon da Dad Omar din yake zaune.