AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

Abinda yake ji a zuciyarsa tsananta ta yanda ko numfashin iskan da Omar yake gurin Bazai iya shaqaba,
Hakama tayaya zasu fuskanci juna da Omar din?
Me zasu tattauna?
Meye a tsakaninsu?
Ameenatu ce Kuma ta rasu Dan haka ba sauran abinda ya rage Dan wannan Ameenatou din ya yanzu tasa ce Babu abinda zaisa ya tsaya ya sauraresa, idan ma zasuyi magana to yabari sai bayan daurin aurenta.

Takawa yayi a raba gefen Ahmed ya wuce Yana Jin kirjinsa na tsananta nauyi kaman numfashinsa ma zai toshe.

Motsawa Ahmed yayi zai bisa Omar ya dakatar dashi sbd Shima tasa zuciyar datai nauyi.

Tayarda motar sukai suka bar gurin sbd ganin kaman wata motar tafe Wanda Sam bayason asan Yama San Babbah sbd abinda ya lura ya karanta a tsakanin zuwansa zuwa yanzu shine su mamman basusan Ameenatoun itace Ameenatou Jden ba da suke tsananin nema Dan haka yanada Daman Hana auren ko dauketa kafin sanin nasu Wanda kowanne time zasu iya sanin Hakan sbd yasan sarai ana biye da takunsa da lamuransa shiyasa bayason bayyanarda sanayyarsa da Babbah.

Suna wucewa Babbah ya Nemi guri ya zauna Yana rintse idanuwansa sbd zufan Daya jiqasa me zafi,
Baisan ta inda zai fara barin Ameenatou tasan ba sune suka haifeta ba,
Idan ta sani kwata kwata bayason duniya tasan ita ‘yar Omar Jaden ce sbd hatsarin da rayuwarta zata shiga me girma,
Ba Dan bayason Omar ya Hadu da ‘yar tasa ne ba sai Dan barin su Hadu din asan yarsace komai zai iya lalacewa,
Ameenatou zata iya shiga hadari sbd ko bayan aurenta zata iya shiga hadarin duk da acikin masu arziki sosai zatai auren Amma Shima Omar din me kudin gasken gasken ne Amma aka tafi har cikin gidansa aka kashe Ameenatunsu tana cikin nakuda ba Dan Allah yasa Ameenatou rabo bace da yanxu baisan a wane matsayi rayuwarsa take ba Babu Ameenatunsa Babu abinda ta Haifa.

Ya jima a gurin zaune cikin tsananin damuwa da tashin hankalin da Bai Saka masa Rana ba Dan kuwa duk Jin yayi Lagos din fitar masa a Rai hankalinsa ya fara tashi matiqa.

Daqyar ya dawo da kansa gida sbd kirjinsa dayake wani irin ciwo da nauyi hakama zufa yake hadawa sosai ya kasa denawa.

Yana isowa gida ya shige daki batareda kowa yaga halinda yake ciki ba Dan sunacan sunata hayaniyar bikin da zaayi gobe Wanda Seelahs suka hada.

Omar ma yana komawa gida kusan damuwan tabasa tayi Saida likita yazo ya Danyi checking BP dinsa kafin ya shige cikeda damuwa Dan bayason nunawa Babbah karfinsa yanason ya aminta dashi suyi maganan Daya kamata kafin lokaci ya kure sbd idan ya nuna masa power kaman yaci mutuncinsa ne bayan Tsananin gata da son dayasan Yanawa ‘yarsa fiyeda yanda yake son nasa yayan na cikinsa.

Ahmed dayaji shikam baida hakuri ko lokacin batawa akan lamarin Yanke shawaransa yayi Babbah dole ya saurare abinda ake son fada masa Dan Jin Wanda akeson aji daga garesa.

A cikin Daren jirgi ya sauke Jamaal tareda siddeeq a Lagos batareda sanin kowa ba Kuma a Daren yayi magana da Ahmed Wanda basusan Jamaal na qasar ba Shima Dan haka da safe siddeeq ne yaje mansion din Mam seelah ya dauko Haroon Wanda a ranar yake cikin farin cikin dayafi na kullum sbd daga ranar sai ranar daurin aurensa da mutanensa da yawa Shima suna Lagos Dan halarta daurin auren goben.

Wata lafiyayyar tsadaddiyar Lodge din da Jamaal yake siddeeq ya Kaisa Yana shiga Jamaal dayake jiransa ya fito tareda siddeeq din suka barsa acan sbd Jamaal din na buqatan ganin Dad Jden.

A rumfar hutawan Dake bayan mansion din ta gurin garden suke wadda ta hada kofofin gidajensu uku batareda saika zagayo ya gate ba kake shiga tanan Dan haka yasa familys din suke kaman a gida gade guri daga daga baya Baya gaban mansions din ba.
dukkaninsu ne a zaune su uku sai Ahmed na hudu suna zaune cikin Hutu da nutsuwan Wainda arziki da Hutu ya ratsa fira sukeyi Hakama table dayake gabansu tea ne kusan kala hudu a different tea set masu kyau da tsada sai healthy snacks na Manyan mutane sai wayoyinsu da Kuma jaridan yau.

A Jden mansion baa yadda motar kowa nene ta shigo gidan ba iya ta masu gidan ce kadai take shiga ta Kuma fita Dan haka siddeeq baima nufi gidan Kai tsaye ba mansion din Dad ya shige sbd securities ma na ganin motar Haroon ce ta dawo suka wangale gate din ya shige da ita yayi parking.
##MAMUH#

*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
49
https://chat.whatsapp.com/K3rO5UonX4GDVxtQbA5mZl

Assalamualaikum wa rahmatullahi ta’ala wa barakatuhu!!! Wannan group din dai na komai da komai ne. A taiqaice
*Farashin mu na daban ne compared to sauran Yan kasuwa
*Kaya masu kyau da quality. Abinda kika zaba shi za a Baki
* Swift delivery.watau waybill a sauqaqe da Yardar Allah
* Muna sake New Arrivals ka fin su cika Gari
* Muna iya duba maku kaya a good price ko da ba namu ba ne idan kuka Aiko da hoton kayan
Allah sa mu qaru da juna Ameen

 

****************
Fitowa Jamaal yayi daga motan sanye da sweatset ash na Ralph Lauren wandon mara tsayi da kadan ya sauka gwiwansa kafarsa sanye da sneakers na Louis Vuitton Ash fuskansa sanyeda fcap da glass na Versace Kai tsaye hanyar garden din ya nufa sbd siddeeq Daya sanar masa securities since su Dad na can garden din gidan Sir Jden.

Cikin nutsuwa ya nufosu Kai tsaye idanuwansa na kallan irin zaman Hutu da bayyanarda kusanci,so da shaquwan da sukai Amma abin baqin cikin dukkaninsu ba Hakan ne a cikin ransu ba Dan haka yaji tausayi da tsananin son Dad Jden na sake shigan zuciyansa sbd mutum ne dayake da tabbacin Babu tsatsa a zuciyansa.

Dad Lameenu ne yafara Ankara da tahowansa ya gyara zamansa Yana zuba masa idanuwansa da Shima suke cikin farin glasses Yana kallan fatan kafafunsa Dake bayyane sbd wandon Dake jikinsa sai daukan ido takeyi a fili karara sirkin bature da Nigeria.

Mam ma juyawa yayi ahankali ya Kalli Jamaal din Yana sake fuskan Dan yanzu Haroon ya zama hasken idanuwansa,
Sedai murmushin nasa Neman sauyawa yayi sbd idanuwansa Jamaal suke nuna masa Dan kuwa tafiyan da class da kamewan duk na Jamaal ne yake Gani Amma ya kasa yadda da abinda idanuwansa ke nuna masa da sauri ya juya ya kalli inda lameenu yake shima Lameenu din shi ya kalla kafin suka Kalli Omar a tare Wanda idan Jamaal ne sun tabbatarda zai fisu ganewa sbd shine ya taso Dashi a gabansa har girma Kuma sun tabbatarda suna tare haryanxu din,
Idan har Omar zaizo auren Haroon sun tabbatarda Jamaal ma duk inda yake Yana cikin Nigeria Kokuma Yana hanyar sauka cikinta ayau din tinda gobe ne daurin auren.

Omar da kallo Daya yayiwa Jamaal ya gane waye ke tahowa a natse cikin kulawa da bayyanarda kauna ya saki fuska murmushinsa me kyau Yana fitowa idanuwansa akan Jamaal din Wanda Shima shi yake kalla murmushinsa daya kusan Saka shayin Lameenu biyowa ta hancinsa Ya saki ahankali da nutsuwa..

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected