AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE
Hafiz dayake ganin sauyi sosai a Haroon din dayake Gani Gurin Aiki da safe da Kuma Wanda yake Gani gidansu da daddare sai ya Saka Hakan akan gurin aiki daban da gida Shima Saiya janye daga nuna kusancinsu da Haroon din gurin aiki saisun hade gida suke fira da gaisawa yanda ya kamata.
Jamaal kansa mamakin Haroon din yakeyi sbd yanda zuciyansa ta gama mutuwa akan yarinyar bayaji Baya Gani Baya gane komai idan bana Yarinyar ba da har lokacin shi Yama kasa tsayawa ya riqe sunan.
Fahimtar irin son dayakewa yarinyar ya Saka Jamaal din Jin bazai iya barin Haroon ya rasata ba.
Ta bangaren su Dad kuwa duk lokacinda ya buqaci ganin Haroon Jamaal ne yake zuwa sbd bayason Haroon ya sake tsayuwa a gabansu Dan kada su lalata masa aikin treatment Daya basa shida mum akan lafiyansa da suketa kokarin ganin samunta Dan kuwa shiyasa suka buqaci komawansa tareda sakashi alkawarin komawan acan Dan kuwa abinda yake Sha Wanda Basu gane Menene ba yayi masa Mummunan illan da basason ma ya sani kwata kwata.
#MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
45
Ranar da Abdul ya cike kwana hudu a Lagos Dan fara aiki a ranar su Dad Lameenu suka sake dawowa nasarawa maganar tsayar da aure hadda Abdul din aka taho Wanda Dad Lameenu ya jasa a jikinsa sosai yana masa kallan kaman ‘dansu duk Dan sbd ya sake dasu sosai ya samu aminta dasu har zuci ya yanda komai zai taho a sauki.
Sun sake zama anyi magana an tsayar da ranar auren sati uku hudu masu Wanda daqyar dai su Babbah suka aminta da Hakan sbd kwanakin sun musu kadan duk da ba wani biki sosai akace zaayiba Tinda a Lagos zaayi komai Amma hakama sun buqaci yafiyan duk wani abu da amarya zata buqata Amma Babbah ya nuna amincewa da Hakan gaskia sbd duk fafutikan rayuwar dasukeyi shi da su Abdul na inganta rayuwarta ne su Bata gata Dan haka dole zasu wadata ta da dukiyan aure kaman kowace ‘ya yar asali yar gata daidai karfinsu.
Su Dad din Basu wani ja da Hakan ba Daya dage Dan haka take suka gabatar da komai aka Yanke sukai Godia Suma su Babbah sukai godiya.
Wannan Karan harda dadah aka kirawo musu suka gaisa da ita da Ameenatou din wadda take sanye cikin doguwar Riga maroon sai veil data doro Akai.
Sun nuna yabawansu da nutsuwanta a fili sosai suka ringa sake yiwa Babbah godiya Wanda tini ya sake Jin hankalinsa ya kwanta dasu da mutuncin da suke dashi hakama Abdul ya sake tabbatar masa da mutuncin dasuke dashi harma agurin mutane Dan haka yake sake godewa Allah akan zabin da yayiwa Ameenatou dinsa Dayake ta addua da fata.
Da farko babbah baida niyar zaman Lagos din Amma a yanzu da Aure yakai ‘yar budurwansa yaji bazai iya zama a nesa da inda take ba tinda harsuna da inda zasu zauna din agidan Abdul Dan haka ya aminta da komawa Lagos din gashi Daman Hafiz ma Lagos din zaibi Haroon kaman yanda yayi masa alkawarin dashi zai koma Koda aikin site ya kammalu acan zai basa aiki a kamfaninsu.
Tsayar da ranar auren ya Saka Haroon shiga lokutan farin cikin rayuwarsa Dan haka ya sake nutsuwa sosai Yana mayarda hankali cikin aikin project din da Jamaal ya tsayu akansa Dan kammalawa ya tafiyansa Dan kullum Jin yake Yana sake matsuwa da barin kasar.
Haroon ganin irin kulawa da kaunan da mahaifinsa yake nuna masa ayanzu Dayake alfahari dashi dakuma ganin abubuwa nata dawowa kan hanya sai yaji soyayyar Dad dinsa na kashe masa jiki kaman bazai iya tafiya ya barsa ba Amma Bai bar Jamaal ya fahimci Hakan ba Dan Jamaal kwata kwata ya Dena bayyana a gaban su dad din sbd yanzu kauna zalla sosai Dad yake nunawa Haroon Dan haka yabarsa ya samu kaunar dabai samu daga Dad dinba Wadda yake tsananin so da burin samu.
*****Su Babbah kuwa A nasu bangaren sosai hidiman tayi musu yawa sbd ga hidiman Shirin biki gata tashinsu duk da ba siyar da gidansa zaiyiba Yan haya aka Nemo zaa Saka Dan haka suketa shirye shiryen tafiya da siyarda abinda ba dashi zaa tafin ba.
Su mum Atee ma da zasu taho kawo kayan aure su lefe da masu gyaran amarya Babbah cewa Yayi su barshi acan tinda suma a satin zasu iso Daman sun zabi yin auren acan ne sbd kawowa kowa sauki dangin angon masu zuwa da Jamaar seelahs din da duka manyan mutane ne da manyan qasa hakama da Yan kasashen qetare sbd sosai Mam ya fito ya nunawa duniya auren dansa zaayi Kuma aure na alfarma na Manyan masu abin duniya Dan haka aketa shiri da Kuma miqa gayyatansa ga abokanan huldansu da manyan masu kudin da suke tare harma da gwamnoni.
Ita kanta amaryan Haroon Kuma budurwan Babbah farin cikinta kusan kullum Baya boyuwa sbd a kwanakin Dan kullum auren yake matsowa cikin tsakiyar ranta take sake Jin tsananin kauna da son Haroon Wanda ya tsayu tsayin daka ya tabbatarda ya dawo da sonsa sabo fil cikin ranta.
Daga shi har ita Hafiz yace ya rasa wanne yafi rawan kafar aurenba ita dai bata tanka Hafiz din sbd ta shirya masa duk abinda Bai zata ba bayan auren tinda a karkashin mijinta zaiyi aiki.
Duk hidiman auren da akeyi Jamaal Bai shiga ko dayaba sbd baida time ko kadan na batawa aiki yakeyi gadan gadan ba dare ba Rana Kuma Hakan saka su dad farin ciki yakeyi.
Ranar dasu Babbah suka gama parking zasu wuce Lagos Kuma jirgi zasubi dukkaninsu sbd murna Ameenatou har fita tayi yau ita kadai a Karan farko rayuwanta taje gidan kawarta Aminiyarta Khadija Tayo mata bankwana itama Khadijan satin zaa fara bikinta shiyasa bazata samu binsu ba ayi bikin da ita Dan haka suka hakura dole da samun bikin juna.
Fitowa sukai tareda Khadija din ta rakota har kusan Rabi kafin ta koma ita Kuma ta wuce.
Dayake hanyar site ne gidansu Khadijan tana kawowa gurin hanyar site din ya hango motar Haroon ta tsaya a bakin hanyar da zatabi ta wuce bakin shago batareda an Budeba.
Glass ya saukan aka miqo masa Abu daga shagon Wanda take kyautata zaton ruwa ne sbd bayan motarsa aka Saka masa.
Wani kyakkyawar murmushi me sanyi ya sauke daga fuskanta tana kallan motar ta tabbatarda shine a ciki bayan yanzu da sukai magana cemata yayi Yana Abuja.
Motan ta nufo tana daga wayarta Dan Saka Kiransa taji me zai fada mata yanzu Kuma.
Tana isowa motar ta miqa hannunta Daya akan mabudin kofan Baya Dan tasan anan yake zama siddeeq ne me jan motar
Tana budewa daidai Yana dagowa daga abinda yake Karantawa daga iPad din hannunsa ya kalli kofan motar da aka Bude Idanuwansu suka shiga cikin na juna
Shikuma a Karan farko Daya Kalli idon wata ‘ya mace rayuwansa bayan rasuwan matarsa.
Itama nata idanuwan kusan shine karanta na farko kallan cikim idan mutum Dan haka ta dauke fararen idanuwan nata tana sake wata fitinanniyar murmushi tareda shiga ta zauna Kai tsaye tana juyowa suka fuskanci juna qamshinsa na shigan hancinta Kai tsaye zuwa zuciyanta murmushinta Bai daukeba sedai yau din ta kasa kallansa sbd kunyar takusa zama matansa Kila yau takeji da wani shagwabbiyan murya ta dago ta zuba masa idanuwanta tace