AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

Kuka wiwiwi Babbah keyi dukkanin jikinsa na rawa sbd shiga tashin hankali da tsoron rayuwar dasuka samu kansu dumi dumi aciki ta masifar da Bai taba ji ba…

Jamaal ma kusan silalewa yayi kan kujera wannan Karan da hannuwansa biyu ya Saka Yana rintse idanuwansa sbd kansa Dake Neman bugawa tareda zuciyarsa….

Ahmed ma da tinda yake da Omar din baisan asalin asalin mafarin komaiba sai yau din sbd kaf duniya yanzu Babu Wanda yasan ba uwa Daya Uba Daya SEELAHs suke ba sai yau din,
Ko Jamaal da Haroon dasuke yayan cikinsu da matayensu Basu taba sanin wannan sirrin ba sai yau din da Omar yake fada musu da bakinsa cewan ba uwa Daya Uba Daya suke ba…

Dukkaninsu Dake palon silalewa sukai qasa kowa kafafunsu na kasa daukansu,

Duk tsananin jarumta da karfin halin Jamaal Hawaye ne suka ciko jajayen idanuwansa yanajin wani abu me nauyin gaske ya tsaya ya tokare kirjinsa sbd baqin ciki da radadi tareda kunyar abinda ake fada mahaifinsa na ciki,

Makashi ne ya haifesa?
Makashin Yan uwansa da wainda Basu da hakkinsu na komai shine mahaifin Daya haifesa,
Mahaifinsa shine makashin kakanninsa da macen da harya mutu bazai taba Dena Sonta ba…..
innalillahi wainna ilaihirrajiun,
Innalillahi wainna ilaihirrajiun

Babbah kuka yakeyi sosai hankalinsa da gashin jikinsa duka suna tashi,

Shi kansa Omar da sai yaune ya Bude Baki ya iya furta abinda yake ransa qunshe tsawon shekarun Nan Bai taba maganar dayake cin zuciyarsa Yana saukar masa da radadi mafi ciwo na yanda shi da Yan uwansa suka kasance,
Tin suna Shan nonon iyayensu suke tareda juna a guri Daya aka haifesu suka taso tare batareda ko a takalman sakawa iyayensu sun banbantasu sbd kauna junan datake yawo a jininsu tin
A iyayensu take acan ta samo asalinta har a nasu jinin,
Sun tashi da kauna me karfin gaske a tsakaninsu Amma yau rayuwar junansu suke nema,

Wannan abin ne yake Saka Omar baqin cikin Daya zauna zuciyarsa yake cinsa akowace daqiqan rayuwarsa Dan haka yau Daya samu furta sirrinsu hawayen ne suka gangaro masa a Karan farko sbd a yanzu bayan su ukun dasuke gabansa Babu Wanda ya yadda dashi Akan yarsa,

Su uku sune wainda yasan zasu tayasa bata kariya da rayuwarsu Dan haka ya juyo da idanuwansa akan Jamaal Wanda shi kadai ne Seelah Daya dayake Jinsa har cikin ransa Kuma ya yadda dashi fiyeda rayuwarsa kaman Ahmed a Sanyaye yace

“My son Ina tsananin baqin cikin hanawa Dan uwansa wannan auren sbd ba Kai bane,
Kai kadai ne namijin dana yarda na bawa aurenta na jefata cikin SEELAHs batareda naji shakka ko tsoron Hakan ba,
Kaine Wanda zan bawa amanarta ko Bada aure ba Amma kwata kwata zuciyata Bazata taba samun nutsuwa ko Kwanciyar hankalin bawa Haroon aurenta ba Badan komai sai Dan rauninsa ga mahaifinsa Wanda ba ita kadaina akanta shi kansa tasa rayuwar a hadari take…..

Dago jajayen idanuwansa Jamaal yayi ya zubawa Dad Omar din tareda girgiza masa Kai bakinsa na sake daukan nauyi sbd tsananin son da Dan uwansa yakewa Ameenatou din idan aka rabasa da ita matsalar ciwonsa zata iya Maidasa cikakken mahaukacin dayake tsananin tsoron ya koma,
Bazai iya kallan Rabin jikinsa Haroon din ya koma Hakan ba,
Zai iya sadaukar da rayuwarsa akan lafiyan Haroon da Kuma samar masa macen dayake so fiyeda nasa ran Dan haka ya Bude Baki bakin cikin muryansa Daya shaqe sbd tsananin tashin hankali da baqin ciki harma da shock yace

“Dad Dan Allah Karka Hana Haroon auren Ameenatou,
Ameenatou itace farin Daya Kuma nutsuwa Daya rak Datake riqe da rayuwar Haroon,
Hana masa aurenta tamkar rabasa da lafiyarsa ne gaba Daya,.
Haroon Yana yimata tsananin son da bazai taba barin komai ya faru da ita ba Koda hakan na nufin zai gitta tasa rayuwar”.

Kuka Babbah ya sake fashewa dashi sbd gano gaba Daya su rayuwarsu acikin seelahs din da aurenma gaba Daya a duhu suke Babu Abu Daya dayake gaskia sai soyayyar da Ameenatou dinsa takewa Haroon sbd Jamaal da Haroon dai mutum biyu n mabambamta da suka ringa wasa da zuciyar Ameenatoun,

Tayaya zai bari Ameenatou tayi aure a cikin wainnan mutanen da yanzu ma tsoro suke tsananin basa bayan Omar din da Ahmed sai Jamaal din Wanda yaji yamafi samun nutsuwa dashi.

“Bazan taba bawa Haroon ko Daya daga cikin zuriar seelahs din auren Ameenatou ba gaba Daya har abada” babban ya fada Yana dagowa jajayen idanuwansa Yana kasa kallan Jamaal Daya cike masa ido har lokacin Hawaye ne ke zubowa daga idanuwansa…..
#MAMUH#
#THE SEELAHS
#THE JDENS
#LOVERS
#MARRIAGE
#AMEENATOU JDEN SEELAH

 

*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#Arewabooks@Mamuhgee
#ZafafaBiyar
#BestLove

53
Maimaicin fasa aura masa Ameenatou da akeyi ne ya Saka kansa kasa dauka hannuwansa suka fara rawa hakama kafafunsa,

Toshewa kirjinsa yakeyi Yana Jin kaman bazai iya Jan numfashi ba ga idanuwansa da suka fara ganin babbiyu Dan haka yafara bin Bango Baya Gani sosai ya juya Yana dafe gefen kansa da hannu Daya Yana kokarin Bude idanuwansa dakyau da basa Gani sosai bayan gasu a buden.

Tsananta rawa jikinsa yakeyi sosai,
Mummunan faduwa yayi Yana gap da Isa motarsa sbd tsananin da jikinsa yayi Dan haka da rarrafe ya nufi kofar ficewa ya fice yabar Motarsa a gurin Yana rarrafawa duhun gaske Yana qara rufe idanuwansa.

BB dayake nesa sosai daga gidan sbd bayan ya koma Mam sakashi dawowa yayi akan ya tabbatarda ya riqe tsawon lokacin da suka dauka a tare Dan haka ya dawo batareda ya tabbatarda su waye da waye a cikin gidan ba gashi Kuma Yana shakkar Isa gurin sosai ko shiga a samu matsala Dan baisan takun Jamaal ba.

Idanuwansa akan gidan da duk motsin dazai fito cikinsa yake Dan haka Yana hango motsi ya fito daga maboyarsa ahankali tareda Dan biyu duhun ya iso gurin daidai lokacinda Haroon yake fara buga kansa a Kan titin dayake tsit Babu kowa ko motsin komai..

Tareda yayi da sauri tareda rufe masa Baki ya janyesa da sauri daga gurin yayi cikin duhu dashi Yana Jin kirjinsa na harbawa Yana leqa hanyar gidan baiga ko motsin kowaba dazai fito daga ciki.

Sunkutar Haroon yayi gaba Dayansa duk girmansa sbd shi kansa BB din ba qaramin Mai qarfin gaske bane sbd a Bude yake kaman basamude.

Gurin motarsa Dake nesa da gidan ya nufa dashi ya Bude ya Sakasa ciki tareda rufe motar yana juyawa yaga har lokacin Babu kowa yaja motar yabar gurin da sauri sbd Baya buqatan cigaba da jiran indai Haroon daga ciki yake tareda su Omar din yasan me zai masa duk abinda suka tattauno zasuji koma Menene adaren Nan.

 

****Jamaal irin roko da tabbaci tareda alkawarin da yayiwa Dad da Babbah akan auren ya Saka jikinsu sanyi Jin irin halinda Haroon yake ciki da ciwon dayake cin kansa batareda shi kansa ya sani ba,

Sanar dasu yayi alkwarine ya dauka ana auren zai tafi tareda Haroon din da Ameenatou gurin mum dinsu acan zasu zauna duk wannan yaqin batareda ko dayansu cikin su biyun ba zaayisa wanna alkwarine yayi musu.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected