AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE
Fira siddeeq yajasa sosai suna tafiya har suka fice gaba Daya daga site din ya fada masa sunanan tafe daga Nan zasu taho gida.
Sallama sukai Hafiz ya wuce gida Kai tsaye Jin suna Nan tafe Dan yasan yau budurwan gidan zata barsu su huta da rigimar rashinsa ba kunya ba tsoron Allah.
Yana wucewa siddeeq ya dawo har lokacin waya yakeyi sedai baima gama ba ya wuce ya nufi mota ya shige siddeeq ya shiga yaja suka bar gurin.
Budurwan Babbah Jin Haroon ya dawo farin cikine ya cike ranta Dan haka ranar ko islamiya qin zuwa tayi tai wanka ta shirya jiransa gashi har lokacin wayarsa Bata shiga Dan haka ta San bazai kwana ba Saiya taho ya ganta.
Su dadah ma Kwanciya hankalinsu yayi musamman Babbah da farko harya shiga damuwa Dan ya dauka rawa maganar auren take kokarin farawa shiyasa ma da Abdul aka kirasa Lagos maganar aikinsa dayaje Babbah ya Sakasa yayi masa bincike sosai akan Seelahs din Kuma suka samu yabo a gurin mutane da Dan abinda aka sani akansu Dan haka yaji ya sake samun nutsuwa da auren kodan yanda Ameenatou ya kwallafa son Haroon din a ranta.
A ranar Dasu Dad suka koma a washe gari aka buqaci zuwan Abdul Wanda hatta ticket din jirgi Siya masa Akai daga Abuja yabi jirgi zuwa Lagos acan ma cikin mutuntawa da girmamawa aka aika mota ta daukosa daga airport bar masaukinsa saida ya kwana ya wuni ya huta da kyau aka Kaisa SEELAHs CPN acan dinma Koda ya Isa anriga an samar da aikinsa Wanda zai fara a matsayin sabon secretary din Alh Lameenu na musamman.
Yayi godiya yayi farin ciki sosai hakama ya yaba Dan kuwa table dinsa ko a bankin da yayi aikin security sai manager ne yakeda irinsa.
Bai gama shiga shock da sabon farin ciki ba Saida aka basa gurin zaman da zai tattaro iyayensa ya dawo dasu sbd karatun Ameenatou da zata fara a Lagos din da Kuma saukin sha’anin aurenta.
Sosai ya Nuna farin cikinsa da yabawa tareda alkawarin yin duk iya kokarinsa da ladabinsa akan aikin harma da girmamawan gaske.
Saida ya Kara kwana biyu a Lagos din kafin ya dawo tukuna daga baya yayi Shirin komawa su Babbah sai daga baya zasu bisa.
Duk tsananin qiyayyar da sunan Lagos da Babbah Baya ko kaunar a fada hakanan ya danne a cikin ransa ya boye sbd farin cikin Ameenatoun Dake murna sosai akan karatunta da Kuma zama da zatai kusa da Haroon Koda yabar Nasarawan.
Ita kanta Dadah dayake sun Dade da dannewa da rufe Babin Omar gaba Daya kwata kwata rayuwarsu Bata nuna komaiba Dan ‘yarsu dai tayi girman da zasu iya Bata kariya daga kowa barshi uban nata da basusan ma Yana raye ko mace ba.
**Har yamma Haroon din Baizoba Dan haka Ameenatou tafara Bata fuska tana shiga fushi musamman da yaqi kiranta bayan Hafiz ya tabbatar mata Daya dawo.
Shigewanta tayi daki taqi fitowa kwata kwata a dakin take komai har dare tana fushi Babbah nata aikin rarrashi da Dadah.
Hafiz dai baima da lokacinda harkokin gabansa yakeyi sbd alamu sun nuna Haroon din ya sauya Kila sbd ciwon da yayi da Kuma Maida hankalinsa dayakeson yayi akan gaggawan kawo sauyi da mafita akan illar data rusa aikinsu gaba Daya.
Washe gari da safe tana tashi kashe wayarta tayi gaba Daya sbd ko Haroon din ya kira karya samu
Fitowa tayi sanye da doguwar rigar atampar A shape data zauna daidai jikinta hula data kasa rufe cikakkiyar gashinta me tsayi ce akanta tana son kunna wayar Amma tana Hana kanta.
Gurin Dadah ta nufa tace
“Dadah kisa Yaya Hafiz ya kaini gurin wanke kan fa ni kitso nakeso zafin kaina nakeji sosa”
Dadah datasan a fushi Ameenatoun take cikin kulawa da lallabawa ta kalleta tana gyara mata zaman hular kanta yanda ta sake mata kyau duk da gashin Bai rufe duka ba Yana daure a cikin hulan tace
“Dauko wayata na kirasa yazo yakaiki yanzun Nan”
Juyawa tayi ta nufi dakin dadahn ta dauko wayar ta fito ta Bata tana sake narke fuska kadan take Jira ta fara Hawaye.
#MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
41
Numbern Hafiz dadah ta Nemo a cikin wayarta ta Saka Kiransa
Ringing biyu ya daga waya Kai tsaye ta sanar masa yazo yakai Ameenatou gurin wankin kai.
Bata fuska yayi zai fara fada ta katse wayar bayan tace masa Maza kazo Ina jiranka kar yamma tayi.
Jin alamun Hafiz ya shaqa ya Saka Ameenatou dariyar da tin jiya taqi yi musu a gidan duk sbd fushin rashin zuwan Haroon din.
Ganin dariyarya ya Saka dadah farin cikin ta saki murmushi tana girgiza kan yanda fadansu da shiryawansu a a tare yake tafiya basa iya zama basuyi fada ba hakama basa iya zama a fadan Basu shiryaba.
Qin dawowa a lokacin Hafiz din yayi Saida ya gama abinda yakeyi ya dawo gidan Kai tsaye wanka yayi Yana fitowa Saida yayi sallan laasar kafin yace ya fito su tafi.
Yaya Abdul ne ya bawa Hafiz din kudin suka fice tana kokarin kunnasa da cewa turarensa qamshin rub yakeyi ba kamshi ba.
Dakatawa yaso yayi yace yafasa Kaita Ashe Yaya Abdul na bayansu zai fita yace
“Yi hakuri kyaleta idan kun dawo ka fasa bakin rashin kunyar kafin Babbah ya dawo”
Cikin Naam da Hakan ya wuce gaba Yana cewa
“Tarata nakeyi duk ranarda nayi cikakkiyar lokacinki zan nuna Miki ni ba abokin reninki bane.”
Yaya Abdul da yayi magana tana narke fuska zatai magana yace
“wuce ki bisa Dan idan ya tafi wlh Babu inda zan kaiki inda gurin zuwa”
Bayan Hafiz din tabi ta cimmasa suka fito gidan Yana cewa karta kuskura ta nuna masa reni a waje.
Cewa tayi ta yadda sbd itama tana tsoron yakaita gurin gyaran kan ya tafiyarsa yabarta.
Take suka kama wata firar suna mantawa da fada suka fito gida sunayi Yana Bata labarin sauyawan da Haroon yai ita Kuma tace ya Dena mata maganarsa fushi takeyi dashi Kuma duk ya sake kwana Baizo ya ganta ba ko ya kirata cewa zatayi ta fasa auren karatu zatayi.
Murmushin takaici ya sake Yana harararta sbd yasan yanda take son Haroon din fada kawai tayi bazata iya dinba duk da Shima Haroon din son dayake mata yafi Wanda take masa shiyasa yake mamakin abinda yasaka Yaki kiranta tinda ya fara rashin lafiyan Kuma yaqi zuwa gidan duk da ya dawo din Amma shi Yana masa uzurin tarin aikin dayake gabansa Mai tsananin mahimmanci ne kawai ya Saka Hakan.
Suna Isa gurin wankin kan ta shiga shikuma yace zaije ya dawo abinda bataso kenan Amma haka ya tafiyarsa yabarta Amma Saida ya Bada kudin ruwa da wani abin ci ko Sha idan ta buqata kafin a gama tukuna ya wuce din.
Dayake sun Saba da me saloon din ana kawo Ameenatou din tin tana yar budurwan yarinyarta harta kawo yanzu Dan haka tafara kokarin tambayarta Ina su dadah da Babbah harma da yayanta Abdul me kame fuska ba sakewa.
Murmushinta me kyau kawai tayi sbd da yawan lokuta batada sakewa da mutane sbd tsananin taka tsantsan da ake Bata da kulawa Bata wani yadda da mutane sosai.
Fira take mata tana mata wankin kan Wanda duk taji surutun ya isheta suna gamawa wankin kan kafin ayi drying kan ta kira Hafiz tace ya dawo ankusa gamawa.