AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE
Koda killer ya iso gidan BB ya tube yayo wanka dagashi sai underwear Wanda kusan Babu abinda na jikinsa da baka Gani.
Dakin suka nufa Yana miqawa killer hannu ya amsa fitinanniyar kwayar wadda take hade da ruwan alluran ta,
Tsananin karfi da balain dayake tattareda ita uku ake tanata asha Daya alluran Kuma tafi komai balai da masifa Dan hadda tsananin azabar gaske ne da ita Dan haka suna shiga dakin ya daga allurar Bai tsaya wata wata ba ya kama wuyan Haroon ya soka masa ita tareda dure masa ruwanta gabaki Daya Wanda yayi daidai da budewan idanuwansa cikin tsananin azabar da Bai taba samun kansa aciki ba take ya qame kaman Sanda kafin jikinsa ya saki gaba Daya Hawaye na gangaro gefen Idanuwansa da sukai duhu gaba Daya Baya ganin komai.
Sakin kansa BB yayi gaba Daya ya yanke jiki agurin ya zube kansa na bugawa da bakin table Dake gurin gashinsa na fashewa jini na fitowa ahankali ya lumshe idanuwansa Yana Jin jijiyan jikinsa kaman suna tsinkewan hakama jinin dayake jikinsa yana konewa cikin wata sanyayyar azaba Mai radadin gaske ga ganinsa gaba Daya ya dauke Baya ganin komai Baya Jin komai.
Dad Lameenu ne da BB ya kira tin Yana hanya ya shigo dakin bayan BB ya Bude masa kofar Yana kallansa tareda basa tabbacin Haroon din bayaji Baya ganin Komai.
Tsayuwa Dad Lameenu din yayi akansa tareda kallan BB Wanda Shima killer ya kalla aka Ciro kwayar killer na kokarin rabawa uku BB yace ya basa a Hakan.
Cikin tsananin firgici da tashin hankali killer din duk rashin imaninsa ya Kalli BB din sbd ko ukun idan aka ranata akasha ba qaramin Neman kashe mutum takeyiba bare duka Kuma har gida biyu.
Karban kwayoyin Yan kanana dasu BB yayi baiyi wata wata ba ya Bude bakin Haroon dayake kwance kaman gawan data rasa gatan suturtawa ya zuba masa su duka tareda karban ruwan da Alh Lameenu yake miqa masa ya zuba masa take suka wuce maqoshinsa.
Suna shiga kafin ma su fara aiki BB ya bari fuskansa da karfi tareda tayar dashi zaune duk da jikinsa asake yake Babu abinda yake Aiko a jikinsa.
Cikin tsananin mawuyacin halin da ko mara Imani Saiya zubar masa da Hawaye ya Bude bakinsa kansa na masa wani hayaqin masifa da balai yafara jijjiga Yana cewa
“Ameenatou itace ‘yarka Dad Omar, Dad Omar ka auramun Ameenatou sbd mutuwa zanyi idan na rasata, Ameenatou bazan taba barin kowa yasan itace ‘yar da ake nemaba ko da Hakan zaiyi sanadin Raina Dad Omar,
Babbah ku bani Ameenatou,
Jamaal ku bani Ameenatou,
Dad Omar ka taimakeni ka cika mun burin auren Ameenatou…….””
Sakinsa BB yayi tareda ja Baya da tsananin karfi jikinsa na daukan wani rawa da tashin hankalin da Bai taba tinanin shiga ba sbd Jin Abinda Haroon ke fada,
Shi kansa Lameenu Baya yayi da sauri Saida killer ya tarosa sbd firgici da shock din abinda yaji din.
Haroon kuwa sanqarewa yakeyi jini na fitowa bakinsa da hancinsa sosai sedai Bai Dena magana ba hakama jikinsa Bai Dena jijjiga ba.
Da sauri cikin masifaffen tashin hankali da tsoron abinda yake Gani da Wanda yaji Dad Lameenu ya Kalli BB Yana cewa suyi sauri su gogewa Haroon din jinin su mayar dashi inda zaa samesa kada ya mutu a hannunsu.
Suma Dake cikin tashin hankali sake shiga sabon tashin hankalin sukai sbd sanin waye Mam idan ‘dansa ya mutu a hannunsu Dan haka ba Bata lokaci suka daukesa suka Kai mota
Kusan motarsu data Lameenu a tare suka fice su sukabi wata hanyar Shima yabi wata.
Tafiya sukeyi suna gudu sosai suna kallan Haroon din Wanda yake zubarda jini sosai har lokacin cikin mafi tsananin azabar rayuwarsa da Bai taba jiba.
Tafiya me tsayi sukai kafin suka Isa inda BB din ya daukosa suka ajiyesa agurin suka gudu batareda kowa ya gansu ba.
Suna barin gurin motar siddeeq da shima ya shiga layin masu tsananin Neman Haroon din sbd zautuwan da Jamaal ke Neman yi gurin Nemansa Yana Sako Kai a layin Dan sake dubawa sai gashi kuwa yayi mummunan Gani Dan halinda ya samu Haroon din saura kadan ya buga zuciyarsa,
Bazai iya barin Jamaal ya gansa a wannan mummunan halinba Dan haka hankali tashe ya daukesa tsaban shiga rikici Kai tsaye Mansion din ya nufa dashi sedai Yan Isa ganin abin yayi muni Dad ya nema Kai tsaye sbd shi kansa jijjiga jikinsa yakeyi tsaban tashin hankali.
Mam na fitowa kallo Daya yayiwa Haroon ya Yanke jiki ya Fadi sbd zuciyarsa data buga irin bugun da zai iya kamuwa da shanyewan Rabin jiki mum Atee ce tayi saurin rikesa itama jikinta na daukan rawar tsoro da firgita sbd ganin abinda yafi karfin nata rashin Imanin.
Daukansa Akai aka nufi ciki dashi Kai tsaye bangarensa Akai dashi zuwa lokacin jikinsa sake sanqarewa yakeyi Dan haka suna Isa Kai tsaye toilet siddeeq ya wuce dashi ya Saka a bathtub din dayake cike da ruwan sanyi.
Dad kasa tsayuwa yayi ya qarasa gurin Haroon din dayake sanqare acikin ruwan jini har lokacin Yana fitowa ta hancinsa.
Wani irin kukan da baisan yanada shi bane ya fashewa Dad din Yana ihun ambatar Haroon din daidai Nan Lameenu yashigo Shima kafafunsa na rawar tashin hankali da tsoron abinda zai iya biyo Baya.
Kamo Haroon din yayi Shima Yana ambatar sunansa sedai Haroon Babu abinda yake ji a lokacin.
Sosai jinin yake sake gudu Wanda ya Saka siddeeq kasa riqe kansa ya kira Jamaal Wanda yaketa bulayi a titin Lagos Yana Neman Haroon din Yanajin abinda siddeeq ya fada Kai tsaye ya juyo motarsa kaman zai tashi sama yayo mansion din.
Isowansa yayi daidai da wani tarin jinin gaske da Haroon ya feso daga bakinsa Mai yawa jikinsa na qarasa sakewa gaba Daya a jikin Dad Wanda yake rungume da Haroon din qamqam Yana Jin Abinda Bai taba ji ba na ganin zaka rasa Wanda kake tsananin so da dukkanin rayuwarka.
Ganin Dan uwansa ya Saka Jamaal karasawa kafafunsa na Neman sarewa hakama zuciyarsa koina yankewa yaji tana yi.
Dad Lameenu da sauri ya janye daga Haroon din ya bawa Jamaal guri.
Hannuwansa duka biyu yakai cikin ruwan ya kamo Dan uwansa Yana fitowa dashi sbd gaba Daya jikinsa ya lalace da jini
Bai tsaya komaiba ficewa yayi dashi daga dakin ya fita dashi Dad Wanda ya kasa motsawa daga inda yake tsaban mutuwan dayakejin duka jikinsa yayi Babu inda ke motsuwa mum Atee ce ta kamasa suka fito suma suka marawa Jamaal din Baya.
Asibiti Jamaal ya nufa dashi cikin gaggawa aka karbesa sedai hadda Jamaal din aka shiga sbd samun damun tsayar da jininsa da ya zube sosai Dan take jininsa ya fara yin qasa.
Dayake da yawan manyan doctors din asibitin sunsan Dr Jamaal Seelah din baa hanasa shigaba Dan shine ya tsayar da jinin sedai ana buqatan jinin sakawa Jamaal din da gaggawa take ya kwanta aka fara diban nasa ana sakawa haroon din Wanda ya koma daidai sedai Babu inda yake motsi a jikinsa yayi fari fayau a cikin kankanin lokaci ya koma abin tausayin da zaka dauka shekarunsa ashirin a kwance.
A waje kuwa Dad da mum Atee da siddeeq ne sai Dad Lameenu da mummy Sarat duka tsit gurin ya dauka bayan Kaida kawo Babu abinda siddeeq keyi su kuwa Dad aketa Neman Kiran likita ya dubasa sbd jininsa yayi mummunan hawan dayake buqatan maganin gaggawa Shima.
#MAMUH
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_