AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE
Yana isowa gurin Omar ya ajiye cup din hannunsa tareda miqewa tsaye ya ware masa hannuwansa suka rungume juna.
Qamshin Jamaal din Mam ya shaqa da kyau yaji bana Jamaal din bane sbd yasan Babu wani qamshi da a duniya zai Saka Jamaal sauya nasa.
Lameenu ma qamshin Haroon Daya shaqa din ya Saka zuciyarsa Dake tsallen rawa Dan daidaita Yana miqa hannu ya zari tissue din gabansa ya Dan goge goshinsa Yana kallan Mam Wanda yake a natse hankali kwance sedai tasa zuciyar aciki tafi ta lameenu shiga wani irin firgita da karyewa Dan ya dauka Jamaal ne ya bayyana gabansa.
Cikin nutsuwa Jamaal Daya dago yana kallan Dad Omar bayan sun saki juna da sauti mara karaje ko sauri yace
“Dad Omar barka da dawowa”
Muryan ya Saka Dad Omar sake kallansa sbd Haroon ne da sauran yayansu ke kiransa Dad Omar Amma Jamaal Dad J kadai yake ambatarsa dashi.
Yanda Jamaal ya fuske bayan maganar Yana rungume Ahmed Wanda ya miqe cikeda farin cikin ganinsa da kaunan dayake masa Shima Mai tsananin gaske Yana cewa
“JAMAAL my man”
Murmushi Jamaal din yayi Yana Dan janyewa yace
“Haroon ne, JEEY Bai isoba tukuna Banda tabbacin ma idan zaizo din”
Dad Omar dayake kallan fuskansa wani murmushi me kyau ya sake Yana dauke kallansa daga Jamaal din Yana cewa
“Haroon Yaya hidiman?farko daya iso Nima na duka Jamaal dinne sai daga baya na gane,
Kamannin nasu nata sake rudarwa haryanxu dai.”
Ahmed ma Yana zaunawa yace
“Ni haryanxu bana banbance su,
Barr Yaya hidiman?
Inshallah zaka samu farin ciki da zaman lafiya da Kwanciyar hankali me dorewa bayan auren,my wishes kenan.
Murmushi Jamaal yakeyi Yana cewa “thank you, thank you”
Bai tsammanin tararda su Dad tareda Dad j dinba Dan haka dole ya sake Yana murmushi da sakewa sosai kaman yanda Haroon yakeyi sbd har lokacin Daya gaida su Dad din idanuwansu dai a kansa suke sun kasa tantance mema suke Gani ko ciki,
Dad Lameenu idan ya shiga wani hali Baya iya boyewa da wuri ake gane Hakan a tareda dashi sbd tinda jamaal din ya taho gurin duk da sun shiga shock a farko Amma ganin dai da gaske Haroon dinne Amma kwata kwata ya kasa Dena hada zufa karshe dai haka ya ringa Neman rikicewa a zance.
Mam kuwa hankalinsa kwance yake ci gaba da maganarsa suna tattauna ci gaban da Haroon din yake samu sosai ayanzu akan manyan ayyukan dayake handling da yanda zai karbi babban nauyi akansa bayan auren.
Sun jima sosai a gurin kowa da abinda yake zuciya da cikinsa hakama kowa a tsananin mace yake Daya tashi yaje ya tattauna abinda yake ransa Amma hakanan kowa ya fuske suke cigaba da fira cikin walwala da farin ciki.
Sallan azahar ne ya rabasu bayan sunyi sallah kowa ya wuce Dan hutawa a gida.
Suna rabuwa Mam da lameenu office suka nufa,
Suna shiga Dad Haroon ya kira a waya Kai tsaye yace masa
“Menene Dayan alkawarin daka mun bayan na project????
Haroon dayake zaune a dakin Jamaal Yana cin abincin dayayi order Yana Jin tambayar yasan me Hakan ke nufi Dad Yana zargin Haroon din dayake gabansa Dan haka Kai tsaye yace
“Alkawarin Nemo Maka duk inda Magajin Dad Omar yake Kokuma bayanin da zai nuna mana inda yake”
Numfashi Dad din ya sauke kafin yace
“Kazo yanzu Nan Ina office ka sameni Kuma ka zo da takardun aikinsu Chris Jeremy.”
Kashe wayar yayi Yan kallan kofa sbd ya ji abinda yakeson ji Amma Kuma idan har da gaske ne zai gane idan Haroon din ya shigo.
Haroon na kashe wayar siddeeq yafara kira ya sanar masa inda takardun suke ya dauko Kai tsaye yakaiwa Jamaal Daya fito sallan tareda Dad Omar sunason magana Amma dai dama Dan haka address kawai Ahmed ya bawa Jamaal Kai tsaye ta waya da time a yau din zuwa dare.
Haroon Kiran Jamaal din yayi hankalinsa tashe tsoro na ciked zuciyarsa ya sanar dashi abinda sukai magana da Dad din a waya kafin Jamaal din ya nufi office din Dad din.
Koda ya shiga Dad Lameenu Yana tsaye Yana Kaida kawo sbd haduwan Jamaal da Omar su nasu yazo karshe Dan Basu iya da Omar dinba shi kadai bare Jamaal da kaman ma su da suke iyayen sune suke tsoronsa sbd zai iya ruguzasu tinda yasan hanyoyin yin qasa dasu.
Mam kuwa Jamaal din na shigowa ya miqa masa hannu Yana kallansa yace
“Takardun Menene wannan din?
“Chris Jeremy’s” ya Bada amsa Kai tsaye Kansa a kasa.
Dad na Jin Hakan ya jefar da takardun kan table Yana fuskantar Jamaal din yace
“Menene kake Jira haryanxu akan alkawarin daka dauka?
Kana ganin Dan gobe ne daurin auren Nan bazan iya dagasa fa har Sai abinda mukeso ya tabbata”
Dagowa Jamaal yai ya Kalli Dad din Kai tsaye Shima yace
“Ni nafara cika nawa farkon alkawarin komai ya tafi daidai sauran alkawarin da kayi na tabbatarda ka auramun yarinyar a gobe…….
Wuta Mam ya dauke Dad Lameenu kuwa dakatawa yayi daga Kaida kawon dayakeyi cikin rudewan zuciya da Kai Daya dauki zafi ya dawo gaban Jamaal din ya tsaya ya juya ya kalli mam dayake Jin kansa Shima Yana daukan wuta kafin ya sake dawo da kallansa Kam Jamaal kafin yayi magana cikin tsananin zafi da bacin Rai daya rufe Mam idanuwansa na rufewa zaiyi magana Lameenu yayi saurin taresa da cewa
“Ba lokacin fada bane muna tsananin buqatan sanin wani abu gameda magajin Omar ko yayane Kamun gobe a daura auren Nan,
Ana daura auren Nan zai juya ya tafiyarsa yabarmu batareda mun sani sani akan abinda ya sakamu tilasta masa zuwan na,
Jinina tafasa yakeyi Kuma bazai daina tafasa ba zuciyata bazata daina bugawan tashin hankali da baqin ciki ba idan bamu samu sanin abinda mukai shekarun Nan ba muna bibiyan son sani,
Rayukan da aka kashe duka an kashesu a banza,
Har matar Omar din dana yanka cikinta aka kashe duka an kashe a banza,
Hakama su kasim da jamilu da muka kashe da hannuwanmu duk da zamansu jini da Rabin jikinmu tin farko duk anyi a banza,
Duka a banza idan har daga karshen Nan bamu samu sanin abinda Omar ya haifaba da inda yake muka hadasa da Omar din muka kawar dukiyan ta shigo hannunmu,
Duka wannan komai da komai zai tashi a banza idan dukiyar Nan Bata dawo tamu ba,
Zamu rasa komai,zamu koma Asalin zero agaban Omar…..”
Maganganun cikin tsananin zafi da radadi tareda tafasar zuciyar yake fadansu idanuwansa jajir Dan kuwa an daura auren kaman yanda suka samu labari Haroon kasar zai bari Dan su BB sun kawo masa tabbacin Haroon din yakai Ameenatou anyi mata passport ba tareda saninsu ba bayan sun San ko garin Lagos Haroon Baya bari Saida izininsu.
Jin wannan maganar a bakin Lameenu ya Saka Mam Jin kansa ya qarasa daukan zafi Shima zuciyarsa wani zafi takeyi a quntace ya kalli Jamaal da idanuwansa sukai wani irin mugun jajir hannuwansa na wata irin rawa ya dunqule hannuwan sbd rawan da sukeyi tayi yawan dayake Jin zai iya raba Dad Lameenu Kamanninsa na asalin mutum Dan haka juyawa yayi kirjinsa na nauyin da Saida yayi saurin dafesa Yana dafa table din gabansa sbd wani mummunan jiran Daya dubasa kansa ma Neman kasa daukan abinda kunnuwansa suka ji masa yakeyi sbd sunayen dayaji suna ambatar sun kashe da hannuwansu,
Mutuwan granny dinsa Dayake matiqar kauna yaji a bakin Lameenu cewan Dad ne……wani irin sarewa kafafunsa sukai take ya durqushe a Gurin Yana riqe hannuwansa Dake tsananta rawa da zufa me tsananin gaske amma har lokacin Babu Wanda ya tsaya lura da yanayinsa sbd a rikice suke Suma da tashin hankalin Dan sun tabbata Jamaal na tafe wlh.