AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE
Kallansa Dad Omar da idanuwansa sukai jajir yayi sbd Babu abinda Jamaal zai rokesa a rayuwarsa yaji bazai iya basa ba Amma kuma yanzu ana magana ne akan ‘yarsa da Bai hadata da kowaba hakama tafi komai na duniyar Nan Daya mallaka mahimmanci da daraja Mai girman gaske a zuciyarsa.
Babbah a nasa bangaren farin cikin Ameenatou ne kadai abinda yake tsaye a ransa,
Tsananin Son da Ameenatou kewa Haroon shine babbar matsalar Dake tayar da hankalinsa Dan kuwa Babu wani abu komai girmansa da zai ciresa daga zuciyarta…
Omar kuwa Jamaal Dayake cikin tsaka me wuyar gaske akan Dan uwansa ya kalla Yana Jin abubuwa da yawa a zuciyarsa gameda auren Wanda zaifi farin ciki da Jin dadin tareda samun cikakkiyar nutsuwa ko bayan mutuwa ace Jamaal ne igiyoyin auren ‘yarsa suke hannunsa,
Auren Ameenatou tamkar wani babban nauyin da mutum baisan dashine ba zai dauka Dan kuwa dukiyarta gaba Daya nauyinta akansa zasu sauka,
Haroon bazai taba iyawaba sedai Kuma so yayi gaggawan shiga lamarin nasa da Ameenatou Amma Kuma aurenta ba abune Mai saukin gaske ba garesa,
“Jamaal kayi mun alkawarin zaka tsaya ka tsayu ka zama kariya ga ‘yata?
Ka mun alkawarin zaka Hana duk wani cuta tarwatsa rayuwanta?
Kamun alkwarin ko Dan uwanka zaka tsayu gabansa ka zama katangar karfenta idan ya kasa Bata kariya da tsaron Daya kamata,
Idan na bawa Haroon auren ‘yata ka sani shi auren na basa Amma Kaine na bawa Amanarta ta har abada,
Ni amatsayin mahaifin Daya haifeta Kaine na bawa aurenta da kaina kaikuma ka karbanwa Dan uwanka Dan haka idan har ka Aminta shi ka bawa auren tabbas bazan Hanaka ba sedai Kasani har abada ni Amanar ‘yata na baka Kaine ka aura mata Dan uwan naka.
Jajayen idanuwan Jamaal ya dago Babbah ya fara kalla Wanda Shima shi yake kalla zuciyarsa na rawa hakama jikinsa amsarsa suke Jira Dan dai shi Kam Babbah bayajin zai aminta da auren sedai kafin yayi magana Jamaal ya fadawa Dad maganganun da suka hatta jikin Babbah yin sanyi baisan lokacinda Hawaye suka sake gangaro masa ba sbd yanajin tabbas Shima ya amince a aurawa Haroon din Ameenatou sbd Jamaal ya kashe musu jiki da alkawarin Daya dauka tareda Amanar Ameenatou Daya tabbatarwa dad din idan har su Dad dinsa sun samu damar taba ko suturar jikin Ameenatou da dukiyarta to bayan ransa ne Inshallah.
Ahmed Daya kasa riqe kansa akan tsananin kaunar dayakewa Jamaal rungumesa yayi sbd Daman yasan Jamaal namijin gaske ne ko Dad Omar baice komaiba jininsa yafi karfin ganin cutatarwa indai Jamaal Yana sane,
Kaunar datake tsakanin Jamaal da Omar kaunace irin ta asalin ‘da da uban da suka hada jini,
Yanda yake Jin Dad Omar ko mahaifinsa Baya jinsa a cikin ransa Hakan,
Shi kansa Omar yanda yakejin Jamaal ko ransa ko cewa Yayi yaje da kansa ya sanarwa su Mamman waye yarsa zaiyi sbd yasan bazasu iya komai Dan itaba.
Rungumesa Ahmed yayi Yana Jin nauyin dayake zuciya da kansa sun rage na alkwarin bawa Omar da ‘yarsa kariya Koda da rayuwarsa ne.
Har lokacin Jamaal zuciyarsa wani irin nauyi da daci ne danne da ita Dan haka Dad Omar ma dayake Jin nauyi da tsananin dacin zuciya rungumesa yayi sai alokacin hawayen Jamaal din suka gangaro daga idanuwansa Shima Dad Omar sai alokacin nasa suka gangaro Dan Bai taba zubda Hawaye ga rabuwarsa da Yan uwansa ba sai yau din Badan abin Baya cin zuciya da ruhinsa ba sai Dan baisamu Wanda daidai irin radadin ne aransaba sai yau din Dan yasan radadin dayake ransa shine yake ran Jamaal.
A cikin daren Omar ya sanar dashi komai daya Dade a rubuce na sunan AMEENATOU dayake kan komai na Abinda ya mallaka Dan haka Babbah yaji hankalinsa ya sake tashi Dan kaman sun sake nutso ne shida iyalansu da Ameenatou din cikin wutar qaddarar da zata kona kowa Dan haka take yaji zazzabi da ciwon kirji na rufesa,
Jamaal ma ciwon kan ne tareda zazzabin gaske ya rufesa sbd kirjinsa Daya toshe Dan haka cikin karfin hali ya fito kusan su babban da Dad Omar na bayansa suka fito gurin sedai babban tashin hankalin da suka tarar a wajen ne ya Saka jiri diban Dad Omar da Jamaal lokaci Daya sbd tabbatarda motar Haroon ce a gurin pake.
Ahmed ma dayake cikin shock saurin tare Omar yayi Yana kallan motar da tashin hankali yace
“Haroon Yana gurin Nan??
Babbah na Jin Hakan jiri ya zubar dashi jikin motar Omar Dake gurin Yana ambatar “Qalu innalillahi wainna ilaihirrajiun.
Jamaal Daya ji kansa na sake daukan masifaffiyar zafi da sauri ya nufi motar yaganta a rufe
Ahmed da Shima cikin tashin hankalin ya zagaya Baya ya zagayo koina gidan baiga Haroon dinba ya dawo saiga key din motarsa a kasa gurin yashe.
Babbah na ganin Hakan yayi zaman Yan bori a gurin Yana cewa
“Shikenan haukarsa ta motsa zaije ya sanar WA mahaifinsa”
Zabura yayi da sauri ya nufi Omar Yana cewa
“Wallahi tinda baida cikakkiyar lafiya tsaf zai iya sanarwa ubansa,ku yi wani abu Akai ko wlh tallahi a cikin Daren Nan na tattara iyalina ku nememu ku rasa wlh ko zaka sake ganina sai qiyama idan mun hadu gaban Allah.”
Dad Omar da Baya ma gane me Babbahn ke fada motarsa ya nufa Dan sauri Shima Jamaal tasa ya nufa Ahmed ne yasamu karfin halin Jan Babbah ya jefa mota ya rufe suka tayarda motacinsu kaman masu wasan tsere cikin mugun gudun Daya Saka Babbah sake shiga tashin hankali suka hau titi su sukai kudi shi yayi arewa kowannensu Yana Saka Kiran wayar Haroon din ba kakkautawa.
Jamaal kaman zai tashi sama haka ya figi motar Yana Saka Kiran Haroon din idanuwansa na rikidewa gaba Daya Dan kuwa kowannensu tsoronsa kada Haroon din ya nufi su Dad Dan haka tabbas yaji wani abu shiyasa ya bar gurin a halinda basuda tabbacinsa tinda ga key din motarsa yashe a gurin.
#MAMUH#
#JAMAAL JEEY SEELAH
#AMEENATOU JDEN SEELAH
#OMAR JDEN SEELAH
#MAM SEEELAH
#LAMS SEELAH
#THE SEELAHS
#WAR
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_AMEENATOU_*
_Mamuhgee_
#Arewabooks@Mamuhgee
#ZafafaBiyar
#BestLove
54
BB kuwa Kai tsaye gidansa ya nufa Dan Haroon din Kuma harya Isa Bai Hadu da wata matsala ta jamian tsaro ba Dan haka Yana Isa yayi parking motarsa a harabar gidansa ya Bude ya fito ya zagayo ya Bude motar ya dauko Haroon din Wanda ciwonsa yakai kololuwan tashi sai fizga yakeyi Yana jijjiga kansa Yana buga kan a jikin hannuwansa idanuwansa a rintse.
Kai tsaye Dayan dakinsa yakaisa ya zubar a kasa tareda juyawa ya fice daga dakin Yana Ciro wayarsa ya Saka Kiran babban yaransa.
Yana daukan wayar Kai tsaye BB yace
“Killer ka kawomin Ps biyu yanzun Nan”
“Yes oga” killer ya fada daga bangarensa Yana kashe wayar tareda ture macen datake kansa tana lashesa kaman sweet har Saida kanta ya bugu da Bango ko a jikinsa ya miqe tsaye Yana kama dadar kansa datake a watse ya Saka Roba ya daureta tsakiyar Kai Yana nufar toilet ya wanko jikinsa ya fito,
Underwear yafara sakawa kafin ya Saka Jean Akai ya Saka shirt ya dauki wayarsa da key din motarsa yafice bayan ya shiga dayar dakinsa da mugayen kwayoyin rayuwa suke ciki ya dauko wadda ogan ya buqata.