AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#Arewabooks@Mamuhgee
#ZafafaBoyar

 

55

Dad Omar ma tin kafin a ga Haroon din jininsa yahau Shima har yana Naman zubewa dole Ahmed ya dawo dashi gida Shima aka Nemo likita.

Babbah ma a gida likitan aka Nemo sbd take ya rafke zuciya na ciwo sosai hankalin nasa Iyalin yayi mummunan tashi.

A cikin Daren abubuwa da yawa sun faru marasa dadi da tashin hankali tareda Saka hawan jinin mutane da dama,

Sai guraren asuba Haroon ya farka sedai cikin yanayin Daya Sakasa tsiyayo da Hawaye masu zafin gaske Yana kallan Dan uwansa Dake gabansa zaune Yana kallansa idanuwansa jajir
Ko baa fada ba yasan irin radadin dayake zuciyar JAMAAL bamai faduwa ne ba,

Wani numfashi Mai dumi ya sauke ahankali hawayen cikin idonsa na gangarowa yanason magana Amma ya kasa sbd baisan me zai fada ba,

Abu uku zuciyarsa a yanzu kadai take so sbd samun sanyin da sassaucin azaban dayake ji na cin jininsa,

Ganin mahaifiyarsa,ganin Ameenatou da Kuma Jamaal din Wanda shi gashinan a gabansa.

Ahankali ya Bude bakinsa cikin sanyi da karfin hali yace

“Nagode”

Sukan Jamaal kalmar tayi Dan haka ya miqe tsaye Yana kokarin danne tausayi da tsinkewan da zuciyarsa keyi tareda nauyin dayake ji a kirjinsa yace

“Ka manta yau daurin aurenka???

Murmushi Haroon din yayi Mai sanyi kafin yace

“Ban manta ba shiyasa nayi Maka Godia.

Magana yakeson yi Amma bazai iya ba sbd hakanan zuciyarsa da bakinsa basa son furta komai bayan idanuwansa Daya zubawa Jamaal din Yana kallansa jikinsa na mutuwa hakama idanuwansa sunyi jajir.

Shima Jamaal Jin yayi bakinsa da zuciyarsa sunyi nauyi sosai bazai iya cewa komaiba bayan yin shiru suna sauraron numfashin junansu.

*******Mam a cikin Daren Lameenu daya kasa zama ya kasa tsayi yasaka BB ya kawo musu rahoton abinda yake Neman zautashi tinda yaji a bakin Haroon.

BB a cikin asibitin ya sanar da Mam wacece ‘yar Omar Jaden da Kuma alaqarsa da Babbah akan cewa shine da kunnensa yaji lokacinda ya bisu.

BB na gama fada Lameenu ya sauke ajiyan zuciyarsa Dake cikin balai da masifa tinda yaji zancen shi kadai,

Maganar da farko kaman a mafarki Mam ya jita Saida ya dago idanuwansa da sukai jajir ya Kalli BB
BB din ya jinjin masa Kai alamar haka zancen yake.

Da hannu Mam yayi musu alama dasu kira masa likita numfashinsa tsayawa zaiyi.

Da sauri BB ya fice ya kirawo likita Wanda y dawo dakin tareda Mum Atee da itama tana asibitin Taki tafiya.

Tsaban tashin hankalin firgitan da Mam yayi Saida aka Saka masa oxygen na wucen gadi daqyar yakai asuba sbd tinane tinane da sakawa da warwarewa.

Asubar fari yaji dukkanin ciwonsa dayake ji a jikinsa ya warke,
Bai taba sanin Kowane ‘da da baiwar da Allah yayi masa ba da kalan arzikinsa sai yanzu,

Haroon ayau ya tabbatar masa da Hakan sbd zai basa abinda yayi shekaru Yana nema tin kafin ya Saka ran haihuwarsuba,
Bai taba Saka ran duk wannan tashin hankalin da sukaita fama dashina karshen dukiyar Omar a gidansa zata dawo,
Wannan auren shine babbar taskar arzikinsa Daya Dade Yana kashe kashe gurin mallaka,
Wannan auren da yace bazaiyiba ayau Yana tabbatarwa kansa idan baayi auren Nan ba to shine Baya raye Amma wallahi tallahi Babu Wanda zai Hana auren Nan dauruwa ayau kaman yanda ayau din Omar Zai bar duniyar dukiyar tashiga hannunsa da dalili….

Lameenu da Mam din ya Sakasa zuwa asibiti gurinsa tin asubar fari gama tattaunawa sukai inda kansa ya shiga wani zafi da duhu ya shiga lissafin abinda zai faru Idan auren ya tabbata.

Wannan auren idan anyi sa Ameenatou Jden ta zama matar Haroon sirikar Mam ayau Kuma idan Omar ya mutu gadonta na dukiyarsa gaba Daya zata zama a karkashin mijinta wanda dukiyar gaban dayanta zata koma ne akan yanzu gadon sirikar Mam ce ba tasu ba da zasu mallake su Raba tsakaninsu.

Jin yayi kansa na Neman kuncewa da lissafi Amma Kuma ko yayane su Raba Omar din da duniyar tukuna zasu fuskanci juna shida Mam din akan dukiyar sbd tabbas dole kasonsu me tsoka Yana cikinta.

Mam ne ya shiga dakin da Haroon yake kwance sedai idanuwansa biyu har lokacin shida Jamaal Babu me magana sai da Dad din ya shigo Jamaal ya fice ya basu guri dad din ya Kalli Haroon Wanda Shima Haroon din shi ya kalla Yana Jin tausayin mahaifin nasa akan rayuwar Daya samu kansa Dan haka yake Jin inama zai iya sauya Dad din dayayi Hakan.

Sunansa Dad ya ambata cikeda kulawa da farin ciki shimfide a fuskansa Yace

“Haroon Allah ya albarkaci rayuwar da zaka fara daga yau dinnan har ranar tashin qiyama,
Allah ya haskaka zuciyarka yanda ka haskaka tawa,
Allah yayi Maka kyakkyawar karshe ya albarkaci zuriar da zaka Haifa.”

Hawaye ne kawai suka silalo daga idanuwan Haroon sbd Bai taba samun wannan kyakkyawar adduar Mai dadin sauraro daga mahaifin nasa ba Dan haka ya rintse idanuwansa jikinsa gaba Daya na yin sanyi da mutuwa ahankali ya Bude bakinsa cikin kaunar Dad dinsa da har lokacin yakeji yace

“Amin Dad nagode Allah ya Saka da Khairan,
Allah ya tsarkake Maka zuciyarka ya wanketa Dad ya Kuma baka ikon gyarawa da tubar masa”

Shima Dad din cikin farin ciki da tsananin kaunar dansa yace “Ameen Haroon”

Jamaal ne ya dawo dakin daukeda takardun Haroon din Daya karbo dasu zai tafi akwai binciken da zaiyi akansu.

Duk da rashin karfi dayake jikin Haroon din hakanan Jamaal ya daukesa daga asibiti sbd bazai taba barin a daga daurin auren ba daga ranar sbd hakanan a yanzu zuciyarsa tafi ta Haroon cika da tsoron Da baisan na Menene ba Idan ba ganin yayi igiyan auren Haroon din sun rataya akan Ameenatou ba.

Dad ma bayajin akwai abinda zai Hana wannan auren ayanzu Dan haka gida suka dawo kowa na kokarin fara Shirin daurin auren Wanda zaayi da karfe goma Sha Daya na rana.

Dad Omar ma hankalinsa kwantawa yayi Daya samu tabbacin su Mam Basu ma samu damar magana da Haroon ba tin jiyan Dan haka yasan sirrinsu Bai fita ba Dan haka ya kira Babbah Wanda Shima yake a tsinke tini ya sake yafara Shirin daurin auren shi dasu Hafiz da zuciyoyinsu suke cikin farin ciki Mai tsananin gaske.

Amarya Ameenatou kuwa da batai waya da Haroon ba sai da safen Jin tayi kaman yayi mata caji Dan haka ta sake daga sanyin jikin datake fama dashi yin jiyan zuciyarta da kirjinta na nauyi.
Dan haka ta sake Wainda suka taho shirinta ta Basu Daman shigowa inda take Dan fara shiryata sbd daurin auren ma ya kusa ga gidan nasu a cike yake sosai da Yan bikin gashi Babbah yace bayan daurin auren zai sanar da ita abinda Bai taba sanar da ita ba Mai tsananin mahimmanci Dan haka duk ta sake zaquwa da ayi daurin auren ta zama ta Haroon ya zama nata.
Wannan tinanin kadai sake narkar da zuciyarta yakeji cikin farin ciki Mai sanyin gaske.

******A yanzu kusan dukkanin seelah Babu Wanda tin daga zuciyarsa yake cikin tsananin farin ciki da wannan auren ba Dan haka sosai ake cikin annuwan gaske Dan haka tini suka kammala nufinsu da komai akan Omar Wanda Shima yake cikin nutsuwa da farin ciki Dan ana daura auren zasu tafiyarsu hadda Haroon din da Ameenatou da Jamaal shiyasa ma suka dakatar da Dr Aleena daga zuwan tinda Nan zasu taho.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected