AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE
Haroon ya Jima a gidan Shima kafin ya fito Kai tsaye ya nufi ganin amaryansa.
A Daren Ahmed da Omar suka fita sedai Bai nufi gidan Babbah Kai tsaye ba Wanda suka samu bayanin komai nasa da gidansa,
Zuwa gidansa Kai tsaye yanada hadari Dan haka masallacin da babban yake sallah ya nufa Dan yin sallan ishai acan.
Babbah tareda Abdul da Hafiz suka fito daga gida suka nufi masallaci kowanne da sauran ruwan alwala a fuskansa Hafiz na latsa wayarsa Babbah na masa maganar meyasa yake zuwa da waya masallaci Hakan baida amfani tinda ba dadewa zaiyiba a masallacin.
Shiga masallacin sukai Babbah ne a gaba kafin su a bayansa suna shiga suka shiga sahu
Ana kokarin tayarwa Ahmed da Dad Omar suka shigo masallacin Kai tsaye gefen Babbah Omar ya tsaya Yana gyara tsayuwansa Dan tayarda sallan Ahmed ma gefen Omar din ya tsaya Yana gyara nasa tsayuwar.
#MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
48
https://chat.whatsapp.com/K3rO5UonX4GDVxtQbA5mZl
Assalamualaikum wa rahmatullahi ta’ala wa barakatuhu!!! Wannan group din dai na komai da komai ne. A taiqaice
*Farashin mu na daban ne compared to sauran Yan kasuwa
*Kaya masu kyau da quality. Abinda kika zaba shi za a Baki
* Swift delivery.watau waybill a sauqaqe da Yardar Allah
* Muna sake New Arrivals ka fin su cika Gari
* Muna iya duba maku kaya a good price ko da ba namu ba ne idan kuka Aiko da hoton kayan
Allah sa mu qaru da juna Ameen
***********
Babbah da baisan waye a gefensa ba sbd ya riga ya tayar da sallansa Dan haka hankali kwance da nutsuwa yake sallan hakama suma kowa ya natsu a cikin jam’in.
Dun Yana sallah ne Babu filin tinanin komai a zuciyarsa Amma dai Kuma ya tabbatarda ko waye a gefensa bako ne a masallacin Kokuma babban mutum ne sosai Dan qamshinsa me sanyi da nutsuwa ya tabbatarda Hakan kusan a duka sahun Babu Wanda qamshin me sanyi Baya shiga hancinsa.
Ana sallame sallar Babbah yana juyowa zai gyara zamansa idanuwansa suka sauka akan fuskan Wanda yake kusa dashi din take salatin daya debo daga bakinsa ya bace masa bat.
Juyawa gefensa Daya dasu abdul suke zaune yayi yaga hankalinsu Baya kansa adhkar kawai sukey,
Juyawa yayi bayasan yaga kowa abinda yake gabansa yakeyi da sauri ya sake dawo da kallansa gefen nasa ya sake kallan fuskan Omar ya kasa yadda da idanuwansa Gani sukeyi daidai Dan haka ya ambaci sunan Hafiz a hankali cikin nutsuwa yace
“Wannan bawan Allahn Dake gefena ka taba ganinsa a kuwa??”
Kallan Omar Dake zaune hankalinsa kwance Yana addua yayi yaga kwata kwata idanuwansa basa kansu hakama da alama lafiyayyan Mai abin duniya ne dan daga nutsuwansa da motsin jikinsa kadai zaka gane Hakan.
Girgiza Kai Hafiz yayi ahankali Yana dauke kallansa daga kan Dad Omar din Daya Burgesa Kai tsaye sbd wani sanyayyan kwarjininsa Daya cike idanuwansa dama duk Wanda ke kallansa Dan kaman kusan yakusa zama bature Dan fari ne sosai farin ma na Hutu.
Numfashi me dumi Babbah ya sake saukewa a karo na kusan biyar kafin ya juyo idanuwansa da suka sauya take ya Kalli Omar din baice komaiba Shima Omar din baice komaiba sai hannu Daya miqawa babban Yana Dan sake fuska da muryansa me Kamala yace
“Assalam alkm”
Cikin karfin hali babban ya miqa masa hannun Yana amsa sallamar Kai tsaye batareda ya kallesa ba kafin ya miqe tsaye Yana wucewa yabar masallacin.
Su Abdul cikin girmamawa sosai suka gaida Dad Omar din Wanda ya miqa musu hannu Shima Daya bayan Daya sukai musabaha Yana kallansu cikeda kauna da kulawa kafin suka bi bayan Babbah sedai suna fita suka tarar da ya bace musu da alama ya kama hanyar gida.
Hanyar gidan suka kama Hafiz na fidda wayarsa daga aljihu Dan Saka kira Abdul kuwa Kai tsaye hanyar gidan ya kama sbd zai fita da Dadah siyayyar turarukan wutan da zasuje yi itada umman fadila na MEERAH B PALACE masu fitinanniyar kamshin da duk amaryan datai amfani dashi Babu ta yanda bazata Hana zuciyar duk Wanda ya shaqa zaman lafiya ba Dan qamshine da a iya gurinta ne kadai ake iya samunsa.
Dayake washe gari ne kadai bazaa daura auren ba Dan haka Gyaran da akewa Ameenatou din ya koma so Daya a wuni maimakon so biyu sbd sauyin datai yayi yawa gaba Daya bazaka taba ganinta Kai tsaye ka dauka budurwan Babbah bace.
Babbah daga cikin masallacin Kai tsaye wani gurin ya nufa yaqi nufar gidansa Dan Bayaso abinda zai Kai Omar gidansa Kokuma abinda zai Saka a gansa da Omar ko a mafarkinsa kuwa Dan har abada baida alaqa dashi,
Alaqan Dake tsakaninsu sun Riga sun yanketa sbd shine kadai abinda ya Saka Ameenatou dinsu take raye,
Aurenta shine abinda zai sake Bata tabbatacciyar tsari daga mahaifinta da masu bibiyansa sbd zatai aure gidan arzikin da zasu Bata kariyan da duk take buqata Dan haka yaji Inama gobe ne daurin auren…
Aurenta kadai zai Hana Omar amsarta daga hannunsa duk da Shima Koda Babu auren bazai taba basa ita ba sedai bayan ransa kuwa Dan haka yaji tsananin dadin Daya kasance auren ya raba musu gardaman yaqin da zasuyi akanta.
Mema ya dawo dashi bayan tsawon shekarun da sukai Basu San inda yake ba baisan inda suke ba kowa na tasa rayuwar?
Tayaya Ameenatou zatasan bashine asalin mahaifin Daya haifetaba?bama zata San wannan gaskiyar me rugusa farin cikinta ba a yanzu datake cikin tsananin farin cikin aurenta da Wanda take mutuwan so.
Tafiya yakeyi batareda ma yasan inda yake jefa kafafunsa ba sbd tinani da tashin hankali harma da tsananin bacin ran dayake Jin Yana tasowa Yana rufe dukkanin zuciyansa na bayyanar Omar gabansa.
Tafiya Mai Nisan gaske yayi batareda yasan yayi ba har Saida yaji kafafunsa suna Neman kasawa kafin ya tsaya Yana duba inda ya kawo kansa Bai saniba.,
Kafin ya sauke numfashin zafin zuciyar Dake cinsa lafiyayyar motan dake daukan idanuwansa ta tsaya gabansa Batareda an sauke glass ba Ahmed ya Bude motar ya fito ya Bude kofar Baya inda Omar yake zaune Yana kallan Babbahn Ahmed yace
“Bismillah”
Jajir idanuwan Babbah sukai Yana yiwa Omar wani kallo abinda ya danne shekara da shekaru Yana taso masa Mai tsananin zafi da radadin gaske harma ciwo me nauyi.,
Shima Omar Babbah din yake kallan gashi anguwar tsit Babu mutane sosai Kuma akwai duhu Dan haka Babu Wanda zaisan waye suka tsaya dauka.
Ahmed ne ya sake kallan babban Kai tsaye yace
“Ko zaa taimaka Maka ne gurin shigan??”
Maganar Ahmed ta Saka Babbah dagowa ya kallesa Jan idanuwansa na karuwa sbd yasan me Hakan ke nufi,
Ahmed shine Wanda ya kawo sakon yafe Ameenatou da Omar yayi tin tana kwana Daya da haihuwa a duniya Dan haka tsana da zafin Omar Dayake ji daidai yakejinsu akan Ahmed.
Shima Ahmed a nasa bangaren zuciyarsa a shirye take da duka dangin Omar dana matarsa sbd Bai yadda da kowa ba akan Omar hakama zai iya taka kowa Babu ruwansa akansa,
Idan rayuwar Omar sukeso to tabbas saisun shirya daukanta Dan ba sauki ya shirya musu.