AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE

*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#Arewabooks@Mamuhgee
#ZafafaBiyar

57
Ahankali Dad ya daga hannunsa da yayi masa wani irin mugun nauyi ya Dora a kirjinsa inda yaji wani abu ya tsaya masa Yana hanasa Jan numfashi kwata kwata kafin ma ya sake kokarin Jan numfashin ya yanke jiki a gurin Yana kokawa da numfashin Daya Yanke daga kirjinsa gabaki Daya idanuwansa na tsiyayo wasu zafafan hawayen masu radadi ahankali.

Mum Atee da Dad Lameenu ne suka durkushe gabansa suna ambatar sunansa cikin tsananin tashin hankali da rikicewa.

Dr zayyan ma cikin tashin hankalin me tsanani ya kira nurses da masu daukansa tini aka daukesa Akai ciki dashi Dr zayyan na cewa cikin sauri a kawo oxygen da gaggawa kafin numfashin nasa ya yanke.

Dadah kuwa da Karan farko Bata gane Abdul dinta ake nufi ba saida umman fadila ta rungumeta tana fashewa da kuka sbd dawo mata sabuwa da ranar rasuwar Taya ‘yar tayi a wannan asibitin itama ranar aurenta.

Dadah sai alokacin ta fahimci me ake nufi Dan haka ta silale qasa tana Neman numfashin itama sbd kukan ma mantawa tayi da ana yinsa a duniya iskan numfashi kawai take nema a kirjinta kafin ayi yunqurin Kiran likita ya some a gurin gaba Daya jikin umma.

Mum Nur dasu Aunt Didi kukan baqin cikin rasuwar Haroon din dana farin cikin mazajensu dake raye suka sake lokaci Daya tareda tausayinsu.
Fatmah ma kukan takeyi sbd ta dauka zaace Dad dinta da Dad Omar sun rasu suma sun barsu.

Mummy Sarat ma dasu Aliyah kuka sukeyi sosai musamman Ayeesha datafi kowa shakuwa dashi Kuma ita kadaice yakeda kauna mara sirki daga zuciya a tsakaninsa da ita duk cikin family Dan haka ta zube a gurin kasa tana fasa kukan Daya Saka gaba Daya gurin daukan shiru tana Kiran sunan Haroon din.

Emergency Akai gaggawan shigewa da Dad sbd oxygen din Neman gagararsa ja ma yakeyi Dan haka hankalin likitocin ya fara tashi Dan hak suka Taru akansa ana yaqin cetan numfashin nasa hankali tashe.

Su Lameenu Dake waje ma hankalinsu tashi yayi Dan haka kusan asibitin tayi tsit ba dogon motsi bare hayaniya sbd masu asibitin ne da kansu cikinta a mafi wahalan yanayi da tashin hankalin dasuke ganin Basu taba shigarsaba.

JAMAAL Babu Wanda yagansa har lokacin sbd Yana ciki inda gawar Haroon din take tareda ta Abdul a gefensa,
Gawar Haroon itace gawar datafi masa rayuwar duka Wanda yake duniyarma yake Gani,
Gawar Haroon itace abinda ya kasa dauke idanuwansa daka kansa,
Rabin jikinsa ya tafi yabarsa,
Haroon yasha wahala da baqin cikin rayuwa fiyeda komai,
Bai samu farin ciki ba tinda ya taso harya komawa ubangijinsa,
Yaso samun sauyin rayuwa a tareda Dan uwansa da mahaifiyarsa Dan matarsa bayan auren sedai Allah baiyi zaiga hakanba,

Meyasa suka kasance acikin zuria da jinin marasa imanin duk duniya da rashin tausayi?

Kasa riqe kansa yayi daidai lokacinda ya Tina maganar Dan uwan nasa ta karshe akan farin cikin dayake ciki a yau din sbd zai auri farin cikin rayuwarsa…..

Wani irin kuka Mai tsananin radadin zuciya ne ya fashe dashi Yana Dora goshinsa gefen kan gawar Haroon din duka jikinsa na rawa da jijjigan kukan da yakeyi Mai ciwo da baqin cikin ya rabu kenan da Dan uwansa shikenan.

“Innalillahi wainna ilaihirrajiun”

Kukansa ne sosai ya Saka siddeeq kasa riqe nasa kukan tausayin Haroon da irin rayuwar rashin kaunar da ake nuna masa Daya gudanar tareda wahalan ciwo Daya ringa fama dashi batareda kowa ya sani ba daga karshe ya tafiyarsa yabar duniyar da Babu komai a cikinta sai son zuciya da azaba a gurinsa.

Dadah da Akai gaggawan taimakawa tana farfadowa wani kuka Mai ratsa zuciyan duk uwar Datake da ‘yaya ne da uban dayake da yayane ta fasa tana Jin kirjinta Yana kasa daukan radadin Datake Jin kanta acikinsa,

Rashin ‘dan ta Babba tareda mummunan halinda mijinta yake ciki na tsakanin Rai ko mutuwa baa San wanne zai faru ba da Kuma Hafiz da Shima aketa kokarin ganin an ceta rayuwarsa sbd jininsa da kusan ya tsiyaye da kariyar datafi nawa a jikinsa.

Mum Nur ma da Aunt Didi lokacinda suka samu bayanin halinda su Dad Omar suke ciki mum Nur kasa dauka tayi dole Akai gaggawan mayar da ita gida tinda itama lafiyar tata sai ahankali,

Dadah tin tana iya kuka Dan idanuwanta har lamarin yaci karfina ta sake rikicewa jikinta ya rikice gaba Daya dole dai itama akai gaggawan Bata kulawa aka mayar da ita baccin dole da wahala sbd zuciyarta Dake Neman samun matsala sbd BP dinta yayi mummunan hawan daya fara Sakata kaman zatai jijjiga.

Daidai wannan lokacin ne Ameenatou ta farfado sedai umma kasa barinta tayi tasan meyake faruwa ta dawo gida da ita a taxi sedai Koda suka Isa gida gaba Daya gidan anyi cirko cirko kowa idanuwansa jajir masu kuka sunyi masu shiga tsananin damuwa da tashin hankali duk suna ciki Dan kuwa labarin wannan mummunan ranar ta ahalin SEELAHs ya isarwa kowa.

Duk yanda akaso taimakon Dad abin yaci tura sai da kyar suka samu damar daidaita numfashinsa sedai Kuma Bai San inda kansa yake ba Dan a cikin qanqanin lokaci Allah ya mayar dashi abin tausayi kaman Wanda yayi watanni a kwance take ya jeme.

Lameenu ma cikin tashin hankalin da jemewan yake sbd bazai taba son ya rasa Mam ba tinda a yanzu shi kadai ne yake dashi a rayuwarsa,
Idan ya rasa Mam bazai taba iya komai na rayuwarsa shi Daya ba Babu Dan uwan nasa,

Sun rasa sauran Yan uwansu Badan basa sonsu ba sai Dan son zuciya da shedan tareda muguwar zuciya datake rinjayarsu,
A yanzu tashin Mam da ganin lafiyansa shine abinda yake cikeda zuciyarsa ya Sanyaya jikinsa Dan haka gaba Daya ya koma Kalan jemewan Shima yana cikin tsaka me wuya.

*******Hudu bayan la’asar aka iso da gawar Haroon da Abdul mansion din Dad Omar sbd jamaal Daya Bada umarnin anan zaayi janazah dinsu wadda tini mutane masu yawan gaske suka fara halarta sbd daurin auren da sukai Niya tafiya shine ya koma janazah din Dan haka manyan mutane da Jamaa Tako ina.

Saida aka gama suturtasu siddeeq yaje gida ya dauko Ameenatou wadda take gida ta rikice musu gaba Daya Babbah da Yaya Abdul da Yaya Hafiz kawai take ambata sbd wayarta ce numbern da aka fara kira a wayar Babbah cewan sun samu mummunan accident wanda Dayan police din Kuma numbern Jamaal ya kira da wayar Dad Omar.

Zuwan siddeeq gidan ya tararda sauyawan lokaci Daya da Ameenatou din tayi sbd duk abinda yake jikinta na adon auren da Akai mata ta ciresa ko Dan kunne Bata bari ba daga ita sai doguwar Riga mara nauyi da mayafi ya fito ko gabanta Bata Gani Saida umma ta riqeta suka shiga motar datake jin kirjinta na sake toshewa tana Jan numfashi kaman me asthma.

Suna isowa har cikin harabar Mansion din gidan tana fitowa mota kafafunsa suka sare ta kasa daukan kanta sbd ganin tarin mutane Tako ina.

Umma da Aliyah data fito ne suka kamata har cikin palon farko na mansion din Wanda gawar biyu suke a shimfide fuskan Abdul an Riga anrufe ta Haroon ce ake kokarin rufewa ta iso gurin idanuwanta akan fuskan ta fara sauka kafin ta kyafta idanuwata suka sauka akan dadah Dake gaban dayar gawar zaune kaman mutum mutumi take numfashinta yayi sama Yana Neman fita daga kirjinta jikin tsananin tashin hankalin da Bata taba shiga ba da mummunan shock kafin suyi yunqurin tarota tafara kokawa da numfashinta Wanda yake kokarin ficewa…..

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected