VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Hindu Waallahi ina son mijina, mijina kuma yana so na amman yau komai ya kare”

Amma ta fashe da kuka.

“Har sai kin fada? Ai kowa ya san yadda kuke zaune ya san mijinki yana sonki kuma ke ma kina sonsa, sakin ma da zai miki Iyami na musamman yayi wane namiji ne zai saki mace ya dauki dukiya ya danka mata? Ai sai zababbu cikin mata, kuma ko yanzu karki yanke kauna In Shaa Allah zaki koma dakinki ki cigaba da addu’a nima kuma zan taya ki kuma ki saka ayi miki a islamiyayo nima kuma zan zaka ayi miki”

Kasa cewa komai Amma ta yi sai kuka take kukan da da zaka iya rantsewa mutuwa aka yi mata, idan ta tuna da sakinta Appan Hurriya yayi sai ta ji zuciyarta ta narke ta rasa me ke mata dadi a duniyar nan da ace mutuwa yayi sai ta dangana amman tunawa cewar yana raye kuma shi da kansa ya zabi rabuwa da ita ya fi komai daga mata hankali.

“Toh wai a can kika bar su Hurriya?”

“Ya ce zai rike su”

Ta amsa mata cikin kuka. Hindu bata wani dade a gidan ba ta mata sallama ta fita domin komawa nata gidam ta dora girki. Haka ta wuni a daki idan Gwaggo da jikokinta suka shigo sai ta boye fuskarta ta danne kukanta har sai idan ta kadaita ita kadai, tunanin yaranta ya tsaya mata a rai, tana ta auna lokacin dawowarsu makaranta da kuma irin abubuwan da suke idan sun dawo, da dare yayi sai ta kasa bacci domin wannan ne daren farko da zata kauna a gidansu tun bayan aurenta shekara goma sha shida. Ko biki ake a gidan ko wata hidima Appa baya barin ta kwana ko da kuwa ba girkinta. Daren sai ya zame mata wani dare na dabam da bacci ya gagara kusantar idonta ma balle har ya sace ta, kukan ma sai ta neme shi ta rasa wata zuciyar nata raya mata hanyoyin da zata bi ta shirya da mijinta sai ta saka zaren idan ta karshe sai ga ba hanya ce mai bullewa ba, dare ne da yayi mata tsawo fiye da sauran dararen da suka gabata, karfe biyu da rabi ta doro alwala ta fara raya daren da sallah nafila a haka aka kira sallah asuba akan idonta.

HURRIYA POV.

Da murna ta shigo dakin Appanta ta zauna kusa da shi a kasa kamar yadda ta saba, sai ya kai hannu ya shafa kanta zuwa bayanta yana murmushi irin murmushin nan dake dauke da so da kauna da kuma farincikin abun da idanuwa suka yi arba da su.

“Hurriya toh yaya?”

“Lafiya kalau Appa, ka dawo lafiya?”

“Lafiya Kalau, ina can gurin aiki zuciya na nan tare da ku sai tunaninku nake Ina Hamad”

“Shi ya ce ba zai zo ba?”

Ta amsa tana kai hannu ta gyara gilashin idonta. Hajiya Kaltume dake zaune kan carpet ta yi murmushi, irin murmushin nan da ya zame mata dole ne, domin ta kasa hadeye maganar da Appa yayi cewa yana gurin aiki zuciyarsa na gurin yayansa ta ce.

“Hamad ai ba zai zo ba, dazun ma dukanta yayi ya fasa mata gilashi sai da Yasir ya shiga tsakaninsu”

Appa ya kalli Hurriya cikin yanayin damuwa.

“Me ya hada ku?”

Ta zayyana masa abun da ya faru daga karshe ta rufe da fadar Yasir ya shirya su. Appa ya sauke ajiyar zuciya

“Ina ganin yaran nan za su koma gurin bangarenki sa zama Kaltume, saboda a rika saka musu ido, kar wata Hamad ya ji ma yarinyar ciwo, daman ko dan kula da abincin da wasu abubuwan dole su koma can”

“Gurina kuma Alhaji? Ni da nake da yan mata cike da daki? Kuma ka san yadda bama jituwa da uwar yarinyar nan yanzu nan Hurriya ko kaya ta taka na cire mata cewa za ayi na cutar da ita, ba zan hana ta zama ba idan haka kake so, amman dai da zaka barta a hannun Nafisa wata kila zamu samun zaman lafiya, daman Nafisa bata da yara da yawa uku ne kawai kuma mazan fita suke Namra ce kawai ka ga ta samu yar’uwa a kusa ko? Amman ni Hajiya ma sai tace na mata ba daidai ba domin ta kira ni tana ja min kunne akan yaran nan”

Ko kadan maganar da Hajiya Kaltume ta yi bata yi ma Appa dadi ba, sai yake jin kamar bata son zaman yaransa a gurinta ne, hakan kuma sai ya kara jefashi a cikin damuwar sakin mahaifiyarsu da yayi gashi nan ya koma nema musu gurin zama domin ba zai iya barinsu a katon part din uwarsu su biyu kawai ba babu mai kula da su.

“Hurriya yata ina kike son zama?”

Ya tambaya yana kallon fuskarta, Hurriya ta kalli Hajiya Kaltume sannan ta kalli mahaifinta ta ce.

“Gurin Hajiyarka ko Gwaggo”

“Ba zan iya bari ku zauna hannun kowa ba matukar ina raye, na fi sonku a kusa da ni na rika yaran wasu ma ta ina zan bada nawa riko? Idam har ba zan iya bari ku zauna gurin Iyami ba to ba zan iya hakurin ku zauna a gurin kowa ba, je ki kira Hamad”

Hurriya ta tashi ta fice, Hajiya Kaltume ta bita da kallo Appa kuma ya sauke ajiyar zuciya.

“Yaran nan sun zamar min kamar wasu marayu, Wallahi yau saboda tunanin abubuwan da suka faru na kasa sukuni”

“Akwai damuwa kam sosai, na da zaka hakura ka dawo da mahaifiyarsu da duk yafi wannan nema musu gurin zama da kake, idan ma wani laifin ta yi maka ka yafe mata dan Allah ko mu da muka kwana biyu aka saki a yanzu ai sai mun ji dabam balle kuma ita da take da sauran kurciyarta”

Appa be ce komai ba bayan sauke kai da yayi kasa, domin baya jin dawowa da ita mafita ne kamar yadda sakin ma ya kasa zame masa mafita domin ko yanzu jin yake kamar akan ƙaya yake saboda tunaninta domin yana matukar son matarsa ga kuma tunanin makomar yaranta. Hajiya Kaltume ta tsare mijinta da ido ganin ya noce kai kasa sai zuciyarta ta raya mata zai iya dawowa da ita kenan ganin yadda ya zurfafa a tunani ga kuma son yaranta da yake. Sai a lokacin da Hurriya ta dawo dakin tare da Hamad sannan Hajiya Kaltume ta kawar da kai tana kwafa a zuciyarta, Appa kuma ya dago ya kalli Yayansa. Hurriya ta zauna a inda ta zauna dazun Hamad kuma ya tsaya jikin kofa fuskarsa ba yabo ba fallasa.

“Hamad ka ci abinci?”

“Aa”

Ya amsawa Appa da kai. A take Alhaji Haruna ya kalli Hajiya Kaltume.

“Ba a basu abinci ba Kaltume?”

“Tuwo na girka, ka san Hamad ba ya cin ciwo kuma basa cin abinci da ake girkawa masu aiki”

“Idan shi baya ci ita Hurriya bata ci? Haba Kaltume kin san uwar yaran nan bata cikin gidan nan a matsayinki na babba ki kasa kiran yaran nan ki ba su abinci?”

“Ban yi tunanin ba su ci ba, ranka ya dade ayi hakuri ba za a koma ba In Shaa Allahu”

“Hurriya zaki ci tuwo?”

Hurriya ta daga kai a hankali daman tuwo is one of her favorite saboda abincin Appanta ne ita kuma duk abun da Appanta yake so tana sonshi, kuma yawan girka shi da Amma take ya saka ta saba da cinsa, domin Alhaji Haruna ba shi da wani abinci da ya fi tuwo duk arzikinsa ya fi son agirka masa tuwo a gidansa domin abun da ya saba da shi tun kamin zuwan arzikin.

“Zan ci tuwo Appa”

Ya kalli Hamad da ko a yau ko sannu da zuwa be masa ba kuma be gaishe ba, abun da be saba ba domin duk tsaurin kansa yana gaishe da Appa yana masa sannu da zuwa kamar yadda Amma ta koya masa.

“Kai kuma me kake son ci? Je ka kira Dahiru ko Bello ya kaika Restaurant ka siyo abun da kake so”

“Bana son komai”

Ya amsa kai tsaye ba tare da ya kalli kowa ba. Appa ya kalleshi da kyau.

“Hamad zo nan”

Ya shiga cikin dakin sai ya zauna nesa da Appa kamar wani bakonsa ko wanda be saba da shi ba, bayan kuma a da can ba haka yake masa ba idan yayi nesa da shi to yayi laifi ne, amman idan babu laifi baya zama nesa da mahaifinsa kuma sukan zauna su yi hira da juna ayi wasa da dariya sai dai ba kamar yadda suke yi da Hurriya ba.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected