Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Da far’a Hajiya Kaltume ta fadi haka tana kai hannu ta shafa bayan yarta irin na uwa mai alfahari. Sai a lokacin Khairy ta zabura ta tashi zaune ta kalli Hajiya Kaltume.
“Wane Fadeel kuma Hajiya?”
“Fadeel dai, dan wajen Hahiya Fatee yayanki”
Khairy ta lumshe ido ta bude alamar gajiyawa.
“Hajiya ina tunanin na nuna miki tun ranar da kika min maganar nan cewar Fadeel baya a cikin tsarina, namiji mai mata da yara uku me zan yi da shi?”
*I know littafin nan zai fito, i know zai yi yawo har ya iso gareki. Na fada kuma zan saki repeating Wallahi duk wanda ya karanta min littafi ba tare da ya biya ba, na barshi da mai mafaɗar rana da fitowarta. Daga masu sharing har masu karantawa ba tare da biya ba na barku da Allah…!*
Hajiya Kaltume ta juyo da kyau ta fuskance ta tana kokarin lurar da ita duniya.
“Irinsu ai sun fi rikon aure, balle kuma shi da muka san halinsa ciki da waje? Baki ga yadda yake zaune da matarsa ba? Sannan yayansa ai ba ke zaki rika su ba ko da ya rabu da matar, sannan yaron nan yana da kyau ga kudi, irin sa mata suke rubibi fa amman ke Allah ya kawo miki shi a arha”
“Ko duniya yake da ita, ni baya cikin tsarina bana sonsa, ina da wanda nake so… Saurayi matashi be taba aure ba kuma shi ma mai kudi ne dan masu kudi da baya jin zafin kashe naira”
Hajiya Kaltume ta yi murmushi.
“Yaro yaro ne, ke Khairy ban da yarinta irin naki, har akwai saurayin da zai fi Fadeel a garin nan? Ke dai ki bude idonki kuma ki ba zuciyarki hadin kai nan da nan zaki ji kina sonsa, kuma ki duba ko amincin dake tsakanina da mahaifiyarsa”
A karo na biyu Khairy ta runtse ido ta bude da karfi, cikin ihu ta ce.
“Hajiya bana son Fadeel kuma ba zan so shi ba, baya cikin mazanjen da nake so, ni ina da wanda nake so”
“Khairy lafiyarki kuwa? Ni kike yi ma magana da daga murya haka?”
“Toh Hajiya kina son cilasta ni auren wanda bana so, na fada miki bana ra’ayin Fadeel, ba a auren dole yanzu”
Rai a bace Hajiya Kaltume ta mike tsaye tana nuna Khairy da wayarta a hannu
“Baki isa ba, shi da yake namiji be bijirewa mahaifiyarsa ba balle ke da kike mace, kuma duk samarinki nan naki na banza ba, domin babu wanda ya nuna alamar da gaske yake har kika gama karatunki, kowa na ganki da shi sai ki ce abokinki ne, sai yanzu da na gabatar miki da wanda nake son ki aura mutumen kwarai wanda zai rike ki da gaske sai ki gabatar min da wata maganar banza, to baki isa ba dole ne ki bi zabina, ni na haife ki ba ke kika haife ni ba”
Fuuu Hajiya Kaltume ta fice daga dakin kamar walkiya rai a matukar bace. Khairy ta fashe da kuka gaba daya Hajiya tana son rikita mata lissafi bayan wanda Adam yayi mata. Kuka ta yi sosai sannan ta shiga bathroom dinta ta yi alwala ta fito ta gabatar da sallah Isha’i tana gamawa ta nufi jakarta ta bude ta dauko kwayar magani ta balla ta jefa a baki, sai da ta fara taunawa sannan ta kora da ruwan bandaki ta hade ta hau gado ta kwanta.
Some weeks Later….
Hurriya tana zaune rike da kofin ruwa tana kallon MBC 4 Namra ta fito zauna kusa da ita tana murmushi.
“Hurriya dan gidanki kullum sai yace na gaisheki, kuma ya ce yau zai shigo mu gaisa saboda an ki gayyatarsa gurin gatsar tsire”
Hurriya ta dago ta kalleta da alamar tunani domin bata gane wa take nufi ba.
“Dan gidana kuma?”
“Yeah Ethiopian…”
“Oh… Hmmmm Yaya Namra ashe yau akwai daukar wanka?”
Namra ta harareta hana dariya.
“What do you mean?”
“Yaya Namra na ga taku ta zo daya fa, all my life a yanzu babu wanda nake son ganin aurensa ko partner dinsa kamar ke da Yayana”
“Shi ke nan sai kuma aka ce miki wani abu ne tsakanina da shi?”
“Hmmmm ai yau idan ya zo fita zan yi na tsareku da ido har na gane komai”
“Okay ai tare zamu tafi, daman yace yau sai ya ga kanwata da nake ta masa rowa, but bari na fada miki Gaskiya babu komai tsakaninmu fa, gaisawa kawai muke shikenan”
“Hmmm Yaya Namra i can read your eyes fa, shi ma alamunsa suna nuna akwai abu a zuciyarsa fa”
Namra ta watsa ido da mamaki.
“Ke Hurriya yaushe kika zama haka? Wato ko kunyata baki ji kai tsaye kike fadar haka”
Hurriya ta saka dariya sosai, sannan ta matsa kusa da Namra.
“Yaya Namra maganar Allah mutumen be miki ba?”
Namra ta yi shiru tana murmushi.
“Yaya, amman ba abun da kike tunani ne ba”
“Zai zama abun da nake tunani soon Yaya Namra, daga ganinshi mutumen kirki ne dan Allah idan ya ce yana sonki karki ce aa”
Namra ta girgiza kai tana dariya ganin Hurriya ba zata barta da zancen ba, ta dauki filo ta rumgume.
“Kyaji da shi ke dai”
Hurriya ta yi murmushi. Haka Hurriya ta saka mata ido har yamma tana lure da yadda ta shirya turaren ma na musamman ta saka ta feshe jikinta ta ko’ina kamshi take. Ana gama Sallah Magariba before Isha’i Namra ta sauko tana sanye da wata Egyptian Abaya ko ina kyalli take gashi ta sha kamshi kamar wata amarya. Kusan wannan ne karon farko da wani ya ziyarci gidansu da sunan ganinta kuma shi ba dan makarantarsu ba kuma ba dan’uwanta ba. Har ta fita sai kuma ta dawo ta shiga dakin Hurriya dake kwance tana karatun Qur’ane.
“Hurriya ta so mu je”
Hurriya ta juyo ta kalleta.
“Ya zo”
Namra ta daga mata kai tana murmushi fuskarta har annuri take. Hurriya ta aje kur’anen ta dauko ta nufi Hijab dinta ta dauka ta saka.
“Amman Yaya Namra ki fadawa Momy? Kar ta fito nemanki ko nemana ba mu kusa”
“Ban fada mata ba, dadina dake akwai zurfin tunani, bari na fada mata sai na sameki kasa”
“Okay”
Ta juya ta fita daga dakin ta nufi dakin Momy, daga bakin kofar dakin ta tsaya ta fada mata tana da bako a waje zata je su gaisa, a take Momy ta yanke wayar da take fuskarta ta cika da annuri.
“Maa Shaa Allah, haka nake son ji a gaishe shi”
Ta yi murmushi ta yi baya ta ja mata kofar, kasa ta sauko ta samu Hurriya tsaye tana jiranta. Hannunta ta kama suka fita tare. Sai da Namra ta yi ta rabon ido kamin ta hango shi tsaye can gurin gate din gidan.
“Laa har can ya faka?”
Hurriya ta fada tana ganin kamar ya tsananta ma kansa fakawa a nesa da apartment din Momy. Tun kamin su karaso ya bude motar ya fito, farar shadda ce a jikinsa da hula shi ma sai kamshi yake zubawa irin na manyan samarin nan dake gasar nuna ado a gurin yan matansu. Haka nan Namra ta samu kanta da kunyar kallonsa har suka karasa gurin.
“Salam”
“Salam…”
Ya amsa musu yana kallon Hurriya da murmushi a fuskarsa.
“finally yau dai an fito min da kanwar nan da ake ta min rowa”
Namra da Hurriya suka yi dariya kusan lokaci daya.
“Ba rowarta nake maka ba, kai ne baka bukaci gaisawa da ita ba”
“To ai tsoro nake ji, kar ki ce min na karya doka kuma kin san mai nema taka tsantsan yake”
“Haka ne”
Hurriya ta kalleshi ta ce.
“Barka da dare”
“Hey Young Lady”
“Lafiya Kalau”
“Maa Shaa Allah, yau dai na ce zan zo na dubaki, even though dai aiki yana min yawa amman Yayanki tana min rowarki kullum idan ina cewa ina gaisheki bata ce min kina amsawa sai dai tace min zaki ji kina ji kuwa”
Hurriya ta yi dariya tana kallon Namra dake girgiza kai tana murmushi kawai yadda yake da son ban dariya abun yana burgeta.
“Tana fada min, kuma ina amsawa”
“Good”
Ya fada still yana kallonta. Namra ta kalleshi kadan ta ce
“Ka shigo ciki”
“No nan ma ya isa, kawai dai ki kawo min kujera na zauna”
Hurriya ta wara hannunta