VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Allah ma ya tsareka da hada alaka da wacan yarinyar”

Daga Salim har Captain kallon Momy suka yi sai dai babu wanda ya ce komai. Momy ce ta fara mikewa tsaye.

“Bari mu baku guri ku ci abinci”

Namra ta bi bayanta suka haura sama, haka Salim ya bi abincin da aka jera musu ga kuma plate din plantain da Captain ya saka hannu ya dauki daya.

“Ni zan tafi Captain, bana jin zan iya cin komai kuma sai da na ci abinci sannan na fito, ya kamata na tafi”

Ya mike tsaye tare da kallon ledodin dake gefen kujerar da suka zauna.

“Ka shigar mata da wannan”

Captain ya dan motsa baki irin na wanda ya rasa abin cewa, ya bi Captain da kallo kamin ta mike tsaye ya bi bayansa.

HURRIYA POV.

Kofar windows dakinta ta tsaya tana kallon kasa, har lokacin gabanta be daina faduwa ba arba da ta yi da Salim da kuma mutumen da har yanzu bata san sunansa ba.
Each seconds sai ta juya ta kalli kofar dakinta tana jiran ta ji ko za a kwankwaso mata ace ta fito, gashi idan Momy ce ba ta isa ta ki fitowarba, hankalinta be kwanta ba sai da ta hango fitowar Salim, ta yi baya baya kadan daga windows din gudun kar ya ganta, sai kuma ta ga mutumen da yake tare da shi a dazun ma ya fito. Da sauri ta bar jikin window din ta cire dankwalin kanta ta jefar a gado ta bude kofar ta sauka kasa ita a nufinta ta samu abun da zata sakawa cikinta kamin ta su dawo ko kuma a cilasta mata fitowa a dakin da take da niyar shiga ta rufe kanta. Ganin babu kowa falon ya saka ta taka a hankali ta leka Kitchen nan ma babu kowa, ta dawo dinning har ta fara bude warmers sai kuma wata zuciyar ta raya mata cewar za a iya ganewa ita ta ci abincin ganin ba a taba shi ba, a take ta rufe ta dauki plate daya ta nufi abincin da aka jerawa baki ta zuba white rice ce da ta ji green beans da carrots sai pepper soup din hanta da aka yanka kanana kuma aka saka kaza sai kamshi take, ga plantain da aka soya. Komai sai da ta zuna, Jin kamar motsi a sama wato stairs ya saka ta dauke plate din tana kallon stairs din ta watsa da gudu kitchen ta rufo kofar.

Ta aje plate din a tana auna abincin da hannu biyu, idan ta ci da dama sai ta ci da haka bata ma tsayawa ta tauna burinta kawai ya kai ga cikinta kamin asirinta ya tsonu. Wani irin kuka ne ya tunkaro da ya fi karfin duk wani kokari nata na son hana kanta kukan saboda tausayin kanta, a take ta fashe da kukan marar sauti hawaye shar kamar magudanar ruwa. Kamar daga sama ta ji an bude kofar kitchen din tana kallon kofar suka yi ido hudu da Captain da shigo a zatonsa Momy ko Namra ce a ciki saboda ya ji karar rufe kofar a daidai lokacin da ya dawo falon.

Baya baya ta yi shimkafa a duka hannayenta guda biyu ga kuma bakinta ma cike da wata shimkafar ga fuskarta da ruwan hawaye suka yi mata ado, ka a ganinta ka san a firgice take. Be plate din da be gama zaunawa ba ne ya fado kasa saboda jikinta ya tana plate din kadan a lokacin da take yin baya baya, a take plate din ya fado ya fashe a kasa..

“Waye a kitchen waya fasa plate….?”

Namra dake saukowa ta tambaya domin ta ji karar faduwar plate din na Momy mai tsada. Hurriya ta dauke numfashi da mugun karfi saboda tsoro. Captain yayi baya kadan ya leka falon ya amsawa Namra.

“Ni na fasa”

“Subhanallahi Allah yasa baka ji ciwo ba?”

Ta sauko da sauri, sai amsa kamar yadda ya saba amsawa mutane magana wani lokacin da bakar magana musamman idan baya son a shigar masa sabga.

“Na ji ciwo kin san ai yaro ne ni…”

Tana jin haka bata karasa gurin ba, sai kawai ta yi murmushi tana masa wani kallo har lumshe ido take.

“Allah ya baka hakuri”

Ta juya ta fara hawa sama domin sanar da Momy abokinsa ya tafi Captain ne kawai. Sai da ta haye sama sannan ya juyo ya kalli Hurriya a take ta hade sai ta zubar da shimkafar a kasa ta hade hannayenta biyu waje daya ta daga su tana masa godiya tana kukan da ba shi da sauti sai hawaye. Kamin ta duka zata fara kwashe breaking plate din.

“Zo ki wuce”

Ya fada yana matsa daga jikin kofar ta yadda zata samu hanya. Ta dago ta kalleshi ta girgiza kai

“Idan Momy ta gan ni a kitchen dinta sai ta kusa kasheni tace kar na sake shiga”

Tana fadar haka ta mike tsaye ta nufi kofar baya ta bude ta fice. Juyawa yayi ya fice daga kitchen din kai tsaye ya nufi stairs ta nufi dakin Momy direct, yana dora hannunsa a jikin kofar zai murda kunnuwansa suka jiyo masa wani sauti na Momy da Namra yana fita.

“Wani sabon iskanci ya taso mata ba? Ai Wallahi sai na hanata numfashi a idan nan, saboda tana ganin tana da kyau dole maza su fara binta ganin take yi tana daidai da ni yanzu”

“Daman laifin na waye ne Namra ba naki ba, ki rika jan yarinya a jiki matsayinku ma ba daya ba, uba kawai kuka hada balle kuma yanzu da take munafurci, gashi har ta samu bakin fada miki magana, da yaran Kaltume me da yanzu ba su sumar da ita ba, shiyasa ai bata yarda ta zauna a bangaren Kaltume ta shan wuyar da take sha a hannunsu”

Cewar Momy tana mikewa tsaye. Namra ta ce

“Ko a nan sai na zahira ya fita jindadi, ai na riga da na gane halinta a yanzu”

Slowly Captain ya dauke hannunsa a kofar ya juya ta fara sauka ba dan ya gama jin komai ba, sai dan baya bukatar jin wasu abubuwa da yawa a yanzu, daman he just want to talk to her akan Hurriya ya ji ko laifi ta yi Momy take mata hukunci da wannan. Be karasa sauka ba Momy ta bude kofar dakinta ta fara saukowa Namra na bayanta.

“Captain…”

Ta kira sunansa da mamaki ganin ya rage few steps ya sauka. Sai ya juyo ya kalleta.

“Haurowa ka yi? Wani abun kake bukata ne?”

“No da zan shigo ne sai kuma na ce bari dai na tafi kawai”

“Sorry Namra ta fada min kana falo ban fito da wuri ba, abokin naka ya tafi?”

“Yea ya tafi”

Ya sauka ya tsaya a daidai inda suka zauna dazun tare da Salim, Momy ma ta sauko tana fadin.

“Ai da ma zaka ba shi shawara ya fita safgar yarinyar nan, wani rashin mutunci ne take ji yanzu, ko da yake ni ban ki ta samu miji an mata aure ta bar bangaren nan ba”

Kamin Captain yace wani daman kuma ba shi da niyar fadar wani abu akan maganar. Hurriya ta turo kofa ta shigo falonta ta kofar da ake shigowa, bayan ta bata lokaci a Garden ta wanke hannunta a fanfo da fuskarta. Gaba dayansu dubansu ya koma kanta, tana isowa tsakiyar falon ta kalli Momy sai kuma ta yi saurin kauke kai kasa ta nufi hanyar stairs.

“Ke zo ki dauki abincin nan idan zaki ci”

Captain ya fada in a game way, yana binta da kallo, ita ma juyowa ta yi ta kalleshi kamin ta kalli Momy dake kallonta.

“Zo ki dauka mana”

Ya saka fada ganin tana jiran umarnin Momy, Namra ta yi karaf ta ce.

“Domin ku fa aka yi?”

“To ai shi ya tafi be ci ba, kuma ni ma a koshe nake maybe next time”

Hurriya na jin haka ta dawo ta duka a gurin ta dauki plate ta zuba rice din sai karamin bowl ta zuba miyar sai da tsame rabin naman kazar dake ciki miyar sannan ta dauki cup ta zuba fresh apple juice da Namra ta hada ta dauki wani plate din ta zuba plantain duk abun da ta zuba wanda ta san zai isheta ne har anjima, sannan ta dauka ta mike tsaye.

“Na gode”

Ta furta with sweet voice dinta tana musa laɓɓanta masu kyau. Sannan ta nufi stairs sai da ta kusa haye sannan ta juyo ta kalleshi ta juya ta cigaba da tafiyarta.

 

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar  MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne  cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai  shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected