VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Idan umarni ne Hajiya zan bi idan kuma shawara ce zan duba”

“Shawara ce, Iyami ma da take kyautata min nake kaunarta cilasta maka maida ita ba balle Kaltume da ba dan darajar Yayanta ba da ko kallonta ba zan yi ba, babu kalar cin mutuncin da bata yi min ba, amman shi babba ba ya zama kamar yaro kuma abun da duk ka aikata mai kyau ko marar kyau zaka girbe shi a kusa ko a nesa, wannan fadin Allah ne”

“Haka ne, Kuskuren kuma daga ni ne Hajiya ban tsaya na duba background din ba kamin na dauko, kaddara ta riga fata”

“Wannan ma zai wuce tsoho, ka kyautata zamanka da Iyalinka gwargwadon yadda zaka iya, kuma ka kwatanta adalci a tsakanin ƴaƴanka ita soyayya an sani Allah yake sakata, amman sai mutum ya bar abun a zuciyarsa ba sai ya bayyana ba domin bayyana ko nuna fifiko akan wani shi ke bude kofar abubuwa da yawa da baka yi tsammani ba”

“In Shaa Allahu Hajiya”

“Allah yayi taimako ya hada kan Iyalinka”

“Amin”

Ya amsa sannan suka yi sallama ya sauke wayar ya kalli ragowar furar da Sapna ta daka masa da kanta ta aiko masa bayan dawowar daga kasar Maradum. A yanzu jin kansa yake a free kamar wanda ya fito daga wani kangi ya samu yanci haka yake jin a ransa, nishadinsa na da yadda tsarin rayuwarsa na baya a yanzu jinsa yake a normal a yadda ya saba yi.
A yanzu din ne yake jin marmarin abokiyar rayuwarsa fiye da koyaushe be taba bakincikin rabuwa da ita ba sai a yan kwanakin nan gaba daya ta shige masa a rai wani sabon kaunar Amma yake ji a ransa, be tabbatar da ya tabka babban kuskure na sakinta ba tare da ta yi masa laifi ba sai a yanzu bata kusa da shi, gashi idan ya tuna da yaransa Hamad Hurriya da yan biyun da ta haifa masa sai ya ji tausayinta ya kara kama shi.

Lokuta da dama ya kan nutsa a duniyar tunanin dalilin sakin nata sai ya rasa, gaba rayuwar baya ta zame masa kamar mafarki yayi wasu abubuwan da yayi ma Amma da Hurriya da kuma iyayenta idan ta tuna sai ya ji babu dadi, kuma ya rasa dalilin haka, kamar yadda a yanzu ma ya rasa dalilin tsanar da yayi ma Hajiya Kaltume, macen a da ko tari ta yi jikinsa rawa yake ya amsa mata, a yau ita ce yake jin baya bukatar zamanta a gidansa ita ce a yau yake fatan ta gama zaman idda ta bar masa gidansa, a yau ita ce macen da baya son kallon bangarenta idan zai fita.
Zancen da Hajiya Binta ta yi masa cewar mata ne suka dace da siyayyar kayan dakin Hurriya ya saka shi kiran Number Amma, kamar wani yaro haka ya aje wayar a gabansa ya dauke hannayensa yana kallon number tare da fatan Amma ta daga kiran amman bata daga ba har kiran ya katse, ya sake gwada kiran a karo na biyu sai kuwa ta dauka hannunsa ya kai ya taba speaker dake jikin wayar, sallamarta kadai nishadi take kasa shi tana tuna masa da rayuwarsa da suka yi a baya.

“Wa’alaikissalam…Hajiya an wuni lafiya?”

“Alhamdulillahi”

“Maa Shaa Allah, Ina yarana duka suna lafiya”

“Lafiya kalau”

Ta amsa a takaice domin bata son wata maganar da ta wuce sha’anin yara ko gaisuwa ya wuce tsakaninsu. Shiru ya dan yi na lokaci kamin ya ce.

“Yanzu na gama magana da Hajiya nake fada mata yadda muka yi da ke na siyayyar wasu abubuwan na Hurriya, nake fada mata ina son siyayyar kayan dakinta da kaina kamar yadda nake yi ma sauran Yaya Sapna da Maama, wai take cewa su ma siyen kayan daki ai na uwa ne, iyaye mata ya kamata su yi”

“Haka ne”

“Shi ne na ce idan babu damuwa sai ki shirya tare da mutanenki mu tafi Kano a duba mata kaya masu kyau wadanda hankalinku ya kwanta da su, da ice ita din babu lalura a tare da ita da sai mu tafi tare da ita ta zaba da kanta kamar yadda sauran yan’uwanta suka yi”

“Already mun yi order kayan Kitchen gurin Khadeeja Candy, zata saka a kawo mana daga Kano har gida, kuma wasu abubuwan Gwaggo zata tafi tare da Hindu Lagos su siyo”

(Duk mai bukatar kayan kitchen, Bedsheets da kayan kawata falo ko daya, akwaituna da kayan lefe kamar su laces shadda atamfa materials da Shoes and bag, sarka yan’kunne turareka zai samu a gurin Khadeeja Candy Store cikin sauki da rahusa, muna aikawa ko’ina a fadin Nigeria da sakashen dake makota da mu kamar irin su Nijar Togo da Ghana cikin aminci da yardar Allah, mai bukata sai ya tuntube ni a business line dina kamar haka :- 080361266660)

Appa ya sauke ajiyar zuciya jin kamar Amma bata fahimci inda ya dosa ba ya ce.

“Kayan daki nake magana kamar gado da kujeru da sauran abubuwa na cin abinci, gidansa da ke Kaduna za a iya siya a Kd a saka a can ko kuma a siya daga Kano a kai can, da son samu ne ma a siyo mata komai a waje na fi aminta da kayan can fiyeda na cikin gida”

“A Kanon ma babu kalar kayan da babu, suna dauko kayan waje domin saukakawa masu gaggauwa ba sai an kashe kudin jirgi ba wata order ma sai ka yi bata iso da wuri ba, zaka iya zuwa Kano ka duba mata”

“Da zamu tafi tare ai da zai fi domin ke ce idonta a yanzu, kuma duk yadda zan yi zabe ba zai kai ga ke yadda zaki zaba ba”

“Babu wata hujja da zata saka na shirya baka tafiya da kao Alhaji ko dai ka manta ni din nan ba matarka ba ce?”

“Ba daga ni sai ke nake nufin tafiyar ba tare da familynki, shiyasa zan baki dama ki yi shawara da su daga nan zuwa gobe abun da kika yanke sai ki fada min”

“To shi ke nan mu kwana lafiya”

Yayi saurin dakatar ta ita daga kokarin yanke wayar da take.

“Idan ba zaki tsaya mu gaisa ba, toh ina yarana Hassan da Husaini?”

“Sun tafi Islamiya”

“Hurriya fa bata kusa?”

“Rukayya karbi mikawa Hurriya waya”

Amma ta cire wayar a kunnenta ta mikawa Rukayya da ta mike tsaye ta nufo gurin da suke zaune ta karbi wayar ta fice daga dakin zuwa dakin Bappa da Hurriya ta shiga dazun tana ganawa da kakanta.

“Ka ji min wata magana wai Hajiya Binta dake Saudi gurin Ummara ta ce masa zaben kayan daki na mace ne”

Baaba Uwani wadda ta kasance kanwa ga Gwaggo ta bude hannayenta jin an sosa mata gurin dake mata kaikayi.

“Daman ai na fada, dama nan ya bar zabin komai zai fi, domin dai zaben Kaltume ko wannan Hajiya Nafisa ba za su zabo ma Hurriya abun kwarai ba”

“Daman ni ban saka ran da Kaltume za a je ba, domin babu aure yanzu tsakaninsu, Nafisa nake saka ran zata taimaka masa gurin zaben kayan ita na san ba zata zabo abun kirki ba domin ba son Hurriya take ba kuma tun da aka daura auren nan har yau bata tako gidan nan ba”

Hindu dake bude giɗa ta ce

“Da gaske wai bata zo ba?”

Amma ta waiga ta kalli kawar da za’a iya cewa yanzu ta zama yar’uwarta ta ce.

“Wallahi bata tako ba, kuma kin ga ko cikin danginsa da suka zo bata biyo su ta zo ba kuma bata zo ita kadai ba Namra ma bata da tako nan ba”

“Allah da iko yake, da alama ma fa ita ma bata son auren nan, ke bi ba dan na ga yaron ba tubarkalla Maa Shaa Allah da shi da zan iya cewa aura mata shi aka yi saboda sun ga ba mutunen kwarai ba ne, ina fatan dai an bincike halinsa ba shi da wani nakassu”

Ta karasa zancen tana jefa giɗa abakinta. Amma ta ɗan taɓe baki.

“Bashi da shi gaskiya domin shekaran jiya kamiN Hajiya Binta ta wuce Ummara ta zo gidan nan yi mana bankwana take fada mana Appan Hurriya yayi saka an masa bincike a akan yaron ta hallayarsa ta zamankewa da mutane kuma ba su ji wani aibu ba, Allah ne fa ya wanke Hurriya kuma yayi mata sakamako da wannan, ki duba ko video nan na Khairy yanzu da ya cika gari Appanta yace shi ne ya shiga ya fita ya ga komai ya warware, an goge hotunan Hurriya ta inda zai iya kuma ya saka suka bata hakuri, kuma shi ya cilastawa yaron fadar gaskiyar abun da ya faru, kina jin yadda aka daura auren nan da sadakin kin san abu ne kawai min indin Allahi, karki so ki ga yadda ya zo gidan nan, baya ma iya daga ido ya kalleni, son kakarsa ma ta zo ita da abokiyar zamanta da kanen mahaifinsa su biyu da yayar mahaifiyarsa dukansu kuma ban ga wani abu a tare da su ba, idan ba dayar ba dake ta hankada tana harare-harare”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected