Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Wani abun ma sai nan gaba”
Suka bushe da dariya, Hajiya Fatee ta mike tsaye ta dauki hijab dinta ta saka.
“Bari na tafi kar na batawa Fadeel lokaci aiki zai je na ce ya kawo ni na ganki ya maida ni direba na yayi tafiya”
Hajiya Kaltume ta mike tsaye ta yi mata rakiya suka sauko kasa suna hirar, bacin rai dake zuciyar Hajiya Kaltume tuni ya yaye saboda kawarta ta karafafa mata guiwa kuma ta kwantar mata da hankali. Ganin Khairy zaune a falon ya ba wa Hajiiya Fatee mamaki
“Ah… Na yi zaton kina waje? Tare da Fadeel muke fa”
“Na sani bana jindadi ne shiyasa”
Ta amsa a kasalance tana sauke ido kasa kamar munafuka. Hajiya Kaltume ta ce.
“Wai ke kam me yake damunki? Tun jiya kike wani laude laude kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki”
Sai Hajiya Fatee ta daga hannu tana fadin.
“Wata kila abun yar’uwar ne ya shafeta kin san abun da ya taba gira shi ya kai ga ido har ya taba hanci, idan abun da ta yi karki saka kanki a damuwa kwana nawa ya rage miki ki har gidan ma, kuma wannan ai abun farinciki a gurinku, kowa be lalace ba sai Hurriya na tabbatar da Iyami tana lafiya ace wani ne a cikin yaran Hajiya Kaltume yayi haka farinciki zata yi ”
“Kwarai kuwa shiyasa ni ma bana fatan alheri ya same ta sai sheri”
Hajiya Fatee ta wuce gaba suka jera da Kaltume har wajen gidan, kamin Fadeel ya juya motarsa suka nufi karamin gate din gidan na bangaren Hajiya Kaltume. Daga inda suke tsaye suka hango shigowar manyan motocin na alfarma har hudu cikin gidan, duka motocin aka nufi bangaren Momy da su.
“To baki kuka yi kuma?”
“Ta yi dai ita yar karyar arziki, ita din ma ba barinta zan yi ba Wallahi”
“Aifa ki bari aikin Malam ya fara kawai sai wanda kika so zai zauna a gidan nan, ni na manta ban fada miki ba Afrah fa tana gidansu yaran suna gidana shi kanshi jiya gida ya kwana”
Hajiya Kaltume ta rike baki.
“Ki ce Allah”
“Ba kina wasa da lamarin Malam ba? Hmmmm”
Hajiya Kaltume ta jinjina kai tana kara ganin girman Malamin da kwarewar aikinsa, Afrah da ta gagari Hajiya Fatee yau ace Fadeel ya kora Afrah gida. Babu halin yin wata doguwar magana saboda Fadeel ya faka mota a gabansu ya budewa mahaifiyarsa.
“Hajiya Fatee zamu yi waya”
Hajiya Fatee bata sake furta wani abu ba saboda Fadeel yana gurin sai dai ta yi murmushi mai sauti ta shiga motar, Fadeel ya ja bayan yayi ma surukarsa to be sallama.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
Da tunani kala kala Momy ta sauko falon Namra na bayanta.
“Yaya yau kai ne a cikin gidana?”
Daddy dake zaune akan kujera tare da sauran yan’uwansa yayye da kanne yayi murmushi.
“Nafisa mamakin zuwana kike ne?”
“Kwarai kuwa, Yaya tun da aka kawo ni gidan nan sau daya ka taba zuwa gidan nan fa, da Hajiya Turai ce ba zan yi mamaki ba, amman ganinka ya saka ni a fargaba Allah yasa ba Captain ya ce na yi masa wani abu ba?”
Alhaji Munzali yayi dariya, Daddy ma dariyar yayi ya ce.
“Saboda ba ni da kunya zai na taso na kawo miki takakka har gida?”
Ta yi dariya.
“Namra duk a firgicce take ita ma ta dauka Captain ya turoka, saboda jiya ya zo nan yana neman a kai shi gidansu Hurriya na hana Namra, wata kila hakan ya fusata shi ya kai karata a gurinka”
“Hakan da kika yi ai kin yi daidai, Ammy sa ma ta yi masa magana be so ma amman daga karshe dai ya fahimta kuma yace ya hakura”
Momy ta zaro ido tana dukan kirjinta.
“Ya hakura yaya? Amman ya kyautawa kansa daman can yarinyar bata dace da shi ba Wallahi, ni daman na san Hajiya Turai ba zata yarda danta ya auri yarinyar nan ba”
Daddy ya gyara babbar rigarsa yana kallon Namra dake jera musu abun karyawa.
“So jiya mun yi magana da Captain saboda ya shigar da kara DSS yanzu kuma yana son ya janye karar ne a hannata komai a gurin mahaifinta, ni kuma yau zan koma Kaduna, shiyasa na zo yanzu na san be isa fita ba ina son na yi magana da shi mu kai karshe”
“Hakan yayi, ban da Abin Captain na son wahalar da kai miye na wani shigar da kara, yarinyar nan fa makauniya ce ma idon za su bude ba za su bude ba Allah masani amman ya tsoma kansa a damuwarta har da ikirarin aurenta kamar wanda baya cikin hayyacinsa”
“Wannan maganar kuma ina tunanin ta wuce Nafisa, ki sallamawa mai gidanki zan yi magana da shi”
“Toh Yaya”
Ta tashi jikina na rawa ta nufi bangaren Appa, a nan Daddy ya samu gaisawa da Namra yana tambayarta ya karatu.
“Ai na kare, next week zan tafi service Kaduna In Sha Allah”
“Abu yayi kyau, muna da bakuwa kenan”
Daddy ya fada sai ta yi murmushi tana jin farinciki jin cewar Captain ya hakura da auren Hurriya. Kamar yayan mahaifiyarta Alhaji Munzali ya san dalilin farincikinta sai ya bijiro mata da makamanciyar maganar.
“Aure fa Namra?”
Ta yi shiru ta noce kai kasa, Daddy yayi murmushi ya amsawa Alhaji Munzali yana kare yarsa.
“Za’ayi a daga mana kafa mana Alhaji, komai ai lokaci ne za ayi babu jimawa In Shaa Allah”
Yanayin yadda Daddy ya bada amsar sai ta ji kamar yana mata inkiya da auren Captain ne, hakan ya kara fadada farincikinta.
“Alhaji Rufa’i ku taba wani abu mana, kamin nan da wasu shekaru Nafisa ta mana gorin mun shago gidanta ba mu ci komai ba, kasan Nafisa akwai rike abu ga iya gori”
Sai duk suka saka dariya har Daddy da yayi maganar. Daddy ya dauki ruwa ya sha ya ci yankan cake daya sauran kuma kowa ya ci abun da yake sha’awa even though ba san da zuwansu ba abun da yake gidan na tabawa ne Namra ta kawo. Appa ne ya shigo dakin yana sanye da Babbar riga irin ta Malam Bahaushe sky blue shaddar dake jikinsa har wani kara take tsabar sabun taka, be zauna ba sai da ya mikawa Alhaji Aliyu Turaki hannu biyu suka gaisa yana masa maraba da zuwa.
“Yau Yaya da kansa a gidanmu”
“To kai ma gorin zaka min kenan, daman ance idan zama yayi dadi miji yana daukar dabi’un mata, mata ma tana daukar dabi’un miji”
Momy ta yi dariya tana zaunawa, Appa ma dariyar yayi ya mikawa sauran hannu suka gaisa, sannan ya zauna.
“Toh Allah yasa ba laifi muka yi ba”
Appa ya fada, sai Daddy ya kalli Alhaji Sadiq ya ce.
“Ka gani ko? Ita ma haka ta ce mana”
Sai duk suka saka dariya har Namra, sai suka natsu sannan Daddy ya kalli Namra da Momy ya ce.