VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Na gode Appa”

“Ba zata zauna a bangarena ba”

Momy ta fada cikin zafin rai da daga murya. Appa ya watsa mata harara.

“To sai ki hada komai na ki ki bar mata bangaren, domin duk wanda ke gidan nan yana karkashin iko na ne”

Hurriya ta mike tsaye tana share hawayenta ta fice daga bangaren tana jin kamar an watsa mata ruwan kankara a kunar da zuciyarta take mata.

_____________________

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…

*HURIYYA*

 

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660

@

1️⃣5️⃣

“Sam Sam Sam ni hukuncin da Alhaji yayi a gidan nan be yi min ba”

Cewar Hajiya Kaltume da shigowarta falonta kenan. Khairi ta yi karaf ta ce.

“Ba ke kadai ba Hajiya, ni Wallahi na dauka ma korar Hurriya zai yi, domin zata iya satar kudin nan”

Hajiya Kaltume ta zauna tana fadin.

“Ai ba nata ne ya ban mamaki ba, na Nafisa ne, yadda ta ci mutunci na ta dora min sata ban ji ba ban gani ba, amman ace Alhaji ya kyaleta ba tare da yi mata wani hukunci ba? Ni wane irin rashin godiyar Allah ne zai saka ni sata a bangarenta, ni ban ma san ta fita bangaren ba, amman da yake ta raina ni haka ta laka min sata, saboda bata da ta ido har da wani aiko masu aiki wai su zo duba mata bangarena, haka fa matar ta taba dora min laifin fasa tayar bakinta, ta maida ni kamar wata karamar yarinya”

“Wallahi Hajiya abun da Momy take yi a gidan yana wuce gona da iri, da zarar an taba ta sai tace ita mai kudi ce, mu gaba daya ganinmu take kamar wasu awaki ita kadai ce mutum”

Hajiya ta kara kashe ido domin laka mata sata da Momy ta yi da kuma kyalewar da Appa yayi be yi komai ba ya fi komai bakanta mata rai.

“To wai waye zan tura ya shiga ya dauki kudin a bangarenta, idan ma ba wanda yake bangaren ba waye zai san gurin da take aje kudinta, da sarka har a dauka, ko dai masu aikinta ko kuma ita wannan mai siffar macizan ce”

“Ni fa zuciyata ta fi yarda ma ita ce, amman kin ga yadda ta wani sha jinin jikinta sai kuka take ita munafuka, har Appa ya tausaya mata, wannan yarinyar da film take da ta kwashi kudi dominbta iya acting”

“Bar shi ai sai na masa magana akan haka, dan yau yaushe za a shaideshi ne, har da wani cewa wai duk abun da yake mata ba sonta ne ba shi ba, kin ji min wata maganar banza”

Sai da Khairi ta kalli kofa domin tabbatar da babu wanda zai shigo sannan ta kalli Hajiya Kaltume ta ce.

“Ya Yasir ma da wani ne sai yayi masa dukan mutuwa kamin ma a gane gaskiya, amman kin ga da yake Hurriya ce uffan be ce ba, balle har ta kai ga ya doketa, ai Wallahi Salma ta huta da tafi yin masters dinta a waje, Maama kuma ta yi aure babu mai shan wahakarsa sai ni, daman ni ya tsaneni a gidan nan”

Hajiya Kaltume ta daga mata hannu.

“Ni yanzu ba ta Yasir nake ba, maganar nan ba zan bari ta wuce ba, ba a dora min sata da kurciyata ba yanzu da yayana ba za a dora min sata na kyale ba, kuma Wallahi sai na bawa Nafisa mamaki sai na maidata abar tausayi”

Khairy ta dan kalli wayarta da sakwannin ke appearing saman screen din wayarta, ta dan bata fuska kadan da alamar damuwa sannan ta fara taba wayar tana reply kaminnta mike tsaye ta nufi dakinta. Hajiya Kaltume kamar tashinta take jira sai ta tashi ita ma ya nufi nata dakin ta dauki wayarta ta kira aminiyarta da bata iya boyewa komai, sai dai ga mamakinta sai da wayar ta yanke har sau biyu ana uku Hajiya Fatee ta amsa cikin wata murya dake bayyana damuwarta.

“Toh sawun giwa ya take na rakumi aka ce na kira na fada miki damuwata kuma na jiki a cikin wata damuwar lafiya Hajiya Fatee”

“Ina lafiya anje gyaran kai an kare wuya, Hajiya Kaltume ina nan cikin matsalar cikin nan, jiya da shekaranjiya ko bachi ban iya yi ba, na rasa madafa”

“Subhanallahi, baki sake kiran Malam ba? Ba na ce ki kira shi ba?”

“Na…”

Har zata yi subutar baki ta fada ma Hajiya Kaltume yadda suka yi da Malam sai kuma ta tuna gargadin da yayi mata.

“Toh zan kira shi, ni tsoron kiransa nake kar ya fada min wani abun da zai daga hankali na, domin na lura kamar akwai matsala”

“Aa ki kwantar da hankalinki Hajiya Fatee, kuma ki nuna masa damuwarki, kuma ki bi duk wani abu da zai fada miki, na san ba zai wuce kudi ba, ko kuma ya ce sai kin siya mishi wani abu, komai dai minene karki yarda cikin nan ya bayyana Hajiya Fatee domin bayyanar cikin nan matsala ce da ko mun mutu sai mun bar abun fada, duk tsanani karki yarda sirrinki ya bayyana”

Shiru Hajiya Fatee ta yi na dan lokaci kamin ta amsa.

“Toh Hajiya Kaltume, abun kunya ne kam sosai amman kuma idan ya fada min wani abun da ba zan iya yi ba fa?”

“Kamar ya? Haba ta wajena karki karyar da zuciyarki mana karki yarda ta fada miki akasin abin da na fada miki, yo Allah na tuna ko cewa yayi sai kin bashi kanki ko kin bashi jini ko rabin dukiyarki ai kya aikata saboda rufin asirinmu”

Hajiya Fatee ta yi murmushin takaici mai sauti.

“Hajiya Kaltume ni yanzu me nake da shi? Wannan bakar matar da Fadeel ya auro ai duk ta ga bayan komai nawa, duk wani boko ko malami da kika sani a garin nan babu wanda be ci kudina ba, saboda wannan bakar yarinyar kuma kudi ba kadan suke karba ba, amman babu biyan bukata ni na rasa gane wani irin abu ne wannan, shiyasa na fara yakin yanzu da bakina”

“Waya san da me ta mallake miki da, ai wasu yayan dangin maguzawa ne Hajiya Fatee, kuma su ma fa Malam nan sun iya tsibbo sosai, suka yi ma wasu ma balle yaransu, zata iya yiyu mahaifinta ne ya tsaya mata, kuma yayi mata wani abun da za a lalata duk wani shiri nake”

“Toh yanzu idan magani be yi ba, zan yi yaki da halshena, shiyasa na fada masa ya zaba ko dai kara aure ko sakinta ko kuma na yafe shi har abada kuma Wallahi zan iya saboda kura ta kai bango ba da ita da Iyami su suka ja mana shiga wahala, kara ma Iyami tana san tana amsar nata hukuncin amman ita wannan sai kara samun gurin zama take”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected