VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Gwaggo da ta gama sallame sallah a yanzu ta ce.

“Daman ai ba za a taru a dangi ace kowa sai ya so ka ba, dole za a samu wanda ba ya ra’ayinka, balle dai yadda yaron nan yake ba za su rasa matar ba shi ba”

“Gwaggo ai gabanki Hurriya ta fada mana yadda Namra da Momy suka mata gargadi akan yaron, ashe dai shi ne mijin ba su sani ba”

Amma ta fada tana mike kafarta da har yanzu bata gama warke mata ba, tana kallon Gwaggo ta cire hijabinta tana fadar

“Ki kwantar da hankali ki cigaba da yi mata addu’a ita ma kuma ta cigaba da yi domin ba bari abun da aka zaba za’ayi ba musamman Kaltume Allah kadai ya san hassadarta akan auren nan, kuma kin ga Saurayi ne ba mai mata ba balle ki daga hankalinki da tsoron abun da zai biyo baya”

“Ko mai mata ne ma Gwaggo ya zan yi tun da mahaifinta ya riga ya bada ita? Ai babu yadda zan yi sai hakuri, dan yasan Hurriya ƴata ce ai ya saka shi yin haka, da Momy ce ko Kaltume ba zai taba yi ma yaransu haka ba a daura aure ba tare saninsu ba, kuma na ji dadin da be bawa kowa siyayyar kayan ba ya kawo kudin nan yace a siya komai”

“Yanzu fa ya dawo hayyacinsa kina ganin yadda yake rawar jiki da yaran nan wai ni me yace ma kiran da yayi yanzu na ji kina masa zancen ya siya can?”

Amma ta fadawa Gwaggo abun da ya bukata, Hindu ta kyalkyale da dariya, Gwaggo da Baaba uwani suka yi murmushi.

“Ba wani nan shiri yake nema, yana son ya kyautata miki ne kuma ya samu kanki”

Amma ta tabe baki tana wofintar da zancen Hindu da be kama kanta ba.

“Hindu ke dai baki rabo da zance a bakinki, ni yanzu ina ni ina Alhaji Haruna? Daman can kaddara yara ce ta kaini kuma an haifa, Wallahi yanzu ni baya gabana gidansa be burge ni sam, ke ni fa auren ma ya fita a raina ma gaba daya na wasun mazan ma, balle na Alhaji Haruna mai mata irin Kaltume ko makiyi ba zan so ya zauna da kishiya irin Kaltume ba, kamar dai kun manta inda aka fito? Magana wannan ina son na yi amman na kasa daga kwance sai kwance babu abun da zan iya kawarwa bayan an raba ni da aurensa an juye kansa, hakan duk be wadata ba aka koma a gurin yarana? Shi kuke gani da fatan zan iya komawa? Ai har abada…!”

“Allah dai ya zaba abun da ya fi alheri amma mace ai bata cewa ba zata sake aure ba, kuma idan da yara ko an rabu kamar ba a rabu ba ne yanzu ba gashi ba? Kuma idan baki koma ba ai ita Kaltume ta samu abun da take so kenan”

Cewar Gwaggo domin ita ma a yanzu ta gano zaman auren ya fi babu, ko da wani namijin ne balle kuma uban yayanta da aureta tun tana budurwa gashi har an kai ga aurar da ƴa.

“Ni dai na hakura da Alhaji Haruna, idan har auren alheri a gare ni a gaba Allah ya kawo min wani mai mutunci da sanin ya kamata, kuma ya ba ni abokiyar zama ta gari”

“Amin, idan kuma akwai alheri Allah ya maidake dakinki Iyami, ko dan yaranki, nan gaba kadan zai ce zai karbi yaran nan kuma idan baki a gidan ba za su jidadi ba, ni dai a matsayina na mahaifiyarki ina rokon idan ya nemi maida aurensa karki juya masa baya dan Allah”

Amma ta kalli Gwaggo idonta na cika da hawaye.

“Gwaggo ban manta wahala da azabar da na sha saboda auren bawan Allah nan ba, kuma ke da kanki kika ce inda shi ne ba zan koma ba, ko da fari ku kuka karfafa min guiwar aurensa kuma… ”

“Kuma hakan be haifar miki da komai ba sai alheri, ki rika duba wannan ina son ki sani ita kaddara a rubuce take ko da Kaltume ko babu ita sai kin yi irin wannan ciwon sai haka ta faru, ita dai ta zama sanadi ne kawai kuma yanzu gashi ai kin samu sauki jinyar kuma ta zame miki ibada, bari na dubawa Hurriya maganin Infection da muka siya gurin UMMU SA’ADA WOMEN’S SHOP 09160547983”

Gwaggo ta mike tsaye ta fice daga dakin tana amsawa Baaba Uwani dake yaba kyau maganin na infection.

“Ai da yana da daci ko tsami ma Hurriya ba zata yarda ta sha ba, yadda na san Hurriya da son zaki ba zata sha ba idan yana da daci”

Cewar Amma tana share hawaye Hindu ta ce.

“Shiyasa ai nake jindadin maganinta, ba shi da daci kuma baya saka zawo ko tashin zuciya ki sha abinki kamar kina sha tea, ga aiki a jiki kuma gashi da saukin kudi daga 500 yake farawa har zuwa sama za ki ga yadda wanke marar mutum ta yi tass shiyasa aka ce kar mai ciki ta sha, gashi har kala biyu take yi da mai kamshin takafarnuwa da wanda ba shi da shi, saboda wasu basa son masu warin tafarnuwa, kuma zaka iya sha tare da miji da yara matukar sun haura shekara biyar”

“Gaskiya na ji ana yabon maganinta, mu ma dai mun fara ganin aikinsa a yanzu, Allah dai ya sa a dace kawai”

“Amin”

Wannan karon Baaba Uwani ce ta amsa sannan ta mike tsaye ta bi bayan Gwaggo da ta fice dakin. Hindu ta daki cinyar Amma.

“Ke Wallahi ki koma dakin mijinki wannan kame kamen da yake ba na komai ba ne sai na neman aure, kin san yanzu aurensa ya koma kasa saboda kin cika idda dole shi ma ya shiga cikin manema, iyaka a nemi tsari kuma ki rike addu’a ba dare ba rana, ni kam da zaki bi yawa Wallahi Iyami karki bar mijinki, Gwaggo ma shi take so”

Amma ta kawar dai tana dauko wani zancen domin ita dai a yanzu har ga Allah bata son komawa dakin gidan Appa ita kadai ta san halin da ta shiga kamin ta samu kanta a yau. Kwana da yin haka Appa ya sauka gidan da kansa tare da wani dan’uwansa da Momy ya so a zo gidan sai dai yadda ta juya masa baya a lamarin auren nan ne ya saka dole ya aje lamarinta a gefe, Bappa da dake zaune a madaidaicin falo ya kalli Alhaji Haruna a natse sannan ya fara magana.

“Akan maganar da ka yi ne, ita Iyami tace tana ganin a tafi da kanwar Gwaggon yara wato Baaba Uwani da kuma kanwata Innar su Nasiru da Ibrahim dake can sokoto zan yi waya da ita ta zo sai ayi tafiyar da ita, da kuma Hindu, sai su ku duba kayan a tare da naka yan’uwan”

Appa ba haka ya so ji ba, domin ya so ayi tafiyar ne da Amma, kamar yadda yayi da Kaltume a lokacin da za su zabawa Maama kayan daki.

“Hakan yayi Bappa na gode sosai Allah ya saka da alheri, hakan ma wata alfarma ce, ina godiya Bappa kuma ina kara bada hakuri akan abubuwan da suka faru, ita kaddara haka take a yadda aka rubuta haka take zuwa, wani lokacin sai ido ya rufe hankalin ya gushe ka aikata abun da baka yi tunani ba, ba dan Allah ya rubuto haka ba Wallahi ban yi tunanin rana zata zo irin wannan ina raye ace bana tare da mahaifiyar Hurriya ba”

“Haba wacan maganar ai duk ta wuce, sai dai ayi fatan Allah ya tsare gaba”

“Amin Bappa”

Appa ya kalli dan’uwansa Alhaji Musa, Alhaji Muss na ganin kallon da Appa yayi masa ya fahimci inda ya dosa sai yayi hanzarin cewar.

“Bappa idan da hali ai sai a kira mana ita Iyami, akwai maganar da zamu yi da ita akan sha’anin bikin nan”

“Toh babu matsala zan turo ta yanzu”

Bappa ya tashi ya fice daga falon da aka gina daga waje domin baki. Cikin gidan Bappa ya shigo ya zauna a kujerar roba dake aje kusa da Amma.

“Mun yi magana da shi na fada masa yadda muka yanke, yayi ta godiya kuma ya kara da bada hakurin abubuwan da suka faru”

“A Duk lokacin da ya zo sai ya bada hakuri, shi kam ya fahimci mun hakura mana, gashi ana abubuwa gwanin sha’awa ma”

“Ni ma dai shi na gani, daman shi aure ai ya gaji haka, tare da wani dan’uwansa ya zo shi yace suna son ganin Iyami akan maganar Hurriya, na fada masa zan turo shi”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected