VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Rukayya”

“Na’am”

Rukayya ta amsa daga dayan dakin sannan ta fito

“Gani”

“Dan Allah shiga ki dauko min twins”

“Okay”

Amma ta juya ta koma dakin Gwaggo ta zauna, a dakin Rukayya ta kawo mata su, ta shimfida su a saman gadon Gwaggo, Amma ta dauki Hamid ta bashi nono sai da ya koshi sannan ta bawa Hamad shi ma, ta kwantar da su ta kwanta gefensu ta kai hannu ta shafa Hamad tana murmushi sai hawaye suka zubo mata. A ranar Amma ta kwana cikin tunani kala kala. Misalin karfe uku na dare ta ji kamar an tashe ta sai ta bude ido, ga mamakinta arba ta yi da rana ta haska sosai kamar karfe biyun rana. Da sauri ta sauko saman gadon tana mamakin wane irin bachi ta yi haka bata farka ba har rana, kuma wani be tashe ta ba.

“Gwaggo Gwaggo Gwaggo”

Ta shiga tashin Gwaggo. Gwaggo ta tashi zaune tana murza ido.

“Lafiya Iyami?”

“Gwaggo rana ta yi kalle fa”

Gwaggo ta juya ta kalli dakin har zuwa windows ita dai dare take gani, Gwaggo ta tashi ta nufi makunnin wutar dakin ta kunna, sai haske ya baibaiye dakin, a take ranar ta bace a idon Amma.

“Karfe ukun dare ne fa yanzu Iyami, lafiya kike kuwa?”

Gwaggo ta fada bayan ta duba agogo falon. Sai dai Amma bata ji da ganin komai sai muryar mutum hudu da fuska daya, mace ce mai manyan idonawa kamar girman kwai, ga bakin gashi da aka birkita ya yamutse, da bakin tufafi, wannan na nuna mata Yamma tana cewa ki bi nan. Wannan na nuna mata gabas tana cewa ki bi nan, wannan na nuna arewa dayar na nuna kudu, kowa kuma cewa yake ki bi nan bi nan.

“Innalillahi wa’inna Ilaihiraji’un
Innalillahi wa’inna Ilaihiraji’un
Innalillahi wa’inna Ilaihiraji’un ”

Shi ne abun da ta yi ta maimaitawa ta sai dayar dake hadu ta miko hannu ta buge mata baki. Amma ta yi baya ta fada kan twins dinta har sai da Gwaggo ta dagota daker ta janye yaran sannan ta fara tofa mata addu’a, kamin ta fita ta kira Bappa da Rukayya. Haka suka zo suka rufe tana suna ta tofa mata addu’a sannan Rukayya ta dauko alkur’ane ta fara karanta mata, daman daga iya sai Iyamin ne suka yi sauka, Rukayya sai ta maida hankalinta bangaren boko bayan saukar Iyami kuma bata cigaba ba bayan Primary domin a lokacin babu hali, sai kawai ta saka ga aiki a gaba da kuma karatun addini.

Har safe Iyami bata motsa ba har lokacin kuma idonta a rufe yake. Gwaggo ce ta fara bada shawarar a nemi masu maganin hausa, Bappa kuma ya karkata bangaren Asibiti.

“Wane irin asibiti kuma rana fa ta fara gani kamin komai ya faru kuma na fada maka, karfe uku na dare amman tana ce min rana ta yi”

“Toh tun da kun fi sha’awar na hausar sai ayi, amman dai da mun fara kaita asibiti, wata kila ma damuwa ce ta yi mata yawa damuwa babu abun da bata sakawa”

“Shi ke nan Malam mu tafi asibitin”

Ba dan ranta ya so ba aka dauki Amma zuwa asibiti, suna zuwa kuwa aka bata gado likitoci suka hau dubawa. It take them a week ba su gano komai dake damunta ba, daga lokacin aka dawo gida aka fara yin na hausa shiga nan fita nan babu wani canji ko’ina kuma da abun da ake fada, wasu su ce kishiya ce wasu su ce karo ta yi wasu kuma su ce gidan ke da aljannu. Kowa da abun da yake fada, withing 5 Months Amma ta zama abar tausayi domin bata iya komai sai an mata a kwantar a tayar bakinta kuma bata iya cewa komai sai dai ta yi ta kallon mutane da ido. Wani karin abun tausayi idan twins dinta suka kuka sai dai a daukesu a ciro nononta a basu idan suka gama sha a ciresu. Haka zata yi ta kwanciya idan aka auna kwanciyar ta isheta sai a tayar da ita zaune a jingina. Ganin abun ba zai yi ba aka sake maida ita asibitin a lokacin da suka sake bincike sai suka ce hawan jini ne ya same ta har ya haifar mata da wannan matsalar, sai kuma hankali ya koma gurin shan maganin asibitin, haka dai aka yi ta yi asha na asibitin ayi na hausa amman babu sauki babu alamarsa. Kusa kullum sai an saka mata karatun kur’ane wani sa’in kuma Rukayya zata zauna kusa da ita ta yi ta karatun kur’ane.

 

THREE YEARS LATER….

A dakiku ma akan samu canjin rayuwa, balle kuma azo ga mintuna da awanni, ranaku sati ko wata ba a lissafinsu balle kuma shekaru. Da yawa an shafe wasu shafunka a rayuwar Hurriya an sabunta wasu, an busawa wasu rayuwa. Ta kan manta abubuwa da yawa, kuma ta karbi wasu kadarorin ta rumgumi sabuwar rayuwar dake fuskarta, ta saba da wasu dabi’u da halayya. Sai dai har yanzu ta saka yarda dan’uwanta ya tafi ya barta, ta kasa karbar wannan kaddarar, kuma ta kasa manta ranar da aka sanar mata da mummunan labarin da har gobe take karyatawa. Musamman a yanzu da girma ya gina mata sabon daki, a duk lokacin da wani abun dadi ko akasin haka ya same ta babu wanda take tunawa sai dan’uwanta, idan wani ya tsangwame ta a gida, mai bude hannayensa ya tare mata fada take tunawa, ranar da suka yi Candy idan ta kalli dama da ita bata ganin kawayenta sai dan’uwanta, babu daren da bata mafarkinsa, babu sallah da bata addu’ar dawowarsa.
Yar karamar takardar ce a hannunta tana shafa harrufan da tuni ta da haddace rubutun dake jiki, hawaye na jika kumatunta, a ranta take ta maimaita karatun da. Numfashi ta ja da karfi ta daga kanta ta kalli madubin dake gabanta wata mace ce zane a gaban madubin mai tsananin kyau sura da kyawun halitta da haifa, mai fari da yalwar gashi kamar ƴar Ethiopia. Garin gilashin dake mata mata garkuwa ya kara mata kamala. A natse ta lumshe ido ta hade yawu a hankali.

“Hurriya kina ina? Jiranki fa ake”

Ta bude idon da sauri, ta bude drawer madubin ta saka takardar ta rufe sannan ta mike tsaye ta share hawayenta ta dauki mayafin abayarta ta shafa a saman kanta sannan ta nufi kofar fita da saurinta. Tana bude kofar Momy na bude tata kofar da kan kace kwabo Hurriya ta sauko idonta kasa ta tsaya jikin kofar har sai da Momy ta sauka sannan ta sauko ta fice daga bangaren. Tun kamin ta isa bangaren ta fahimci kowa ya gama tafi domin babu mota ko daya a bangaren Hajiya Kaltume, cikin zullumi ta karasa ta shiga falon sai ta ga ko’ina wayan babu kowa. To daman waye zai tsaya jiranta ita banza a banza.

“Yauwa yar abaya daman a komai ai ke ce baya, kowa ya tafi ke kina can boye yanzu zaki fara karyar baki san sun tafi ba, daman ina bakinciki zai barki ki tafi abun yan’uwa? Hassada ai ta gama cinye ki”

Ta dago tana duba Hajiya Kaltume dake saukowa tana jefar Hurriya da duk kalmar data fado bakinta. Hurriya ta rike hannayenta kana kallon fuskarta zaka san kalaman Hajiya Kaltume ba su mata dadi ba, sai dai ta saba jin wadanda suka fi su ma daga bakinta ko na yayanta babu abun da yake sabo a gareta yanzu, ɗacin kuma ta barwa zuciyarta. Ta juya jiki babu gwari da zimmar ficewa sai aka turo kofar falon, kyakkyawan bakin saurayin nan mai matukar cikar kamala da mazantaka ya shigo falo fuskarsa dauke da murmushi bakinsa kuma kunshe da sallama. A take Hajiya Kaltume ta washe baki.

“Maraba da Fadeel yanzu ake tafe?”

“Eh ina wuni Hajiya?”

“Lafiya kalau ya aikin?”

“Alhamdulillah”

Har ya zauna Hurriya dake tsaye yake kallo, be dauke idonsa ba har sai da ta mika masa gaisuwa da muryarta mai matukar sanyi, so innocent.

“Ina wuni”

Kamar daman gaisuwar yake jira sai ya dauke idonta after ya amsa ya kalli Hajiya Kaltume.

“Hajiya ce tace na zo na dauki Khairi wai ko bata samu mota ba?”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected