VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Yana shiga dakin ya nufi wata kujera ya dafa kanta ya sauke kansa kasa ya rufe ido. Kamar an tsikare shi ya bude idonsa ya juyo da sauri ya fito daga dakin, tafiya yake mai kama da gudu ya sauko stairs din.

“Ina wayata?”

Ya tambayi Ammynsa sai Momy ta bude jakarta ta dauko ta mika masa tana hawaye. Ya saka hannu biyu ya karba ya juya ya koma ciki.

“Yaya da gaske barinsa zaka yi ya auri yarinyar nan? Wallahi bata kai ba Yaya bata yi matsayin da zata zama surukar mu ba”

“Idan aurenta ne abun da Captain yake so, zamu nemi aurenta kuma iyayenta za su ba mu ita dan dole ko da bata so, Allah ba hallatawa iyayen autawa Yayansu wanda basa so ba, ya dai mata ikon zaba musu na gari, kamar yadda ya hallata auren mazina idan sun tuba”

Ammy ta dubi Engr

“Ni fa ban gane ba, da gaske zaka aura masa yarinyar nan kenan? Ni ba da yawun bakina ba ba zan yarda Captain ya zauna da wannan yarinyar ba, ai abun kunya ne ace wannan yarinyar ta zama surukar mu duk matan duniya a rasa wanda zai aura sai karuwa?”

“Ina tunanin kin fi ni son farinciki Captain…”

Ta kawar da fuskarta ta fashe da kuka.

“Wannan goyon bayan da zaka ba shi be yi ba Yaya, be kamata ka biye masa ba shi fa soyayya ce take dibansa lokacin da zata zubar da shi zai fada a mugun guri ne”

Wata kanwarsa ta fada. Engr ya mike tsaye rike da takardar sammacin ya ce.

“Idan har kuna ganin akwai rashin dacewa a auren yarinya to ku roki Allah ya sauya masa da wanda ta dace, kuma ki kwantar masa da hankali ku nuna masa illar hakan, idan ya sauya ra’ayinsa Falillahil-hamdu ”

Ya nufi kofar fita ya fice daga falon yana kiran wani Assistant manager. Sai da ya fita sannan Momy ta dubi Hajiya Turai ta ce.

“Karki yarda Wallahi ta ya za’a kawo miki wannan yarinyar a matsayin suruka? Taya? Ai da kunya ma”

“Wani gine ne Captain yake son na dora wanda ba zai iya karasa ba, ni dai kam ba zan taba karbar yarinyar nan a matsayin suruka ba”

Ammy ta fada tana share hawayenta. Wata step Mother din Engr ta dubi Momy ta ce.

“Kuma da gaske yarinyar nan ta aikata abun nan?”

“Ba mu da tabbaci, ko da ace ba da gaske ba ne, ai be kamata ya aureta ba Hajiya, saboda duniya ta gama ganinta”

“Idan shari aka yi mata bana ganin illar aurenta a gurin Jamal, illar kawai ace ta aikata ne, shi ma kuma idan ta tuba Allah zai karbi tubanta kuma yayi mata sakamako mai kyau, domin Allah yana son bayinsa masu komawa a gurinsa suna kuka suna rokon ya yafe musu, shin idan hakan ya faru da yarki zaki so wani ya juya mata baya? Ku yi tunani mana”

“Ko ma dai minene Hajiya ba zamu yarda Captain ya auri yarinyar nan ba”

Momy ta amsa mata kai a ranta tana cewa saboda ba jikanta ba ne take fadar haka. Safa da marwa yake waya a kunnesa yana jiran wanda ya aikawa kiran ya amsa.

“Nafi’u ka duba hotunan kuwa?”

Ya gabatar masa da abun da yafi daukin ji fiye da gaisuwarsa da sallama.

“Sir barka da yamma, eh na duba”

“Ya ake ciki? Editing ne i know”

“I’m sorry Sir gaskiya ba editing ba ne, na duba na yi bincike ni da entire team dina ba mu ga wata alama dake muna editing ba ne”

Captain ya kai hannu ya shafa kansa ya runtse ido sosai.

“Maybe baka iya aikinka ba, maybe baka duba inda ya kamata ka duba ba”

“Na iya aikina ranka ya dade kai ma ka sani, wata kila da wannan gaskiyar mai nauyi ce shiyasa ka kasa karbarta, amman na gano wani abu”

Ya bude idon da sauri ya nufi bathroom ya bude ya shiga ba dan ya boyewa wani ba sai dan rudewa da yayi jin abun da yake nema zai samu.

“Alamu ya nuna yarinyar nan bata cikin hayyacinta aka yi hotunan, ko kuma tana cikin bachi mai nauyi domin jikinta ya saki sosai, yadda yake rikota da ace a hayyacinta take ba ta yi yaukin jiki haka ba, kuma babu inda take shauki ko murmushi shi ne kawai yake yi, shi ma kuma akwai alamar tsoro a tare da shi ko kuma rashin kwanciyar hankali, yadda hannayensa ma suke a jikinta ya nuna shi yake rike da ita”

Captain ya zauna a jikin bathtub yana murmushi.

“Thank You, Thank You…  Ka gano wanda ya dora hotunan?”

“Shi ne ban gano ba, na yi bincike na biyeye abubuwan da suka kamata ban gane komai ba, amman na bibiye wandanda na ga hotunan a account dinsu na Facebook wasu unverified pages ne masu neman labari wasu kuma daidaikun mutane ne, sai da na bibiye wanda aka fi sharing hotunan da ya rufe wasu bangarora na jikinta sai na samu wani dan jarida ne a Kano, and na dauki wayarsa na fada masa daga ina nake kiransa kuma na tambaye shi a ina ya samu hotunan sai ya ce min a wani account ne, ya fara gani, dayan kuma a bauchi yake shi kuma yace min turo masa hotunan aka yi, na bukaci ya fada min account din da na bincika sai na samu an goge account din”

“Kana aje wayar nan, ka duba list din mutanen da suka dora hotunan karka damu da yawansu ka turo min su, tare da sunanyen gidanjen jaridun, ka hado min da account number dinka”

“Okay Sir”

Ya sauke wayar.

“Za su san sun taba mai gata, na miki alkawarin farinciki Hurriya zan cika miki shi… ”

Ya fada sannan ya nufi madubin dake bandaki ya dora wayar ya cire tufafinsa ya sakarwa kansa shower. Ya bata minti arba’in a bandakin sannan ya fito yana rike da wayarsa jikinsa kuma na daure da tawul.

“Good Nafi’u”

Yayi forwarding sakon zuwa mabanbanta gurare sannan yayi waya da mutane daban daban. At the end ya kira Namra.

“Hello Captain”

“Wace asibiti aka kai Adam? Kanen Salim”

“Ban sani ba, ya jikanka?”

“Bincika min yanzu”

“Toh”

Ya aje wayar ya dauki wani tawul din ya goge jikinsa, sannan ya zauna gaban madubi yana hararo abubuwa da yawa. After like one hour yana zaune kan carpet bayan ya sallame sallah wani kiran ya shigo a wayarsa bayan na calls din dake ta shigo masa na yan’uwa da abokan aiki masu son tambayar jikinsa. Amman be amsa kiran kowa ba sai na Namra.

“Yana yana asibitin Yariman Bakura, layin ya hadurra”

“Good”

Ya yanke kiranta tun kamin ta kara cewa komai, ya shiga whatsapp dinsa ya sake sauke hotunan da Salim ya turo masa, ya yanke iya gurin da fuskar Adam take ya turawa wata number tare da address, sannan ya fito whatsapp din ya shiga contact dinsa ya nemo number the same person da ya turawa sakon ta whatsapp.

“Hello Sir”

“Uzairu na turo maka hoto da addreshin wani dan’iskan yaro yanzu a whatsapp, ni ya taba so the fight is between me and him.. Ka duba address din ka dauki mutanenka ki shiga cikin asibiti ku dauko shi ku aje min shi wani gurin da babu haske kuma babu rahma, ku masa doka irin dukan da idan na masa tambaya zai ba ni amsa a take amman ban ce ku kashe shi ba, ku aje shi a gurin for 10 hours”

“Yes Sir… ”

Ya sauke wayar, sannan ya amsa dayan kiran daya fito daga bachi.

“Yeah good so nake ku kama mai gidan jaridar ku bincike shi a ina ya samu hotunan, at the end ku sa ya rubuta cewar sheri aka yi mata kuma yana neman yafiyar Hurriya, ku saka yayi hakan tun a cikin office din ku idan be yi haka ba ku karya kafarsa”

“Amman Captain me yayi maka?”

“Yarinyar da suka batawa suna yarinya ce mai tsada she is innocent, please karku ragawa kowa a gurin”

“Subhanallahi, aiko za su ga aikin DSS”

“Thank You My friend”

Ya sauke wayar ya amsa wata wayar, haka yayi ta bata umarni a inda umarninsa suke jira a inda alfarma yake nema sai ya roki ayi masa haka.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected