Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Hajiya Kaltume ta dan yi shiru kamar mai tunani kamin ta karasa saukowa ta amsa masa.
“Eh… Amman ta samu daga baya, sai dai ko idan zaka ka leka ne”
“No daman akwai inda zan je kawai saboda Hajiya ta matsa ne ya saka na zo na kaita, amman tun da ta samu shi ke nan ai”
Ya mike tsaye, Hurriya ta dan kalleshi tana jin kamar tace masa ya aikata ya kaita, kuma bata isa ba domin Hajiya Kaltume na tsaye a falon, ko da ma ace bata gurin abu ne mai wahala Hurriya ta iya rokon abu.
“Ba zaka tsaya ka sha ko ruwa ba? Hurriya kawo masa ruwa mana”
“No tafiya zan yi ai”
“Sai fa ka sha zauna mana sa nan da gurin Hajiya Fatee ai duk gidanku ne, kunya kuma na miye?”
Baya son musa mata dan haka ya zauna yana murmushi kamar yadda ita ma take murmushin. Hurriya ta nufi hanyar kitchen bata jima ba ta fito rike da gorar ruwa da cup tana kokarin ajewa ya mika hannu ya karbi gorar ya bar mata cup din, kamar ya san burin da take da shi a zuciyarta sai ya tambaye ta.
“Ke miyasa baki je ba? Ko baki samu motar ba ne?”
Ta daga masa kai a hankali kamar wadda bata son motsi.
“Muje na sauke ki”
Ta juya zata kalli Hajiya sai ta jiyo Hajiyar na fadar.
“Aa haba ka tafi kawai gurin aikinka, ai bata yi niyar zuwa ba ne, shiyasa ta boya sai da kowa ya watse sannan ta fito”
Kalma daya bata isa ta musa ba a cikin kalaman Hajiya Kaltume, dan haka bata ce komai ba ta sauke kanta kasa.
“Ko maybe bata son shiga mutane ne, na lura she’s different, can i drop you?”
Ya karasa da son ya ji amsarta sai ta daga masa kai ba tare da ta kalleshi ko ta kalli Hajiya ba, domin har ga Allah tana son zuwa birthday party din na Khari da ta hade da graduation dinta.
“Hajiya na gode zan ajeta sai na wuce”
“Toh Allah ya kai ka lafiya”
Ya wuce gaba, Hurriya ta bi bayansa har lokacin kanta na kasa, Hajiya Kaltume na watsa mata harara kamar ta fisgota ta yi ta duka haka take ji. Suna ficewa ta tashi ta nufi stairs duk yadda ta so yin sauri bata iyawa saboda jikinta baya barinta ta wala yadda take so. Tana isa bakin kofar dakinta ta kai hannu ta tura kofar dakin zata shiga sai ta ji kamar an turata haka ta tafi suuuuu ta fadi kasa ridd rub da ciki.
“Subhanallahi”
Ta fada sannan ta yunkura ta tashi zaune tana jan kafa ta isa bakin gadonta ta zauna ta daga zane ta duba kafar dake mata mugun ciwo.
“Ya haka abu dai kamar an turo ni”
Ta latsa cinyarta dake cike da tsokar nama tana runtse ido saboda zafin da yake mata. Karar wayarta ne ya dago hankalinta ta kai dubanta gurin da wayar take Hajiya Fatee ce a line hannu ta kai ta dauka ta danna picking ta saka a hands-free ta aje wayar saman gado.
HURRIYA POV.
Tun da suka fita daga gidan idonta na gurin titi da motocin dake ta zirga zirga, Fadeel ma be ce mata komai ba kwarjininta ya cika masa ido ta yadda har ya kasa tambayarta gurin da zai kaita. Kallonta ma sai yayi da gaske yake yi, shi ma kasa kasa, yayi kanwa ta hudu da ita amman ya samu kansa da jin nauyinta, maybe because tana so Innocent ne kuma saboda tana kyau ne irin mai cika idon nan da haifar da natsuwa, or maybe kuma saboda tana karama ne she’s too young yaja ta da hira. Ganin suna ta dawowa the same road da suke tafiya ya saka ta dago ta kalleta sai yayi mata dan murmushi kadan.
“Ban san even center din da za’ayi party ba”
“K_Candy Event Center”
Muryar ta fito between her two soft lips.
“Okay….”
Ya cigaba da tukin, after like ten minutes ya sake yin magana ba tare da ya kalleta ba.
“Yaushe za’ayi naki birthday”
Ta yi shiru kamar bata ji shi ba.
“Ko an yi?”
“Ba ayi ba, amman ya wuce”
“How old are you?”
Uffan bata ce masa ba har suka isa gurin ya faka motarsa ta bude zata fita sannan ta ce.
“19…”
Ya bita da kallo har ta fice.
“Thank You”
Ta rufe masa motar a hankali sannan ta nufi hanyar shiga tana tafiya kamar mai tausayin kasa.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
@
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
8⃣
Tana isa gurin masu aikin tsaron kofar suka tareta.
“Ina zuwa?”
“Ciki”
“Ina katinki?”
Sai a lokacin ta tuna ta ji Khairi da kawayenta suna maganar gate pass amman bata maida hankali ta karba ba ganin ita din ta gida ce.
“Yayata ce take yin biki ciki, ba na bukatar gate pass”
“Gaskiya ba zaki ita wucewa ciki ba sai da gate pass”
“Toh ko zaka taimaka ka kira min ita dan Allah”
“Ki kirata da wayarki mana”
“Ba ni da waya, amman zaka iya ara min taka”
Har yayi kamar zai hanata sai kuma ya ciro karamar wayar ya mika mata. Number Ya Yasir ta saka ta kira shi few rings ya daga.
“Hello Yayana”
Yana jin kalmar Yayana ya san cewa Hurriya ce.
“Hurriya waya waye wannan”
“Na wani ne, na zo gurin birthday din Yaya Khairi ne, kuma ba ni da gate pass shi ne suka hana ni shiga”
“Kin fada musu ke kanwarsu ce? Ya aka yi ma baku shiga tare da su ba”
“Eh na fada musu, sun riga ni zuwa ne na ji muryar Namra tana min magana ko da na fito ita ma ta wuce, sai wannan dan Hajiya Fatee ne ya kawo ni”
“Zan kirata ta fito ta shiga da ke”
“Toh Yayana na gode”
Ta katse kiran ta mika masa wayarsa.
“Na gode Allah ya saka da alheri”
“Amin”
Ya amsa sannan ya maida wayar aljihu. Rumgume hannayenta ta dan ja baya kadan tana kallon kofar. Wani matashin saurayi ne ya fito yana tambayar masu gadin ina wadda ke tsaye.
“Gata can”
“Ku barta ta shigo”
Hurriya na jin haka ta nufi gurin, guy ya kalleta sama da kasa.
“Shigo”
Ta cira kafa ta fara takawa ta shiga ciki, dim Light ne ko’ina sai sauti ke tashi, tun daga yanayin samari da yan matan da aka tara a gurin zaka fahimci ba biki ne na masu mutunci da sanin ciwon kai ba. Kusan ita kadai ce take sanye da abaya dukan nin kawayen Khairi suna sanye da English wears, wasu ma kansu babu dankwali tsabar wayewa da rashin tarbiya.
“Ga Khairi can”
Gayen dake take mata baya ya nuna mata yayarta. Hurriya ta daga kai ta kalleta tana sanye da wata riga kamar yar bayahuda, kanta babu dankwali kanta ya sha gyara an zuba mata attachments din har gadon bayanta, makeup din da aka yi mata ta kara mata kyau gaba daya ta canja kamar ba ita ba. Mamaki ya saka Hurriya bude baki tana kallonta bata sanin wayewar Khairi ta kai haka ba, aranta take ayyana yadda Yasir zai ci ubanta idan ace yana gurin.