Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Say that again”
A wani yanayi da ya fi kama da rauni da tausasa halshe ta maimaita.
“…Ya.. Ya…”
In a gentle way ya shigar da lip dinsa na kasa a bakinsa ya jika shi da yawunsa, yadda take furta kalmar YAYA ya san he missed alot, me yasa ba zai so ta kira shi da Yayanba? Ita din ba kamar yar’uwarsa ba ce?
“Repeat it…”
“…Yaya…. ”
Ta sake fada da sanyin murya irin mai tsoro aikata kuskure, har tana tambayar kanta ko dai bata furta daidai ba? Ko kuma dai yana son ta yi ta fada ne har ya fusata bayan ta san baya maimaita kansa.
_Miracle_
Ya furta a ransa yana kallon idanuwanta da farin yayi fari kamar watsa ruwan madara a ciki.
“Uhmm mmm”
Ya amsa irin amsar dake nuna ta fito ne daga kasan zuciyarsa.
“Ina son na tambayi wani abu…”
Wani shaukin kallonta ne ya daukeshi ya lulashi a wata duniyar da ya haddasa bugawar zuciyarsa a mabanbantan dakiku, natsuwarta na neman bukata a gurinsa ya saukar masa nishadi da ya samu kansa da lumshe ido ya bude yana kallonta kamar mai jin bachi.
“Name what ever you want girl…”
Ta hade hannayenta biyu guri daya ta rankwafar da kai, a wata murya da ta fi kama da tausayi da shagwaba ta ce.
“Kai ne ka ba ni wata takardar ranar da Hamad ya bata? Har ka yi min alkawari zaka dawo min da shi?”
“Me yasa baki manta ba?”
Kwaryar ididonta ya fara tara ruwan da aka sirka da gishiri.
“Har yanzu ziciyata ta kasa amsar cewar Hamad ba zai dawo ba”
Ta tako ta matso kusa da ita yana kallonta
“Ni ma zuciyata ta kasa karya alkawarin da na daukar miki…”
Ya kara motsawa dap da ita ya rage tsawonsa har tana jin saukar numfashinsa.
“Wata kila zai dawo…!”
Zuciyarta da mugun karfi, ta bude baki saboda numfashin dake fita ta hancinta na kokarin karewa.
“Ina fatar haka…”
Ta furta muryarta can kasa sosai. Shi ma sai ya bata amsa da muryar mai dadi da ta fi kama da rada ya ce
“Idan wannan ne farincikinki… Ni ma ina fatan haka Hurriya… Duk wani abun da zai yaye miki damuwa ya sakaki a cikin farinciki ina fatan ki same shi”
“Kana da kirki kana damuwa da ni, thank you for understanding me”
Kamar wata kwarariya haka ta yi masa magana muryarta a kasa fiye da yadda ta muryar shi take a lokacin da yayi mata magana.
“We all need that someone who get us like no one else, a right when we needed the most, you need shoulder to cry on…”
hura mata iskar bakinsa mai kamshi a fuskarta, atak, sai ta lumshe ido, murmushi ya fadada fuskarta hawayen bakinciki da suka rikide mata zuwa farinciki suka kawata kyauta. Kamar wanda ta tuna wani abu murmushin fuskarta ya bace bat, sai ta matsa baya da sauri ta bude idonta ta juya da fice daga kitchen din. Murmushi yayi ya taka backwards yana shafa kansa, ya daga gorar ya sha ya aje, sannan ya kai hannunsa saitin da aka aka yi gurbin zuciyarsa.
“Ajiya ce wannan, please ki ba ni hadin kai, saurin fushi breaking up with so many girls wannan duk na yafe miki, karki raba ni da wannan she’s special na gane haka from DAY 1 na san ke ma kin san haka… ”
Ya rufe idonsa ya sauke dogon numfashi, ya kai ma zuciyarsa duka a hankali yana aje mata sako.
“Idan kika raba ni wannan ni da ke duka zamu cutu, wata kila mu salwanta in one way or the other, so try to be strong please, ki ba ni hadin kai i hope you understand me”
Zuciyarsa ta buga da karfi tana raba sakon da yayi aika mata ga sauran sassan jikinsa da suka kasance mukarraban aikinta. Ya bude idon yana murmushi, sai farinciki yake kamar wani sabon ango, ba shi da kwashe kwashen mata, amman idan ya ga wanda hankalinsa ya kwanta da ita ya kan tallata mata soyayyarsa, sau uku ya taba yin haka, sau biyu aka yi nasarar saka ranar aurensa aka fasa saboda rashin hadin kan da zuciyarsa take ba shi. Falo ya fito ya zauna yana kallon tv sai dai gaba daya hankalinsa ba a gurin tv yake ba. Ya kusan minti goma shabiyar da zama sannan Appa ya sauko Momy na bayansa waya a kunnesa.
“Gani nan zuwa”
Ya fice tare da twins dinsa, sai jan rigarsa suke. Momy ta zauna tana mamakin ganin Captain domin Appa be fada mata tana da bako ba, ko da yake ba zata kira shi da bako ba a yanzu daman tuni ya zama dan gida. Namra ma da ta haura sama da bacin rai bata fada mata Captain ya zo ba.
“Ban san ka zo ba?”
“Saboda Appa yana nan ne, tun dazun na zo ai”
“Maa Shaa Allah yau dai na san babu aiki yau Sunday, kuma na ga farinciki a fuskarka a yau fiye da ko yaushe, kana albishir ne?”
Yayi murmushi shi kansa ya san fitowarsa daga kitchen zuwa zamansa a falon nan ya banbanta da kullum, and baya bukatar wani ya fada masa yana farinciki ya fahimci haka tun a lokacin da sexy voice din Hurriya ya huda kuunnesa har ya karya dokokinsa, ga kuma numfashinta da ke masa yawo a saman hanci har yanzu.
“Wata kila nan gaba kadan na yi albishir, farincikin kuma ina fatan ya daure har abada”
“Allah ya tabbatar maka da shi”
“Ameen Momyna that’s why i love you kina son farincikina”
“Kai dan gatan family mu ne Captain, idan wani be so farincikinka ba, to be so Familynmu ba”
Ya bude baki ya rufe yana murmushin gefen baki. Daga bisani ya kalli Momy ya aika mata da tambayar abin da ya tsaya masa a rai.
“Momy me yasa kannen Hurriya ba su taba zuwa gidan nan ba sai yau?”
Momy ta dan tabe baki.
“Alhaji ya juya musu baya tun da aka haifesu, ni kaina na yi mamakin yadda yau ya shigo min da su dakina ya dorasu har kan gadona yana wasa da su”
“Why?”
“To Allah masani Captain, wata kila shiga tsakani ne”
“Kuma mahaifiyarsu ba ta yi tunanin ta kawo su ba?”
“Ta ina? Ka manta na fada maka bata da lafiya? Aiko hannu bata iya dagawa, bata magana bata iya komai nan gaba kadan ma wata kila bara zata koma, domin dai ance duk abun da take da shi ya kare, daman talakawa talas shiyasa kwadayi ya ja ta auri Alhaji, yanzu kuma ta auren ya kare sai ta koma babu komai, ita fa wannan Hurriya kaskantacci ne uwarta ga aiki ta yi, ta zo gidan ta bangare Kaltume daga aiki ta aure Alhaji shiyasa Kaltume bata kaunarsu ko kadan ai, kara ni ina da zuciyar imani ina ragama mata amman can ba ta sha da dadi ai”
“Mahaifinta mai kudi ne i guess to me ya kawo zancen kaskanci?”
“Ai wannan talauci da uwarta take ciki ba zai taba gogewa ba a ido, kuma ba zai taba barin mutane irina su ga kimarta ba, ba gashi nan ta koma a kwance ba, da ynzu tana da arziki zata tsaya jinya haka ne? Shekara hudu yanzu ana fama da abu daya, ko Kaduna ba su taba kaita ba balle a fitar da ita, kuma wani lokacin da tana da kudi ai ba za’ayi ma yarta ko ita ba, yanzu ka hada ta ni? Ko ka hada Hurriya da Namra? Ai ba za su tana haduwa ba har abada, ka ga fa gidan nan kowa yana karatu wasu sun kare amman ita tun da ta gama SSCE ubanta ya aje ta gefe ko kallonta baya son yi, ya ki sakata makaranta da uwar tana da kudi ai ba za a yi ma yarta haka ba, ko kuma ta dauki matakin shari’a ta karbe yarta ta saka ta makaranta mai kyau”
Jawabin da Momy ta kora masa, be kara masa komai ba sai tausayin Hurriya, bayan kalubalen da take fuskanta a gidan ga damuwa na rashin uwa da dan’uwa a kusa, ga kuma rashin lafiyar ido, yanzu kuma ya kara jin halin da mahaifiyarta take ciki, talaucin da ya hana su ganin kimarta a gidan, ya kara mata martaba da tausayi a idonsa.
HURRIYA POV.