VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Bari naje na dauko…”

“No bari na dauko”

Kamin Hurriya ta sake cewa komai ta juya ta nufi cikin gidan. Hurriya ta juya zata bi bayanta sai ya kirata.

“Ina zaki je?”

“Zan taya ta daukowa ne”

“Hmmm baki son yayarki ta wahala kenan, ni kuwa na saba bata wahala kullum saboda sai na ce ina gaisheki”

Hurriya ta yi murmushi ta bi bayan Namra, a tare suka dauko kujerun biyu ta nufi bangaren da Motar Momy take suka aje a gurin, yana ganin haka ya san baya bukatar ace masa ya karaso ya zauna, dan haka ya cira kafarsa ya gurin ya zauna a kujerar da Hurriya ya aje. Namra kuma ta zauna a dayar, sannan Hurriya ta koma ciki ta dauko musu ruwa da cups ta aje a gabansu.

“Ke ina taki kujerar?”

Hurriya na kallon Namra sai suka yi ma juna murmushi saboda tunawa da ta yi da cewar ta fada cewar zata tsaresu da ido har sai ta gano komai.

“Tana falo tana jirana, a sha ruwa lafiya”

Ta bar shi a gurin ta wuce, sai ya bita da ido har sai da ta kauce daga ganinsa sannan ya juya ya kalli Namra.

“Kanwarki nan tana da kirki, kuma tana da kyau ba zan yi karya ba”

“Yeah haka ake yawan fada duk ta fimu kyau, kuma maganar gaskiya ta fi mu kirki, Hurriya tana da kirki sosai”

“Maa Shaa Allahu haka ake so, ina take karatu?”

“Tukuna nan dai bata fara jami’a ba”

“Why? Takardunta ba su fito ba ne?”

“Sun fito kuma sun yi kyau domin tana da kokari sosai, akwai abun da Appanmu yake jira ne shiyasa be saka ta ba”

“Ko aure za’ayi mata?”

Ta yi dariya.

“Mu ma da muka gama jami’a muke maganar zuwa NYSC ba a yi mana aure ba balle ita, ita ce karama a gidanmu yanzu”

“Oh… Na tambaya da tsoro fa, i thought answer ki would be yes”

Ta yi murmushi mai alamar tambaya.

“She’s too shy bata son tsayawa ma, tana son saka glasses kuma yana mata kyau”

“That’s because of her illness bata gani sai da gilashi”

“Whoo..what… Wow…”

Ya juya ya kalli part din Momy kamar zai ganta tsaye a gurin.

“Wow…”

“Wow… ”

He said for the third time.

“You make me like her more.. Gaskiya duk wanda ya samu yarinyar nan ya dace, and i think I’m the luckiest guy”

Namra ta kalleshi tana murmushi da ya zame mata kamar na dole ne.

“Hmmm”

“The true is i like your Sister so much Namra, kuma na zo nan ne saboda na yi magana da ita, amman na ga tana da kunya sosai ko tsoron mutane take ne i don’t know”

Namra ta sauke idonta kasa zuciyarta ta fara bugawa da mugun karfi, but she managing to wear her light smile on her face. Ya mike tsaye ya nufi gurin motarsa sai ta bishi da kallo har ya isa ya bude ya dauko abun da zai dauko ya kamo hanyar dawowa. Sai da ya kusa isowa sannan ta share hawayenta, not because of tana sonshi but because of disappointed, all her life ta dauka ita yake so ba Hurriya ba, yawan tambayarta Hurriya da yake ba saka ta kawo a ranta son Hurriya yake ba. A gurin da ya da ya tashi ya zauna ya mika mata ledar farko kamin ya mika mata ta biyu

“This one is for you, wannan kuma na Young Lady ne, last time i asked for her contact kika ce bata da waya, so na saka mata waya a ciki, ban sani ba ko za a barta ta yi amfani da ita, idan ma ba a barta ba, ba ki iya amfani da ita, ni dai abun da kawai nake bukata ta fahimci me yake tafe da ni, kuma ta tsaya ta saurareni, ta nan zamu fahimci juna da ita kamin iyaye su shigo ciki, idan Allah yayi, amman kna son ta san cewa ba da wasa nake ba, so ina ganin ke zaki min wannan kokari ki fahimtar da ita”

Ta amsa mishi da kai sannan ta mike tsaye rike da ledodin ta fara tafiya.

“Sai da safe…?”

Ya fada. Sai ta mayar masa ba tare da ta juyo ta kalleshi.

“Sai da safe”

Tun da ta saka gaba bata juyo ba har ta shige falon Momy. Tsaye ta yi da ledodin a falo not knowing what to say or do, Hurriya dake kokarin mikewa tsaye ta amsawa Momy dake fadawa Appanta yana nemanta a bangaren Hajiya Kaltume, ta kalleta ta yi murmushi irin murmushin nan na zolaya.

Namra ta kasa mayar mata da murmushi kuma ta kasa barin kofar falon da take tsaye, Momy ma dake tsaye stairs kallonta take kamar mai karantarta. Hurriya dake sanye da Hijab dinta ta nufi kofar falon ta bude ta fita ba damar ta tambayi yayarta me ke faruwa saboda Momy tana stairs tana kallonsu. Sai da ta fita daga bangaren Momy sannan hankalinta ya koma gurin kiran da Appa yake mata, tana ta tunanin laifin me ta yi?

“Hurriya…”

Ta juyo ta sauri ta kalli bakuwar motar dake fake kusa da motocin da suke bangaren Hajiya Kaltume.

“Na’am”

Ta amsa ba dan ta fa mai kiranta ba, sai Khairy da ta gani tsaye ta daure fuska ta rumgume hannayenta kamar an mata dole ta tsaya a gurin. Fadeel ya bude motar ya fito ya tsaya kusa da Khairy, Hurriya a ganinsa ta matsa ta gaisheshi.

“Barka da dare”

“Sannu Hurriya, ya kike?”

“Lafiya Kalau”

“Dan samo min ruwa ciki na sha”

Ta kalli Khairy kamar ta ce wani abu sai kuma ta ji ba zata iya ba, ta juya ta nufi bangaren Hajiya Kaltume ta shiga, babu kowa falon dan haka ta wuce Kitchen kai tsaye ta dauko ruwa da cup ta dawo ta mika masa da hannu biyu. Ruwa ya fara karba ya bude sannan ya ta rika masa cup din ya zuba ruwan ya ya mika mata da dayan hannunta ya karbi ruwan ya sha ya mika mata Empty cup.

‘Dama ace… Ke ce…, da raina ba zai ba ce ba, kuma zuciya ba zata ki yarda ba’

A ransa yake maganar yana binta da kallo bayan ta isa kofar falon surukarsa Hajiya Kaltume. A dinning ta aje cup din da bottle water ta nufi upstairs gabanta na faduwa domin yanzu ta san abu ne mai wahala Appa ya kirata akan wani abun alheri balle kuma a bangaren Hajiya Kaltume, waya sani ko wani sherin suka kulla mata. Cikin tsoro da fargaba ta tura kofar dakin ta shiga.
After Hurriya ta wuce, Fadeel ya sauke ajiyar zuciya ya kalli Khairy dake tsaye kamar an sassaka itace ya ce

“Ni zan koma”

“Toh a gaishe da gida”

Ta fara tafiya sai ya tsayar da ita, ya bude Motarsa ya dauko leda ya mika mata.

“Thank You”

Ta furta sannan ta wuce ta yi gaba, shi kuma ya shuga motarsa ya zauna, har sai da ta shige ciki sannan ya yi ma motar key ya juya. Har ya isa gidan Hajiya Fatee be daina tunanin yadda za’ayi su yi rayuwa haka da Khairy ba tun a waje balle kuma ace ya aureta, tun ba yau ba ya lura ita ma bata ra’ayinsa kamar yadda baya ra’ayinta. Domin wannan ne zuwa na biyar da yayi a gurinta idan suka gaisa baya sake cewa komai ko da ya gwada ma sai ya ji baya iyawa ita ma kuma bata cewa kuma bata sakewa, haka za su yi ta zama kamar wasu hotuna. Be kashe motar ba ya fita domin ba dadewa yake son yi a gidan ba so kawai yake yayi magana da Hajiyarsa. One step forward a falon Hajiya Fatee yayi arba da bako da ya fito daga dakinta sanye da shadda ruwan kasa, kana ganinsa ka ga bakauye, and instead of ya karasa fitowar sai ya juya da sauri ya koma cikin dakin na Hajiya. Fadeel yayi tsaye a falon yana kallon kofar dakinta with curious face, sai ga Hajiya Fatee ta fito tana ganin Fadeel ne ta saki fuska.

“Ashe ma Fadeel ne, yaya Malam fito ai danka ne”

Fadeel dai kallonta kawai yake.

“Waye wannan?”

“Kawuka ne na kauye, zauna sai ya fito ku gaisawa, yau ya zo nan zai kwana yanzu haka ma zancenka muke sai gashi ka zo, Yaya Malam fito mana ku gaisa da Fadeel”

Fadeel ya zauna yana kallon kofar dakin da Yaya Malam ya ki fitowa.

 

_____________________

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected