Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Cire gilashin idonki”
Cikin wata muryar data fi kama da shagwaba da kuka ta ce
“Idan na cire hudu zan gani, bana gani komai sai da shi”
Kansa ya daga sama, yana addu’a a zuciya, na neman Allah ya kara masa hakuri da juriyar iya controlling kansa, domin babu abun da ya tsana a duniyar nan kamar musu. Hannunta ta kai ta cire gilashin ganin kamar zata bata masa rai a rashin aikata hakan, bayan kuma Momy ta gargadeta, a take kuwa ta ganin komai da kyau hudun da take tsoro ya mamaye idonta, da can tana ganin dishe-dishe idan ta cire gilashin sai dai bayan tafiyar da dan’uwanta daya tilo yayi ya barta sai idanuwan suka kara lalacewa saboda kukan da ta sha, da kunnuwanta take auna sautin takunsa har kwakwalwarta ta sanar mata yana tsaye a gabanta. Tsakiyar cikin kwayar idonta yake kallo, ya sani ko da zai saka wuka ya barka cikinta, ko ya dora mata bindigar da take tsoro a kai ko yayi mata dariya ba zata shaidar abun da ta gani ba, domin ita ta rasa wannan ni’imar. Kansa ya sauke kasa ya busar da iska bakinsa a hankali.
“Alhamdulillah”
Ya furta da nuryar da shi kadai sai muhallinsa za su ji, domin shi ya samu abun da Hurriya ta rasa, daman kuma hausawa sun ce mutum dan tara ne be cika goma ba, Allah ya mata gomai ya rage da ido, shi ne kadai tawaya a gurinta. Kamar an kunna wuta haka jijiyoyin idanuwanta suka sanar da kwakwalwarta dake raba sako, ta karbi sakon hoton fuskar Captain dake tsaye a gabanta hannayensa kuma suka zagaye tsakanin dama da hagu na kyakkyawar fuskarta. Dauke hannunsa yayi bayan ya saka mata gilashin sannan ya karbi na hannunta a lokacin da hawaye suka sauko a idonta irin saukowar da wanda yayi arba da su a fuskarta zai tausaya mata. Ya nade gilashin ya dora a kan teburinsa ba tare da ya kalli hawayen da suka zubo mata ba.
“Direba yana waje yana jiranki”
Daga haka be kara cewa komai ba ya fice daga office din, gafen hijabinta ta saka ta share hawayenta, sannan ta nufi gilashinta ta dauka ta cire wanda ya saka mata ta maida nata sannan ta nufi kofar ta bude. Taku daya biyu kamin ta yi na uku wanda ya kawo ta ya nuna mata hanyar da za su ba, ba wanda suka zo dazun ba. Ba musu ta bi bayansa har suka isa gurin motar ya bude mata ta shiga ta zauna, shi kuma ya shiga mazaunin tuki yayi ma motar key, amman shiru shiru ta ji yaja motar sun kama hanya ba, bata ankaro ba aka bude back seat inda take zaune, Captain ne ya shigo cikin motar ya zauna, tana kallonsa ta yi saurin maida idonta kasa, sai ya kai hannu ya dago fuskarta ya cire gilashin idonta ya saka masa nasan data cire ta aje masa a office, sannan ya bude motar ya fita da nata ya rufe motar.
Damdamdam.. Ya buga bayan motar sai sojan yaja motar suka fara tafiya.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
Sai da suka wuce sannan ya dawo office dinsa, yana shiga ya aje gilashin na Hurriya a saman teburinsa ya zagaya ya zauna ya cigaba da aikin da yake. Few minutes Namra ta kira wayarsa dake gaban teburin sai ya amsa ta bluetooth din dake kunnensa yana duba wasu takardun.
“Ni fa na zagaye garin nan kaf duk inda nake saka ran samu wannan turaren Kapter Bokur Perfume ance min babu shi, wasu sunce sai Abuja da Kaduna ake samunsa ko Kano, wasu ma cewa suke ba su sanshi ba”
Ya dago daga aikin da yake yana murmushi ya jingina da kujerar da yake zaune yana lilo, shi kanshi daman ya san ba za a samu turare ba domin abun da babu ne be ya fada mata, shi ya hada sunan turare and ya san babu turaren dake da exiting mai irin sunan.
“Okay, na baki zabi ki zabo min turare mai kamshi”
“Aa ka fada dai, kar sai na dauko maka turare ka zo kana min fada ko ka ce mai warin albasa ne, kasan wata rana ba a maka daidai, garin gwaninta sai a bata maka rai”
“Ssi ka ce ni nafi kowa muguwar zuciyar? Please select ina jiranki”
“Toh”
Ta kashe wayar, sai ya juyo kansa a hankali ya kalli gurin da Hurriya ta zauna, rabin abincin da ta zuba a duk a kasa yake garin sauri ta zuba kuma ta ci.
“Mtscheeeeee”
Yaja tsaki ya tsani guri da datti ko kadan ne balle kuma na abinci, telephone dinsa yayi using ya kira aka shigo aka gyara gurin aka maida komai gafe daya, bayan kamar awa daya Namra ta kira sai ya fada mata inda zata zo ta same shi, a lokacin da ta iso gurin ita kanta sai ta tsoro ya kama ta even though ta taba zuwa amman yadda aka gyara gurin aka canja komai da tsaurara tsaro ya fi na da, arzikinta daya ya aiko aka shiga da ita har ciki. Tana shigowa Office din ya dauke hannayensa daga aikin da yake yana murmushi.
“Allah yasa kin zabo mai kamshi”
“I try my best na ga na samu mai kamshi kuma mai dadi, shiyasa na siyo kala biyar ba daya ba”
Ta matso kusa da teburin ta dora bag din da turaren yake ciki ta fara cirowa tana nuna masa. Ba laifi duka suna da dadi kuma duka na maza ne, amman babu kalar nasa a ciki, haka yayi mata godiya ya karba ya aje, a lokacin da take kokarin dauke idonta daga teburin idanuwan nata suka yi arba da gilashin Hurriya dake kan teburin a take ta kai hannu ta dauka tana dubawa.
“Kamar gilashin Hurriya”
“Nata ne”
Ya amsa mata kai tsaye ba tare da tunanin komai ba.
Ta juya ta karewa ko’ina na office din kallo sai ta dora hasashenta akan abinci ta kawo masa saboda kulolin Momy da ta gani.
“Abinci ta kawo”
Ashe kuwa ta yi hasashenta daidaita, sai dai wani abun ne ya tsaya mata a rai da ta kasa hadewa har sai da ta tambaya.
“Me ya kawo gilashinta a nan?”
“Sato shi na yi kin san ni barawo ni”
Ta dan yi murmushi.
“Ni ban ce ba, na san bata gani sai da gilashin ne shiyasa”
“Na bata wani, ki zauna mana”
Ta zauna tana jin numashinta kamar zai shake zuciyarta na bugawa da mugun karfi.
“Kuma ta karba?”
“Da na yi mata ta karfi ba, kin san kanwar nan taki akwai musu da kafiya, amman kuma tana samun sa’a na duk fushin nan nawa na kanyi kokarin controlling kaina na daga mata kafa saboda kawai lalaurar da take tare da ita”
Yana aikin yana amsa nata da babu alamar wasa ko second thought a tare da shi.
“Ka taba bata wani abu kamin yau ta bata karba ba?”