VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Idan ya fita ma babu inda zai je, already yayi received email daga gurin aikinsu sun aminta sun ba shi sati biyu ya huta, to me zai fita yayi a waje?”

“Namiji ne shi fa, yana da abokai yana da guraren zuwa da yawa yarinyar nan ma tun da aka daura aurensu ba ki barshi yaje ya ganta ba, Turai duk wanda zai so ďanki yana bayanki ne, domin ke kika haife shi ke ya kamata ace kin fishi son abun da yake so, ba shi kanwa ko yayar da zai ti shawara da ita akan Matsalar rayuwarsa ke ce uwa da ke zai yi shawara a komai, yanzu kuma kin juya masa baya kika kokarin cilasta masa ya zaba tsakanin rayuwa da mutuwa”

“Hajiya abun da yarinyar nan ta yi yayi tsauri da yawa, ko da kuma bata aikata ba ni bana sonta bata cikin irin jerin matan da nake son Captain”

“Saboda dake za’a daura musu aure ko ba da Captain kuma ke zaki zauna da su ba Captain ba, ko a gidan karuwai ya dauko ta tun da har ya nuna yana sonta ya kamata ki so ta kema, balle kuma har igiyar aure ta shiga tsakaninsu ai zance ya kare, tarewar ki a nan ba zai hana Jamal ya gana da matarsa ko ta tare a gidansa ba, na san duk saboda shi ne kika aminta ki bi mijinki”

Ammy ta bata fuska sosai tana jin ta wani bangaren kamar bata kyautawa danta ba, sai dai ita ma kuma ba su kyauta mata ba, sam bata son Hurriya a matsayin suruka.

“Ba gori nake miki ba, amman lokacin da Aliyu ya gabatar mana ke a matsayin matar da zai aura, ba mu ce masa fa wanda muke so, sai kuma karba muna murna da addu’ar alheri, mu dai muradin mu ya auri wanda yake so ba wanda mu muke so ba, so da yawa mu kan ki abu ya zame mana alheri, kuma mu so abu ya zame mana sheri”

‘Gorin dai kike min Hajiya’

Ta fada a ransa a zahiri kuma sai ta mike tsaye ta dauki hijabinta dake gefen kujera ta saka ta fice daga falon. Sama da haura zuwa dakin da Captain yake, tana tura kofar dakin ta ji karar unkurin aman da yake daga bandakin dake bude, tsantsar soyayya da kulawa irin na uwa sai ta karasa gurin da sauri hankalinta a tashe.

“Da gaske baka da lafiya ashe”

Ta taba wuyansa zuwa kansa ta ji shi da zafi sosai, da kanta ta kunna lap ta wanke masa baki kamar wani karamin yaro.

“Mu je asibiti yanzu”

“Zan iya kira likita ya zo gida ya duba ni”

“Aa asibiti zamu tafi”

Ta cikin tsananin razani da tsoron kar wani abu ya samu danta. Sakinsa ta yi ta fice daga bandaki da sauri. Tawul ya dauka ya goge fuskarsa idonsa har wani ja suka yi alamar jikinsa ya saki saboda Fever, haka ya fito bandakin yana jin aman kamar be gama yi ba, kofar bandakin ya rike yana jin yawun bakinsa na tsinkewa. Sai ga Ammy ta shigo tare da Momy Ikilima

“Mu tafi ga direba can a waje”

“Ammy ba wani ciwo ba ne da zaka daga hankalinki ba”

“Ban taba baka umarni ka aikata a take ba tare da ka yi min musu ba, haka last time na ce maka zamu tafi England a duba lafiyarka baka yarda”

Ammy kamar zata fashe da kuka take maganar. Ganin haka ya saka shi nufar gurin da ya aje wayarsa ya nufi wayar ya dauka.

“Mu tafi”

Gaba ta saka shi, kamar wanda zai gudu sannan ta bi bayansa ita da kanwar mijin nata.

“Zan iya tuki ba ni key”

Ya mikama Direban hannu, direban ya kalli Ammy. Sai ta girgiza masa kai.

“Ka bari ya kai mu ina zaka iya tuki yadda jikinka yake da zafi nan”

“Ammy ciwon nan be kai yadda kike tunani ba, zan iya tukin nan da kaina”

Ya rufe baki yana karkata dubansa ga motar Salim da ya faka kusa da wata motar gidan. Captain ya bude motar zai shiga Salim yayi hanzarin bude tasa motar ya fito.

“Captain…”

Be amsa shi ba kuma be fasa shiga motar ba. Ammy ta kalli Salim din ta kalli ďanta.

“Salim ne”

“Na san shi ne Ammy mu tafi”

Salim na isowa gurin ya gaishe da Ammy da yar kunyarsa kunshe a aljihu.

“Lafiya Kalau Salim”

“Fita zaku yi?”

“Eh Captain za mu kai asibiti”

“Ba shi da lafiya ne?”

“Eh”

Salim ya kalli Captain din da baya son kallon gurin da Salim din yake tsaye ya mika masa hannu.

“Hi”

Captain ya kalli hannunsa ya kalli fuskarsa, sai ya amsa masa ba tare da ya mika masa hannun ba.

“Hi”

“Come on mu bar abun da ya faru ya wuce mana, ba yara ba ne mu, mun samu rashin fahimta kuma mun hau dokin zuciya, amman ba zan bari wannan abun ya lalata alakarmu ba, we’re friends for more than 15yrs now wannan dan karamin abun ba zai bata alakarmu ba, na san na yi ba daidai ba a wani gurin kai ma kuma ka zafafa I’m sorry”

Salim ya sake mika masa hannunsa a karo na biyu, sai dai wannan karon na neman kawarda fadan dake tsakaninsu ne, ba irin na dazun ba da yake na gaisuwa. Wannan karon ma sai da Captain ya dade yana kallonsa hannunsa sannan ya mika masa nashi hannun ba tare da yace komai ba. Ammy ta yi murmushi.

“Ko ku fa, amman ace mace zata shiga tsakaninku kamar ba maza ba? Ban jidadin abun da ya faru ba kuma daman ina da kudirin na shirya tsakaninku”

Still Captain be ce komai ba, Ammy ta bude baya ta shiga tare da Momy Ikilima dake yaba yadda Salim ya fi karfin shaidan ya kawar da girma kai ya kawo kansa. Direban ya ja motarsu zuwa asibiti Salim kuma ya shiga motarsa ya bi bayansu. Sai da aka fara diban jininsa aka auna bayan likitan yayi masa tambayoyi sannan ya ba shi gado domin har yanzu akwai gajiya a tare da shi kuma yanayin jikinsa ya tsananta sosai. A take aka saka masa drip Ammy ta tare a dakin tareda Salim hankalinta a tashe ta fita dakin tana sanar da Daddy. Momy Ikilima kuma ta koma gida dare da direba domin sanar musu halin da ake ciki da kuma dauko wasu abubuwa da ake bukata. Sai dakin ya zama daga Salim sai Captain da idonsa yake rufe hannunsa kuma yake sanye da cannula.

“I’m so sorry akan abun da ya faru, gaskiya ta bayyana yanzu kuma za a yadawa duniya cewar Hurriya bata aikata ba”

“Matsalata da kai ba akan Hurriya ta aikata ko bata aikata ba ne, so please sunanta ya fita daga bakinka, matsalar sa muka samu saboda na karya hannun Adam ne so mu yi magana akan haka kawai”

Salim yayi ya dan tabe baki.

“That’s right… Adam yayi abun da kake bukata an turawa mahaifinka video kai ma kuma na turo maka ka duba whatsapp dinka”

Captain ya bude idonsa ya kai hannunsa na hagu ya ciro wayarsa ya bude whatsapp dinsa, suna ganin Salim ya fara budewa kamin ya sauke video kiran Daddy ya shigo wayarsa ta whatsapp video.

“Daddy”

“Hi Jamal… Yanzu Ammynka take fada an baka gado a asibiti, haka ne… ”

“Eh amman da sauki ba yadda take daga hankalinta ba ne…”

Salim ya juya ya fice daga dakin, yana rufe kofar dakin Ammy na kawowa bakin kofar dakin, ganin Salim sai ta fasa shiga ciki.

“Ina son magana da kai Salim”

“Okay Ammy, zamu iya yi a nan ko sai mun tsada”

“Idan muka matsa zai fi”

Ya fara takawa ita ma ta taka sai suka jera suna tafiya.

“Amman ina son na sake yaba maka ne akan kokarin da ka y na kawar da komai a ranka, kuma ka bawa Captain hakuri duk da kasancewar ta wani bangaren ka fi shi gaskiya, na jidadin haka domin idan baka yi ba na san Captain ba zai taba iya aikata abun da ka aikata ba, ka san halin abokinka”

Salim yayi murmushi.

“Nasan halin kayana Ammy ba sai kin fada min ba, shiyasa ai na bada hakurin da kaina, ni kuma na fahimci ban kyauta ba ta wani bangaren and be kamata na bar yarinyar kamar Hurriya ta raba ni da Captain”

“Good na jidadin dawowarka sosai, daman ina neman wanda zai taya ni fadan nan domin ni kadai nake yakin nan a gidana, Engr yana goyon bayan Captain yan’uwansa kuma basa son fada masa gaskiya saboda Engr, yau ma Hajiya Nene fada ta yi min tana ganin kamar kishi nake da yarinyar nan ni kuma ba kishi nake da ita ba i just can’t find any reason da zai saka na so ta, i know da cousin dinka aka aikata abun nan amman ko da ba gaskiya ba ne ai wannan abun ba zai shafe a idon duniya ba”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected