Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
”Nii kuma ba zan iya tunkararta kai tsaye ba, saboda ina tsoron kai ta fada a gidansu, gashi ban samu yadda zan yi magana da Hurriya ba, a lokacin ne na gane kamar wayo Khairy ta yi min, sai fadan ya koma tsakaninmu, na kasa daga nata kafa saboda zan bar kasa na tafi gurin masters sanadin haka mu ka yi fada, washe garin ranar da muka yi fadan na kirata na bata hakuri muka hadu a wani gurin and…. I… Rape her there…. ”
Captain be san lokacin da ya bude baki ba.
“Wait… Wa ka yi raping?”
“Khairy saboda ta ci kudina kuma ta kasa ba ni abun da nake so, sai fadan min take na yi amfani da hotunan, ni kuma hotunan ba su da amfani a gurina saboda ban samu damar kebewa da Hurriya ba, kuma ban san ya hakan zai faru ba”
Captain ya mike tsaye yana jinjina lamarin Ubangiji, bahaushe ya ce wanda Allah ke yi ma fada baya fada, all this plan akan Hurriya amman Allah ya kareta sherin da suka kulla be same ta ba.
“Wacece Khairy ma?”
Ya sake tambaya domin tabbatarwa.
“Yayarta ce, mahaifinsu daya a gurin Birthday Khairy muka hadu da Hurriya, saboda Khairy ce friend dita”
“To me yasa ka hadawa hotunan? Bayan ka samu abun da kake so a gurin Khairy? Akan me zaka cutar da Hurriya meye nata a ciki?”
“Ba ni na yada hotunan ba Wallahi, ban san waye ya yada ba, wata kila Khairy ce saboda ta ji haushi abun da muka yi mata, ta ce min sai ta dauki fansa, wata kila ita da yada hotunan”
“Me yasa ka amsa cewar tare kake da Hurriya? Why? Idan ma an yada me ye ribarka na amsawa”
Ya kasa magana sai wayyo wayyo yake yana kuka. Captain ya kama hannun ya murza.
“Ba tambayarka nake ba?”
“Wayyo….wayyo…. Wayyoooo….. Na yi hakan ne saboda kar nawa sunan na bace ni kadai, dan Allah ka sa a maida ni gida dan Allah”
“Za a maid kai, na samu abun da nake so ai ka saukakawa kanka, amman still zaka fuskanci hukunci…”
Captain ya tsayar da video ya mike tsaye ya fice daga dakin da Adam ke ta ihu yana neman ceto.
“Ku bar shi a nan DSS za su zo su dauke shi, ku babu hannunku a ciki, ko a office kar wanda ya amsa cewar kun je dauko yaron nan”
“Yes Sir”
Ya sara masa, sauran soldera din da suke waje mota biyu duka suka sara masa, sannan ya bude masa motarsa ya shiga ya rufe motar ya sake sara masa. Captain ya cire plane mode din ya shiga contact dinsa ya nemo wata number ya kira, after sun gaisa ya ce
“Mubarrak akwai wata yarinya da aka batawa suna, kuma abun ne da ku ya kamata ace kun yi Handel a yanzu, Lawyer na zai shigar da kara a gurinku cikin dare nan, please ina son ka tashi yaranka a location din da zan turo maka yanzu su dauki yaron, already na saka an dauko shi daga asibiti na san be kamata na yi haka ba amman na kasa hakuri ne”
“Me yaron ya aikata….”
Captain ya labarwa abokinsa abun da ya faru a takaice, sannan ya dora da cewar.
“Already babansa ya kai case din kotu saboda na karya masa hannu, na zubar masa da hakora so now i want you to cover me up…”
“Karka damu I know my job, ka turo Lawyer ka ya saka kara a gurin mu yanzu nan”
“Thank you”
Yana sauke wayar ya kira Lawyer sa Barrister Hauwa Zamau. Yana tukin motar yana fada mata abun da ya faru har ya isa gida.
“To a matsayin wa zamu shigar da karar?”
Yayi shiru yana kallon harabar gidan kakan nasa.
“A matsayin wanda zata aura, ina neman hakkin cin zafinta da yayi, abu ne kika sani duk wanda ya yi ta’adi ko kuma ya buga hotuna ko bidiyon tsiraici na mutum a yanar gizo ba tare da izinin mutum ba, to lallai irin wannan mutumin ya aikata laifi, and can be punished for Cyberstalking under S.24 of Cybercrimes (Prohibition, Prevention, etc.) Act 2015 of Nigeria or any law being in force in Nigeria..”
“Amman a yadda ka fada min ya amsa maka cewar ba shi ya yada hotunan ba”
“Wannan zai zo daga baya, a iya yanzu shi kadai muka sani da hotunan dan haka shi muke zargi, shiyasa muka shigar da karr gurin DSS saboda fadada bincike”
“Good point, i hope iyayenta ba za su ba mu matsala ba”
“I will fix that later… Ki aiko min da account number dinki yanzu nan”
“An gama ranka ya dade”
Ya katse kiran ya sauke wayarsa. Gallary dinsa ya shiga ya kama hoton Hurriya da ya dauka a dakinta ya duba.
“Mai tsada… Kin rike mutumcinki gashi abun da suke shirya miki ya koma kansu, ashe kaddarar mai yawa ce Allah ya takaita a haka, pretty girl with golden Heart…”
Magana yake da hotonta dake cikin wayar yana murmushi kamar ance masa tana saurarensa, kaunarta ta karu a zuciyarsa, a yanzu ya kara tabbatarwa ita din tabbas mai tsada ce…
Sai da ya turawa Barrister alert mai kauri tare da Nafi’u sannan ya fito motar, sai a lokacin ya lura bakin motoci dake gidan, kamin yayi wani motsi kira ya shigo wayarsa wannan karon Daddysa ne ya kira, ya amsa kiran da girmama da ladabi.
“Hello Daddy”
“Jamal kai ka aika aka dauki yaron nan daga asibiti?”
“Wane yaro?”
“Dan gidan Bashir Sarauta”
“Cewa suka yi na dauka?”
“Ka amsa min kawai ka dauke shi ko aa? Me ya fitar da gidan?”
“Na dauke shi, amman na yi covering case din yana hannun DSS yanzu”
“Why? Fadan nan ba naka ne kai kadai ba so ka cire hannunka a ciki ka bar ni da mahaifin yaron nan, ka zo gida yanzu nan”
Daddy ya katse wayar a take. Captain ya karasa ya shiga cikin falon, ga mamakinsa sai ya samu Salim a falon tare da wasu mata biyu, sau daya ya kalli gurin da Salim yakw zaune ya dauke kai zai wuce gurin Ammynsa dake tsaye tana kallonsa da waya a hannunta.
“Jamal…. Ina Adam…?”
Captain ya juyo ya kalleshi.
“Jamal….? How dare you call your boss like that?”
“Ba a office muke ba, baka da wannan ikon a nan, ina Adam?”
“Na dafa shi an cinye ka san ni maye ne”
“Kai ka aika da boys aka dauko yaron nan ina ka kai shi?”
“Taya ka san ni na aika aka dauko shi? Ka gan ni a gurin ne?”
“Mahaifiyarsa ta fada min yadda komai ya faru? Taya zaka aikata hakan Jamal? Ina hankalinka ya tafi?”
Captain ya taka ta isa inda yake tsaye, cikin wani irin isa da izza Captain ya ce.
“Bari na kira headquarter na fada musu Salim Sarauta ya shigo har cikin gidanmu ba tare da uniform ba, yana tukumar ogansa da sace wani wanda ban san da wanzuwarsa a kasar nan ba, kuma ka kira sunana kai tsaye with full of disrespectful, and you know yadda wannan abun zai taba aikinka”
Captain ya kara matsawa kusa da shi sosai.
“Ka san yadda Power take da karfi a Familymu, zan yi duk yadda zan iya na ga an cire uniform a jikinka, lastly ka san yadda bad ending yake karewa korarren ko da karami ne balle kai, and you know i can do it, so respect yourself….”
“YES SIR…”
Salim ya amsa masa dan dole yana kamewa guri daya, sannan ya hade yawu ya juya ya kalli matar da hankalinta yake a tashe ya ce.
“Mu tafi Anty Nabila”
“Mu tafi? Bayan ba mu san inda yaro yake ba? An zo an dauki yaro cikin asibitin yana cikin tsananin ciwo sannan ka ce min mu yafi? Mu koma mu yi me?”
Cikin kuka matar take magana, sai dayar dake gafenta ya amsa waya sannan ta kama hannunta
“Mu tafi Anty Nabila”
Sai da suka wuce sannan Salim ya kalli Captain ya juya ya fice daga falon cikin tsananin takaici.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.