Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Mahaifiyar Adam ya fashe da kuka domin a gurinsu yin abun da Captain ya bukata ma cin mutunci ne da kara zubewar kimarsu. Daddy ya mike tsaye ya kalli Captain
“Ina ganin shi kenan nan ai, idan sun zabi haka sai ku aiko mana da video idan kuma kotun kuka zaba duk daya ne, akwai uzurin da zan yi kamin na bar garin yau zan wuce Kaduna”
Captain ya mike tsaye sai suka fice tare da Daddy aka bar Alhaji Bashir Sarauta da matarsa da yan’uwansa da suka rako shi a falon.
“Adam ne ya ja mana wannan wulakanci, ni ban ga dalilin ma da zai sa a nemi janye shari’ar ba a bar shari’ar ba, da abar shi kotu ta koya masa hankali”
Cewar daya daga cikin kanen ubansa. Alhaji Bashir ya ce.
“Ba za’ayi haka ba, shi ma ai sai ya wahala kuma ko kotun muka je ba nasara zamu yi, tun da kudi za su zuba kuma su suke da gaskiya”
Mahaifiyarsa ta kalleshi.
“Yanzu kenan Alhaji dole Adam sai yayi haka? Babu wani abun da zaka iya yi? Shi Captain ba zai duba abotar dake tsakaninsa da Salim ba?”
“Kina kallo Salim din ya tashi ya fice be ma tsaya aka yi magana da sho ba, wata kila sun samu matsala da Captain din akan haka, kuma shi Adam ai ya fada mana cewar Captain ya masa video idan ma ba mu saka ya bada hakurin ba zai iya sakin video kuma ga shari’a a kotu, yara ne idan za su yi abu basa tunani, yadda Alhaji Turaki ya fice ya bar a falon nan ai kin san akwai abun da yake zuciyarsu da jira kawai suke”
Cikin kuka Hajiyar ta mike tsaye ta fice daga falon sannan sauran ma suka mike tsaye.
“Alhaji ka tashi mu tafi, babu amfanin zama ai domin ba saurarenmu za su yi ba”
Alhaji Bashir ya mike tsaye.
“Zan samu mahaifinta na yi magana da shi, zamu samu mafita a can”
Cikin rashin jindadi suka fice daga falon. Dayan falon Daddy ya shigo tare da dansa sai suka samu Ammy zaune tana jiransu, fuskarta a hade kamar ba ita ba.
“Ina tunanin ya kamata kaje ka samu mahaifinta ku yi magana, domin za su iya bi ta can su siye shi da kalamai ya yafe musu, bayan kuma ba su cancanci hakan ba matukar ba su aikata abun da ka umarce su ba”
Kamin su zauna Daddy yake fadar haka, Captain ya rausayar da kai
“Okay Daddy”
“Daga yin aure matsalar har ta tattara ta dawo mana a gida? Mu miye na mu da za su zo mana a nan?”
“Saboda danki ne ya shigar da karar kuma mijinta ne a yanzu, sannan lalama suke bi suna neman yadda za a kashe wutar ne cikin ruwan sanyi”
“Idan wani abu ne da ya shafi Hurriya ko mahaifinta kai ya kamata ka yi magana da shi kai tsaye, ba Captain ba yaron da lafiya ma bata wadace shi ba, tare da shi zamu tafi kaduna a yau….”
Captain ya kalli Ammy da sauri, Daddy kuma yayi murmushi ya ciro wayarsa yana lasawa.
“Kin kawo shawara mai kyau, haka ya kamata yi tafiyarka Jamal zan yi magana da mahaifinta da kaina”
Ya amsa masa da kai sannan ya juya ya fice daga falon.
“Ba zan tafi Kaduna na bar ďana ba, ko dai na fasa tafiyar ko kuma ka fada masa ya shirya mu tafi, kuma a fadawa iyayen Hurriya tun da an daura aure a ba mu amaryarmu zata tare”
“Wannan hurumin iyayenta ne ba na mu ba, ki je ki same su ku daidaita idan sun saka ranar da ta yi miki shi ke nan, amman dai ki sani duk wani abun na zubar da mutunci ba zan bari ya faru ba”
Yana kaiwa nan ya mike tsaye ya shige bedroom ya barta a falon zaune kunshe da bakincikinta.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
HAJIYA KALTUME POV.
“Wai ni kam ya ma sunan addu’ar nan da ake idan za a bar gida, wanda aka ce idan ka karanta babu abun da zai same ka har ka je ka dawo?”
Hajiya Fatee ta yi shiru alamar nazari tana kokarin tunanin addu’ar amman ta kasa.
“Akwai dai Bismillah a ciki, Bismilah da wani abu a ciki ni ma fa na manta addu’a”
“Kin ga da kin rike ai da mun karanta yanzu, mu tafi cikin kwanciyar hankali”
“Duk abun da za’ayi fa ba zan samu kwanciyar hankali ba, domin ba mu da shi a yanzu, tafiyar nan dai ta zame mana dole ne kawai, domin ni ma ina son na san lafiyar Malam”
“To kin gani, dole a haka zamu daure mu tafi, Allah dai ya kaimu lafiya, amman tashin hankali da nake ciki a yanzu ai ya fi na yan kidnapping”
“Babu wanda ya di wani, fatan dai Allah ya kaimu lafiya”
Cikin tsoro suka shiga motar ta suka dauki shatarta tun daga tasha direban ya zo gidan Hajiya Fatee ya dauke su. Hajiya Fatee ce mai rike carbi tana ja tana leka lake waje, Hajiya Kaltume kuma shiru take sai da suka iss cikin garin sannan hankalinsu ya kwananta Hajiya Fatee ce ta yi ta nuna ma direban hanyar gidan Malam be sauke su ko’ina ba sai a kofar gidan da yayi baki kirin har wani bangare na ginin ya zube. Hajiya Kaltume ta kalli kawarta.
“Anya akwai lafiya a gidan nan kuwa?”
“Ina lafiya kina kallon gida kamar an yi gobara”
“Ni ma abun da ya daure min kai kenan, amman dai bari mu shiga cikin gidan mu ji”
Hajiya Kaltume ta zagoyo ta gefen da Hajiya Fatee take suka jera suka nufi gidan da kusan ma za’a iya cewa ya zama kango.
“Ke yaushe rabonki da nan?”
“Wai ni? Ai tun zuwan da muka yi tare da ke van sake zuwa ba, to me zai kawo ni irin wannan gurin ma sai dole”
“Yanzu wai da gaske kike filaye da gonakin da kika ce mutumen nan ya siya miki duk baki ga ko daya ba?”
“Ai yarda ce ta kawo haka, ni na yarda da ko ban zo na duba ba na san ba zai cuceni ba”
A bakin kofar gidan da aka zagaye da ƙaya suka tsaya suna kallon yadda gaba daya gidan yake kone kuma babu alamar ana rayuwa a cikinsa.
“Hajiya wannan gidan da kike gani gobara aka yi, kuma kina kallon gidan ya zan kango babu kowa a ciki”
“Amman Hajiya Fatee ni da ke a nan muka san matan malam suna rayuwa?”
“Bari mu tambaya, ba mamaki ma ace ya tashi tun da yanzu linkafa ta yi gaba”
Juyowa suka yi suka fito daga zauren gidan suka yar tafiya sannan suka isa gida daman makotansa suka yi sallama. Hajiya Fatee ta shiga ciki Kaltume kuma ta tsaya daga waje tana waige waige kamar wanda bata yarda da garin ba.
“Sannu ina kwananku?”
“Sannu dai muna lafiya”
“Alhamdulillah dan Allah Malam muke tambaya ko ya tashi a nan ne shi da Iyalansa? Mun shiga gidan babu kowa a ciki na ga kamar ma ginin ya fadi”