VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“To waya kira shi?”

“Ni amman na ce masa ya zo ya dauke ni ne kawai saboda wannan saurayin ya takura min kuma ba ni da wanda zai kai ni gida, amman WallahI ban ce ya shiga ciki ba”

“To ai ke kika yi kuskuren Hurriya kema kin san dole zai shiga ai, kuma yanzu babu mai wanke ki a gurin Hajiya”

“Ba Hajiya kadai nake tsoro ba, har da Yaya Khairi na san ni zata dorawa laifin”

“To kije ki ba su hakuri mana”

“Zan yi haka”

Ta fada cikin yanayin damuwa wasu hawayen na kara cika idonta. Namra ta fice tare da ja mata kofa. Hurriya ta kai hannu ta taba hancinta kamin ta dago ta sake juyawa top side view ta rumgume hannayenta.

 

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
Misalin tara da rabi Hurriya na zaune dakinta ta ji an kwankwasa kofa, tana jin haka ta san wanda be saba shigowa dakin ba ne domin Momy ko Namra basa kwankwasa mata kofa balle kuma Miwan da Musib da basa gidan ma. Ta tashi da saurinta ta nufi kofar ta bude sai ta yi arba da Ruma.

“Appa na kiranki”

“Ni”

Ta nuna kanta, Ruma ta daga mata kai.

“Eh”

Ta juya ta bar kofar ta fara sauka kasa, Hurriya bata tsaya komai ba ta bi bayanta tana sanye da kayan bachi kanta sanye da hular saka. Ruma na gaba Hurriya na bayanta tana jin kamar ta tambaye ta me ya faru kuma dai bata tambaya ba. Cikin tsoro da fargaba ta shiga falon na Hajiya Kaltume gabanta na faduwa. Hankalinta be kara tashi ba sai da ta yi arba da fuskar mahaifinta dake hade babu annuri a tare da shi, bata yarda ta karasa cikin falon ba ta tsaya daga jikin kofa cike da ladabi ta ce

“Appa ga ni”

“Okay tasowa zan yi na iskoki can kenan? Ni zan same ki a inda kike na yi magana da ke ko?”

“Aa Appa ka yi hakuri dan Allah”

Ta taso ta karaso kusa da shi, ba duka take tsoro ba domin be taba dukanta ba, fadansa take tsoro tun daga lokacin da ya canja mata sai ya zame mata abun tsoro bata ma son zuwa kusa da shi sai da dalili domin ta lura baya bukatar ganinta.

“Appa gani”

Ta durkusa gabansa tana kallonsa ta cikin gilashin idonta, Yasir na tsaye gefen Hajiya Kaltume dake zaune kusa da Appa, Khairi kuma na zaune a dayar kujerar tana shafa man zafi.

“Miye wannan?”

Appa ya nuna mata video karin kudin da aka yi mata. Sai ta saka hannu biyu ta karba tana kallo jikinta na rawa kamar yadda bakinta ma yake rawa domin bata san me zata ce ba.

“Wace ce a nan?”

“Ni ce Appa”

Ta amsa da sauri.

“Waye wannan da yake miki liki”

“Ban san shi ba Appa Wallahi”

Tana rufe baki Hajiya Kaltume ta kai mata duka a bakin da mugun karfi.

“Baki san shi ba zai zo yana zuba miki dollars haka?”

Apoa ya kalli Hajiya cikin yanayi na rashin jindadin kai hannu da ta yi ta daki Hurriya.

“Ba sai kin dake ta ba, magana ma ta isa a yanzu shata nata line zan yi”

“Ai idan ba a dake ta ba, ba zata san Annabi ya faku ba, karya da munafurci babu kalar wanda bata iya ba, ka duba yadda ta zuga Yasir ya fasawa Khairi jiki”

Appa ya daka mata tsawa da ta saka ta fashe da kuka ta ja baya tana girgiza kai.

“Waye wannan mutumen na ce?”

“Ban san shi ba Appa Wallahi ni ma yau na fara ganinsa?”

“Karya take yi Wallahi Alhaji bata san shi ba”

Hajiya ta kai kafa ta halba mata wani shuri, kamin ta janye da sauri saboda ciwon da kafar take mata har yanzu.

“Karya take munafuka baki san shi ba zai zuba miki kudi haka kuma kina zaune gashi har sunanki ake fada”

Yasir dai yana tsaye sai kallo yake baya son yayi magana Hajiya Kaltume ta rufe shi da fada, bayan kuma ga wanda ya kamata a rufe da fada nan wato Khairi.

“Ku dai duk abun da zai zubar min da mutunci ko kima a idon duniya shi kuke kokarin aikatawa? Ko soyayya zaki yi me zaki yi da mashayi? Kaltume ta fada min yaron nan yayi kaurin suna gurin iskanci da shaye shaye”

Hurriya ta saka hannu ta rufe bakinta, ta san duk wani abu da zata fada ba zai wanke ta ba, ita kan da ta sani ma ba zata tafi bikin ba.

“Sannan kuma ka ja mata kunne akan munafurci abun da take ba shi da kyau, kina hada yan’uwa fada kina sa a ciya daya mutumci a cikin mutane”

Sai a lokacin Yasir ya saka baki.

“Ni ba ita ta fada min Khairi tana wani abu a gurin ba, daukarwa kawai naje yi sai kuma na yi decide na shiga ciki, kuma idan ma Hurriya tana da laifi to laifin Khairi ne, domin ita ta shirya biki kuma Appa da ka ga irin shigar da ta yi da irin mutanen da ta tara a gurin sai ranka ya bace”

Hajiya Kaltume ta watsa masa harara.

“Ita Khairi da ka raina ba, ita meye laifinta? Birthday kawai ta yi fa, kuma ina ce Hurriya ce silar kowa ya fara yin birthday a gidan nan amman ba ayi mata fada ba sai Khairi”

Appa ya mike tsaye.

“Ban shigo nan dan ku rufe ni da ka ce na ce ba, and Hurriya ina jan kunnenki idan wani abu makamancin wannan ya sake faruwa sai na baki mamaki”

Yana kaiwa nan ya fisge wayarsa da Hajiya Kaltume ta tura masa video ya fice daga falon. Hurriya ban da aikin kuka babu abun da take yi, ta rasa ta ina zata fara wanke kanta.

“Munafuka sahibar kuka, ki yi ta rerawa mutane kuka saboda a tausaya miki a kyale ki ko? To yanzu dai kin ji abun da Alhaji ya fada idan zaki kama kanki gurin yan iskan samarin nan ki kama, idan kuma ba zaki yi ba yi, ga ki ga guri duniya ce”

“Wallahi Hajiya ban san shi ba, ni ban taba ganinsa ba”

Ba dan Yasir na tsaye gurin ba da babu abun da zai hana Khairi saka baki, sai dai tana tsoron ta yi magana ya sake rufeta da duka. Dan haka ta ja bakinta ta yi shiru sai kallonsu take, Hajiya Kaltume kuma ta rufe Hurriya da fata ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, sai balbale Hurriya take da bala’i ta ko’ina kamar ita ce ta aikata abun da Khairi ta aikata. Sallama aka yi sai suka dago baga dayansu suka kalli kofar amman aka rasa wanda zai amsawa Rukayya sai Yasir dake kokarin sakin fuska.

“Rukayya”

“Na’am Yasir ya gd”

“Lafiya kalau”

Hurriyya ta tashi da sauri ta nufi kanwar mahaifiyarta ta rumgume ta da sauri tana kuka.

“Mama Rukayya kara da kika zo”

“Idan ta zo magani zata miki? Idan dai zaki canja hali ki canja domin hanyar da kika daukarwa kanki yanzu ba mai daurewa ba ce”

Hajiya Kaltume tana fada tana tabe baki, Rukayya da ke rumgume da Hurriya ta kalli Hajiya ta ce.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected