Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
.
@
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
6️⃣
The following week Appa ya aika mota dauko Hurriya, a lokacin ne hankalin Amma ya tashi sosai daman babu irin magiyar da bata yi ma Hajiya Binta ba a lokacin da ta zo mata da sakon cewar Appa zai aiko da mota a dauki Hurriya next week, Hajiya Binta ma ta yi iya kokarinta amman be saurareta ba, saboda ba zai iya tsabawa abun da Hajiya Kaltume take so a yanzu ba, ita kadai zata ba shi shawara ya dauka bayan ita baya sauraren kowa ciki har da mahaifiyarsa da kuma Momy da bata ma gane kansa yanzu, sai dai bata cika damuwa da al’amurransa ba domin ta bussinees dinta take da harka da manyan mutane. Son ta mallaki gida ko ta mallake Alhaji Haruna baya gabanta domin jin take kamar ma ta kusa gogawa da shi a arziki. Hurriya kamar zata shide haka aka fito da ita daga gidan ita kuka Amma kuka Gwaggo kuka Rukayya kuka tana rikon Amma amma na rike ta kamar wadanda za a raba rabuwa ta har abada. Ita dai bata son komawa gidan saboda babu dan’uwanta mai tare mata fada a cikin haka kuma babu mahaifiyarta, kuma a yadda ta fahimta ba zata sha da dadi kamar da ba a hannun Appa yanzu. Amma kuma tana jin kamar za a kara mata kewa ne domin babu Hamad a kusa da ita a yanzu Hurriyar take gani tana jin sanyi yanzu kuma za a dauke ta. Har aka iso gida da ita kuka take sosai kamar na mutuwa, gaba daya ta bi ta rike ce da direban yayi parking ta rasa ina zata shiga bangaren Hajiya Kaltume ko Momy gurin da dakinta yake a yanzu, ko kuma bangaren mahaifiyarta da babu kowa a cikin, kamar wata bakuwa haka ta rika kallon gidan.
“Hurriya”
Ta dago da sauri ta kalli Dattijon direban da ya kawo ta, jikinta na rawa.
“Ki yi hakuri ki yi da addu’a babu abun da yake daurewa”
Tana kokarin amsa masa da kai sai ta kasa, daman shi kam baki ba zata iya furta komai ba.
“Ina zaki je? Gurin Momy ko gurin Hajiya Kaltume?”
Sai kawai ta fashe masa da kuka.
“Ko kuma gurin Alhaji zaki je? Yana nan ciki daman yace ba zai fita ba sai kin dawo”
Ta daga kai da sauri, sai ya kama hannunta suka isa bangaren mahaifinta sai da suka isa daf da kofar falonsa sannan ya saki hannunta.
“Ki shiga ciki”
Ta daga masa kai, sai da ya wuce sannan ta kwankwasa kofar part din kamar wata bakuwa bayan ba haka ta saba ba, idan zata shiga bangaren Appanta sai dai ta tura ta shiga da murnarta tana rangada sallama. Sai da ta yi knocked sau uku sannan ta tura kofar falon ta shiga, sanyin ac ya fara yi mata maraba da zuwa, kaminnta juyo muryar mahaifinta a dayan falon da alama waya yake, babu komai a hannunta sai carbin Amma da ta dauko, tufafinta ma sai daga baya za a dauko mata ko kuma ta yi using wadanda suke gidan na bangaren Momy. Hawaye na sauko mata kamar ba gobe haka ta shiga karamin falon tana ta son ta bude baki ta yi sallama amman ta kasa. Appa na ganinta a take annurin dake fuskarsa ya gushe kamar wanda yayi arba da bakin maciji, a take ya yanke wayar da yake ya mike tsaye ya nufota yana fada.
“Ya aka yi? Kin dawo kina ta yi ma mutane kuka mutuwa aka yi? Ni ba dan Kaltume ta matsa ba ai sai ki zauna can a gurin uwar taki”
“Appa”
Ta furta tana kallonsa gilashin dake mata garkuwa na daf da faduwa. A madadin ya amsa sai yace waye bana son jin muryarsa ba ke ba, a take korata ya saka ta gaba.
“Muje can bangaren Nafisa tafi tafi”
Ta tsaya a gurin tana kallonsa kamar hoto har ya iso, ganin ba tafiya zata yi ba ya saka shi fisgar hannunta ya wuce gaba ya hanyota sai kallonsa take har suka isa cikin falon Momy ya sannan ya saki hannunta. Kamin ya ce komai Momy ta aje plate din doyar dake hannunta ta rafka salati.
“Haba Alhaji, ina laifi ka barwa Iyami yarinyar tana ganinta tana jin sanyi? Ni dai tsakani da Allah hankali ya fi kwanciya yarinyar ta zauna a gurin uwarta”
Ita ma kamar Appa na jiranta sai ya rufeta da fada.
“A nan nake son ta zauna, a nan zata zauna ke kanki gurin da na ga dama zaki zaun balle kuma ita da take yata, karki sake fada min abun da ya kamata na yi, ba shawararki nake nema ma”
Tabe baki ta yi bata sake cewa komai ba har ya fice, sannan ta ce
“Ni ma dan an rasa ya za’ayi da ni ne, na cika na make gurin kuma sai hakuri Wallahi, ni da zai maida Iyami ki koma can gurinta ya fi min kwanciyar hankali, ina zan iya da rikon yayan wasu yayan da idan suka girma suka samu arikin uwarsu za su nema”
Hurriya dai tana tsaye a gurin da Appa ya barta ta kasa matsawa ko’ina sai hawaye take. Mahaifinta ya canja mata, ta rasa dan’uwanta kuma ta rasa mahaifiyarta a kusa da ita.
“Lafiya kika tsaya nan kika zuba min ido? Mahaifinki ma baki da amfani a gurinsa yanzu balle kuma ni, wuce ki tafi dakinki tun da an kawo min kaya ya zan yi, Iyami ta haifa mana ta tafi ta bari”
Huriyya ta dauke kai da sauri ta fara tafiya, sai kuma Momy ta kirata.
“Hurriya”
Ta juyo a hankali ta kalleta ta kasa amsawa har lokacin hawaye take.
“Zo ki zauna yi hakuri kinji”
Hurriya ta dawo ta zauna saman kujerar dake dama da Momy.
“Gaskiya dai Alhaji ya ci amanarki Wallahi, ni ai ko da bala’i sai na karbi yayana, ko da yake Iyami ba zata iya ja da Alhaji ba, ta ina talauci zai ja da arziki, amman dai gaskiya be dace ya rabaki da Iyami yanzu ba, ai sai tunanin ya hade miki ga na dan’uwa ki kamu da hawan jini da kurciyarki, kai Kaltume bata da imani, haka fa ta raba Sapna da ubanta, Sapna bata isa ta tako garin nan ta ce zata zo gurin ubanta ba, tana can kauye cikin talauci shi kuma ya kyaleta… Hmmmm”
Ta mike tsaye tana kwalawa mai aikinta kira.
“Bilki”
Tsohuwar ta fito da gudu daga kitchen, daman haka take da yan aiki idan tana falo sai dai su boya a wani guri bata zama daki daya da su, idan har ka gansu a falo to tana dakinta ne ko kuma ta fita.
“Hajiya ga ni”
“A dauke plate din nan kuma ga yar Iyami nan idan zata ci abinci a zuba mata”
“Toh Hajiya”
Tsohuwar ta dauke plate din sannan ta kalli Hurriya dake zaune.
“Hurriya a zuba miki abinci?”
Hurriya ta girgiza kai alamar aa, Momy tabe baki ta dauki wayarta.
“Dan kan masa in ji sure, cikinki ko na wani, kin san dai ba rarrashinki zan yi dan ki daina kuka ko ki ci abinci ba, ina da tausayi da zuciyar imani amman laisa son dan wani kamar nawa kam karya haram babu boye boye ba munafurci, shiyasa ni na fi sha’awar uwarku ta dawo ta rike yayanta”
Tana fadan tana hawa sama har ta haye ta shige dakinta, Mai aikinta kam tuni ta san inda dare yayi mata. Hurriya ta bi ta kallo har ta haye stairs din, ji ta yi kamar ace wani na nan ta fada jikinsa ya rumgume ta yi kuka ammab babu wannan damar, saukowa ta yi daga saman kujera ta zauna kasa sai ta dora kanta sama kujera ta takure guri daya. Ta rufe ido hawaye na sauko mata. After like 30min ta ji an zungureta sai ta farka da sauri gilashin idonta ya fadi da sauri ta dauka ta saka ta gyara mayafin abayarta ta kalli Musib dake tsaye kanta.