VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660

@

CAPTAIN POV.

Da hannu daya yake tuki dayan hannunsa kuma yana amsa wayar da Salim yake masa.

“Matsalata da kai naci, tun muna Ethiopia kake damuna da maganar yarinyar nan, Salim ba zan iya forcing dinta ta soka ba, ya kamata ka hakura tun da har ta nuna maka bata kaunarka”

“Ba wacan maganar ba ce Captain wannan mai girma ce, ba maganar soyayya bace, and yanzu na fahimci yarinyar nan bata cancance ni ba, kuma Alhamdulillah da bata yarda ta amince da soyyayata ba”

Captain yayi dariyar da bata da sauti. Good Boy yanzu ka gane kenan. Ya fada a ransa a fili kuma sai ya amsa masa da.

“To akan me ne?”

“Abun ba zai fadu ba, na kira Namra ina son ta sada ni da Hurriya na yi magana da ita bata amsa min wayar ba, kuma ina son naje gidansu ina tunanin kamar ba za a bari Hurriya ta fito ba”

“Yanzu kana ina?”

“Ina gida”

Captain ya kalli agogon hannunsa.

“Masallaci zan je yanzu, idan mun fito Jumma’at zan kiraka”

“Na so ka zo yanzu Captain wani abu ne da ba shi da kyau gani, ko na zo na same ka?”

“What so ever it’s, sai na fara gabatar da Sallah zan fuskance shi, so ka jirana idan na fito zamu yi waya”

Be jira abun da Salim zai sake cewa ba ya kashe wayar, ya aje a cikin motar ya cigaba da tukunsa, a babban Masallacin kan wurin Sarki dake garin Gusau yayi Sallah Jumma’a sannan ya kira Salim at that Salim yana mosque domin ba masallaci daya suke sallah ba, and akwai banbancin lokacin sallah Jumma’a a Masallacin Sheik Umar Kanoma da na kan wuri. A kokarinsa na martaba lokaci ya nufo gidansu Salim din kai tsaye, a harabar gidan ya shiga ya faka sannan ya aika masa da sako.

“Idan ka gama ina harabar gidanku”

Ya aje wayar ya bude gurin da yake cewa ajiye pistol dinsa ya dauka ya saka a jikinsa sannan ya dauki counter dinsa dake cikin motar ya laka a yatsansa yana tannawa, ya san yau ranar jumma’a ce ranar da aka ce a ninka salati ga Annabi Muhammad S A W, idan kuma baka yi ka yi domin shi salati haske ne a duniya da kiyama. Ya kusan minti talatin a gurin sannan reply din Salim ya shigo wayarsa.

“On my way”

Ya karanta sakon ya sake maida wayar ya saka aljihu ya cigaba da salatin, yana kallon harabar gidan iyakarta rabin na su harabar dake Kaduna. Tsaki ya dan ja ya duba agogon hannunsa, wata zuciyar na ce masa ya kira Salim ya fada masa idan sun hadu a gurin aiki za su yi magana domin baya son bata lokaci a gurin, kamin ya kira motar Salim ya shigo harabar gidan ya faka daidai gurin da motar Captain take, kusan a tare suka bude motocin kowa ya fito, but jin kai irin na Captain ya hana shi isa gurin Salim sai da Salim din ya karaso gurinsa ya jingina jikin motarsa.

“Minene?”

Captain ya tambaya ganin seriousness a fuskar Salim. Karamar ajiyar zuciya Salim ya sauke sannan ya fara taba wayarsa dake hannunsa.

“Ina dawowa na tararda wani labari marar dadi a gidan nan”

Captain ya dauke kai.

“Kan da son jan zance, kai ba mace ba balle ace zan bika ina lallabaka, tun a mota ma ya kamata ka fada min ko minene amman baka yi ba yanzu kuma na zo kana abu kamar mai rubuta littafi, and you know bana son wannan bata lokaci”

“Akan Hurriya ne, wani abu ta aikata ita da Cousin dina, so abun ya daure min kai na tura maka hotunan yanzu ta whatsapp ka duba”

“Ba zan duba ba idan ba zaka fada ba zan tafi”

“Tana mu’alama da cousin dina, ina tunanin shi ne reason din da ya hana ta amsar soyayya ta, and Alhamdulillah na jidadin haka”

Captain ya tsaya cak yana kallonsa with so many questions zuciyarsa ta soma zafi kamin ta tafasa, idonsa na kokarin sauyawa, the word mu’alama kowa ya ji ya san bad thing ake nufi kalma ce ba mai kyau ba. Salim ya mika masa wayarsa

“Duba wannan”

Captain ya karbi wayar ya sauke idonsa akan mugun abun da he wish be kalla ba, hotunan Hurriya ne a sirara tare da mutumen da yake ganin idan ya zo gurin Salim, wani gurin suna kwance a gado daya, wani gurin kuma ta kwanto jikinsa wani kuma ta yana kissing dinta ya tallabo kanta da hannunsa dake cikin gashin kanta, na karshen ne hannunsa yake kan kirjinta and duka hotunan daga ita har shi babu mai tufafi a jikinsu.

“Wannan ba Hurriya ba ce”

“Ni ma hala na fada da farko domin yadda take da tarbiya da mutumci ba zaka yi zaton ta aikata ba”

Captain ya dago ya kalleshi naman fuskarsa na rawa cikin wata kalar murya mai fita da sauti ya ce

“Waya turo maka wannan?”

“Cousin dina ne fa, yanzu haka case din da na zo gida na tarar ana yi kenan, i was shocked da na ga abu kuma na yi magana da shi ya fada min gaskiyar itace amman be san ya aka yi hotunan suka fita ba”

Captain ya hade yawun bakinsa sannan ya nuna wayar Salim dake hannunsa da yatsansa na hadu.

“Ina yaron nan yake Salim? I need to talk to him…”

“Yana ciki bari na kira shi…”

Salim ya nufi main house din da saurinsa shi kansa mamakin abun yake ta wani bangaren kuma yana gode Allah da be yi soyayya da Hurriya ba. Captain ya juya ya kife kansa jikin motar zuciyarsa na bugawa da karfi, wani numfashi mai zafi yana fita a hancinsa da bakinsa, wani irin kuna zuciyarsa take tana isarwa har cikin kansa. Can kuma ya juyo ya jingina da motar, kamin ya daga ya fara zagaya motar hannayensa nade a baya rike da wayar ta Salim.

“Hurriya….?”

Ya furta mamakin zayyane a fuskarsa, juyowa yayi ya dawo gurin da Salim ya bar shi ya tsaya ya rumgume hannayensa yana kallon Salim din da ya fito tare da Adam, kamin su karaso Captain ya nufi gurinsu suka hadu a tsakiyar gidan.

“Abun da Salim ya nuna yanzu nake son na tambaye ka it’s real or fake?”

Adam ya kalli Salim ya sake kallon Captain.

“Wane irin tambaya ne wannan”

Captain ya kawar da fuska yayi murmushi, Salim ya kalli Adam.

“Just answer him”

“It’s real”

Captain ya kara matsawa kusa da Adam yana wasa kafafuwansa kamar wanda yayi shekara a tsaye.

“When how? Where?”

“A inda muka saba haduwa?”

“Da saninta ka dauki hotunan?”

“Aa ba da saninta ba, kuma ban san ya aka yi hotunan suka fita ba”

Captain ya juya baya ya busar da iskar bakinsa ya juyo ya kalleshi.

“Adam idan wani ya saka ka yi wannan abun i cam pay you fiye da abin da aka biyaka”

Adam ya girgiza kai.

“Babu wanda ya biyani, kamar baka san waye ni ba? Wa zai biyani na yi wannan abun?”

Captain ya kalli Salim, Salim ma ya kalleshi kamin ya kalli Adam a karo na biyu.

“Ina kuke haduwa da ita?”

“Tudun wada low-cost”

“Why not gidansu?”

“Saboda iyayenta basa so na”

“Ya aka yi ka san yarinyar nan ina ka santa?”

“Hurriya…? Na hadu da ita a bikin birthday din yayarta Khairy daga lokacin muka fara soyayya sai kuma iyayenta suka fara nuna basa son alakata da ita, daga lokacin sai muka yanke gurin haduwa daga nan dai sai shedan ya shiga tsakaninmu”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected