VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Captain ya maida dubansa gurin Salim cikin kalar yanayi dake sauya kyau fuskarsa da raunin idonsa.

“Idan kana son Hurriya bata so ka ba, wannan normal ne an saba haka, amman kokarin aikata wani abu, martabarta da ta gidansu kake tabawa”

Ya matsa kusa da Salim irin matsawar da yan dambe suke yi idan suka kullace mutum a zuciya.

“Ba zan bar wannan ba, ba zan kyale kowa da hannu a lamarin nan ba”

“What do you mean? Ni zan saka kanena ya aikata haka? Shi ma an taba martabarsa da ta gidanmu ko ka gane?”

“I don’t care shi namiji ne zai iya haka, ko kai ka saka shi ko kuma yana sonta a karan kansa zai iya haka? Hurriya ba zata aikata wannan abun ba ba zata yi hakan a cikin hayyacinta ba”

“Saboda yana wearing innocent face tana nuna ita ta kwarai ce? Baka da wannan tabbacin Captain, miye alakarka da ita wai da kake ta wannan kokarin”

Captain ya matsa baya ya watse wayar Salim dake hannunsa cikin daga murya da ya hankalonta da idon kowa a harabar zuwa garesu ya ce.

“Ubanta ne ni Salim…. Haka kake son ji?”

Cikin zafin nama ya riko hannun Adam ya lankwashe hannun hoton da ya gani na hannuns aa kirjin Hurriya kawai yake ta gani a idonsa har yanzu. Salim yayi hanzarin rike Captain

“No no no no… Captain..”

Captain ya fisge hannunsa ya rika hannun Adam dake ihu da hannu biyu ya daga kafarsa ya karya hannun Adam, da mutane suka yo kansu kamin su kawo ya dunkula hannunsa ya kai a bakin Adam a take ya barar masa da hakora daya jini ya wanke baki, Salim ya rike Captain da karfi amman hakan be hana Captain shimfidawa Adam duka a kirjin da ya kwantar da kan Hurriya ba. Mutanen suka rike Adam dake ihu kamar za a cire masa rai. Salim ya sake shi da karfi ya dawo gabansa ya tsaya

“Captain miye haka? Miye alakarka da ita? Dan me zaka rasa control akan wannan abun?”

Sai kuma ya juya da sauri ya tare wani yayan Adam din dake son kaiwa Captain duka.

“Aa please matsala ce da za a iya magancewa dan Allah Kabir ka bar wannan abun a hannu”

“Bar shi ya taba Captain din soja ya jawa kansa bala’i”

Salim ya juyo gurin Captain dake maganar ya kalleshi ganin yana kokarin ballo masa wasu ruwan ballo masa ruwa a lokacin da yake son toshe wata hanyar, kowa dake gidan sai yayi ma Captain uzuri saboda suna zaton yayan Hurriya ne, shi kansu abun ya taba su balle kuma shi da yake da kanwa mace. Captain ya bude motarsa ya shiga ya bar Salim a tsaye yana bawa Yayan Adam din hakuri domin yau jumma’a wasu yan’uwa duk ba su dawo daga gurin Sallah ba, masu aikin gidan ne kawai sai wannan yayan nasa da kuma mahaifiyar Adam din wacce ta fito tana kuka tana fadin ba zata bar Captain ba.

“Yadda abun ya taba martabar gidansu haka ya tana martaba mu, kuma ai tare suka hadu suka aikata saboda me zai fadawa dana?”

“Ba kyale maganar za’ayi ba, dole za a bi kadi ai, yanzu dai abun da ya fi a dauki Adam din a kai shi asibiti”

Su biyu suka kama shi, Salim da yayansa Kabir suka saka shi a motar Salim din suka nufi asibiti da shi. Suna isa Emergency Salim be tsaya an karbi Adam ba ya bar Kabir da Adam din a gurin ya juyo da motarsa ya bi bayan Captain ya san ba zai wuce ya tafi gidansu Hurriya ba.

Kamin Captain ya iso gidansu Hurriya ya kusa balla sitiyarin motar saboda yadda yake dukansa da mugun karfi yana fisgarsa, gaba daya ya rasa ta ina zai fara tunani. Yana yin fakin be tsaya kashe motar ba ya bude ya fita ya bar motar a bude, yadda ya tura kofar falon Momy da a rufe take zai iya ballata. Hurriya dake tsaye a dinning rike da plate ta juyo cikin tsoro ta kalli kofar falon, domin yadda ya turo kofar falon ya shigo ya firgitata even though bata san waye ba har sai da ta kalli kofar. Kai tsaye ya nufeta daman zuwan domin ita ne!

“Waye Adam…..!”

Ta daga kai ta dubeshi gaba daya muryarsa ta cika dodon kunnenta ta cika falon tsayen da yayi a gabanta kuma ya cika duniyar idonta. Sai tsaya baya da sauri at that time ne ya fisge plate din hannunta ya bugashi a kasa.

“Waye Adam….!!”

Ta yunkura zata ranta ana kare, ya rikota kamar wata bulala haka ya jujjuyata ya jefar a gefen kujera ta fadi kasa tana kwala ihu.

“Subhanallahi? Captain Lafiya?”

Amadadin ya amsawa Momy dake saukowa tana tambayarsa tare da Namra sai ya nufi gurin da Hurriya take kwance ya mikar da ita tsaye ya dauketa mari.

“Waye Adam?”

Ta kai hannu zata taba fuskar ya wanke mata fuska ta dayan gefen sai ta fasa taba fuskar yawu da jini suka gangaro mata lokaci daya, yadda yake daka mata tsawa gurin tambayarta da kuma marin da yayi mata a yanzu ya mantar da ita Adam, domin ta dade ta tattara lamarinsa ta aje a gefe daya tun da dadewa. Momy ta iso da sauri ta rika Captain ta matsar da shi gefe ta kalli Hurriya.

“Me kika masa?”

Hurriya kallon Momy ta yi ta fashe da kuka domin ba zata iya fadar abun da ta yi ba, tambayarta yake wanda bata sani ba. At that time ne Captain ya samu damar runtse ido ya bude ya zauna a kujera ya kasa cewa komai, zuciyarsa na masa wani irin bala’in zafi.

“Wai me ya faru ne can anyone explain?”

Momy ta tambaya a tsawace tana kallon Captain kamin ta juyo gurin Hurriya.

“Me kika yi?”

Hurriya ta girgiza kai. Captain ya dago daker ta danna wutae da yake ji ya kalli Momy yana nuna Hurriya.

“Waye saurayin yarinyar nan Momy?”

Momy ta daga kafadunta.

“I don’t know, waye saurayinki? Miye matsalarka da saurayinta? What’s going on here?”

“Ba ni da saurayi Wallahi Allah”

Hurriya ta amsa cikin kuka, Captain ya daka mata tsawa.

“Karya kike yi waye Adam?”

Namra dake saukowa stairs ta amsa masa.

“Adam Sarauta? Wanda yayi miki ruwan kudi a birthday Khairy ina tunanin shi yake nufi”

Captain ya kalli Namra yana kara tabbatar da zancen da Adam din ya fada masa cewar a birthday yayarta suka hadu.

“Ba sarauyina ba ne….”

Ta amsa cikin kuka bakinta na mata mugun ciwo yana zubar da jini, kana ta kai hannu ta rike rigar Momy ganin Salim ya shigo cikin falon sai zuciyarta ta raya mata taruwa za su yi su duketa. Momy ta juyo ta kalli Salim Namra ma da mamaki take kallom yadda ya shigo falon dake bude babu sallama babu neman izini, hakan kuma yana karantar da ita akwai abun da yake faruwa.

“Ita ma ka fasa mata baki ko Captain? Wai duk na minene? My mind is telling me son yarinyar nan kake a boye Captain? Is that the reason da yasa idan na yi maka maganarta kake fushin dina away? Ba abun kunya ba ne a gareki ka yi soyayya da yarinyar da ni na fara? You betrayed me Captain….”

Salim ya juya gurin Hurriya dake tsaye ya kalleta.

“Thank you da kika rufe kofafin soyayyarki a gareni, na gode da baki ba ni damar dandana bakinciki da yanzu ya zame min abun kunya ba, ashe kin san tarayya kike da cousin dina Adam shiyasa baki karbi soyayya ta ba, tir da ke babu uban da zai so mace mai two face irinki green snake under green grass, kowa ya san wacece ke yanzu”

Duk wata kalma da Salim ya fadawa Captain be dago ya kalleshi ba har sai da ya kai ga taba Hurriya. At that time Captain ya kalleshi sai kuma ya daga kansa sama ya kyalkyale da dariya ya daga kafarsa sama ya buga a kasa.

“Hahahahaha Salim.. Haba Salim….”

Ya sauke kan ya kalli Salim kamar bakin maciji da ke shirin yin sara. In less than second Captain ya mike tsaye ya cire bindigar jikinsa ya taka ta isa gurin Salim ta dora masa bindigar a kasan makoshi ya daga kansa kasa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected