Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
“Baka dai ci abincin ba”
Ya kalli Momy yana saka hananyensa aljihu.
“Abokina ya tafi ransa a bace, taya zan zauna ni na ci abinci? Maybe next”
Ya kalli Namra dake tsaye ya kira sunanta. ”Namra”
“Hmmm”
“Be a good girl please”
Ta yi murmushi mai kyau.
“I will as always”
Ya mayar mata da murmushi sannan ya juya ya nufi kofa, da kansa ya bude ya fita Momy ta take masa baya ita da yarta. Momy na nade hannayenta ta aika masa tambaya.
“Sai yaushe kuma Captain”
“Anytime kina iya ganina ma anjima, ai yanzu ina garin nan har na tsawon wata uku kuma ina tunanin wannan ne best place da zan iya zuwa na yi yadda nake so, ba kamar a bariki ba”
“Me yasa ba zaka dawo nan gaba daya ba?”
“Ban sani ba ko za a su bar ni zan gwada haka”
Ya bude motarsa bayan ya amsawa Namra sannan ya shiga yayi mata key, Momy na daga masa hannu Namra kuma ta bishi da kallo da murmushi har ya fice. Momy ta juyo ta kalleta.
“Wata kila ya jidadin yadda kika karbi bakonsa a yau”
“Ni ma na ga alama”
“Yayi kyau”
Momy ta fada tana murmushi sannan ta sauke kai kasa ta juyo cikin tafiyar kasaita ta shiga falonta. Namra ta dade a gurin tana ta karatun wasikar jaki kamin ita ma ta juya ta koma ciki. Hurriya ta ci abincinta yadda take so, sauran ta saka dayan plate din ta rufe domin idan ta tashi ci anjima ba ta nema ba, kusan ita da marainiya duk daya agidan, wata kila ma marainiya ta fita gata da samun kulawa. Hakan ya taimaka mata bata fito neman abincin dare, shimkafar ta sake ci da dare ta kwanta abunta. Da safe ma bata fito gudun kar ta yi wani laifin ko kuma Momy ta rufe ta fada saboda ta zuba abinci da yawa ta kwashe nama, tana zaune a dakin har karfe goma na safe, tana unkurin tashi ta yi wanka aka turo kofar falon aka shiga, da sauri ta kalli kofar tana zaton ganin Momy ko Namra ga mamaki sai ta yi arba da Khairy.
“Yaya Khairy”
“Na’am Hurriya yanzu kika tashi?”
“Tun dazun amman ban sauko ba sai yanzu”
“Kin yi breakfast?”
“Aa”
“Ni ma ban karya ba, zo muje mu karya bangarenmu, idan mun gama ina son ki rakani wani gurin kin ji”
Ta dan yi shiru kamar mai tunanin yadda zata amsa mata kamin ta daga mata kai.
“Okay”
Ita kam gaba da ta kai ta ko ba komai zata karya, ba kamar jiya ba, already ta san Momy ko masu aikinta za su ce mata abincin safe ya kare kamar jiya, gashi kuma bata isa ta ce zata shiga kitchen ta girka ba ko ta saka a girka mata. Dan haka ta sauko saman gadon suka fice a dakin tare da Khairy, kamin su isa bangaren Hajiya Kaltume Khairy ta kama hannunta ta rike tana bata labarin guraren da za su da kawayenta da ta kwana biyu bata hadu da su ba. A dinning suka zauna ita Khairy da kanta ta hadawa Hurriya tea ta zuba mata komai na karyawa. Hurriya na tauna wainar kwai zuciyarta na raya mata akwai abun da Khairy take shirya mata, domin a iya saninta Khairy bata tana sonta ba ko na rana daya, idan ma kowa zai raga mata a gidan ban da Khairy amman me yasa take nuna mata kulawa tana janta a jiki yanzu? Anya ba wani abu take shirya mata ba? Ta mike tsaye sai Khairy ta kalleta da sauri.
“Ya aka yi baki sha tea ba fa?”
“Ruwa zan dauko a kitchen”
“Zauna bari na dauko miki”
Ta mike tsaye, Hurriya kuma ta koma ta zauna tana kallonta, Khairy na shiga kitchen ta dauko ruwan da cup ta fito, sai mamaki ya kara rafe Hurriya. Haka dai ta karya ba dan zuciyarta natsu da yadda Khairy take mata ba.
“Yaya Khairy saboda Adam ne?”
Khairy ta kalleta
“Ban gane ba?”
“Kike min haka kuma kike son na rakaki mu fita”
“Haba Hurriya Adam din da Appa yace kar ya sake ganinki da shi, kuma yaya ma yayi gargadi akan haka, shi ne zan hadaku? Na rantse miki da Allah indai ni ce ba zaki taba ganin na kawo miki Adam da idonki biyu ba, haba Hurriya kawai ina kokarin ganin na kyautata miki ne, ni yar’uwarki ce be kamata ace muna samun tsabani ba, kin ga yanzu ni aure zan yi, duk kuwa da ba a saka rana ba, amman ban san ya rayuwata zata zama a gidan auren ba, kuma hausawa suna cewa idan kana son gani da kyau to ka aikata mai kyau, and trust me daga yanzu an fara kenan har gaban abada da yardar Allah sai kin ji cewar baki da wata yar’uwa kamar ni a duniyar nan”
Hurriya ta dan yi murmushi ba dan ta yarda ba.
“Amman ina tsoron wani abun da zai saka Appa yayi fushi ko yayi fada, musamman ma ni na batawa Appa rai da yawa idan an sake ban san abun da zai biyo baya ba”
“Hakan ba na fatan ya faru, komai zai zama labari Hurriya, tashi ki shirya da wuri dan bana son mu yi latti”
“Tou”
Ta tashi cikin sanyi jiki ta fice daga falon, ko da ta dawo bangaren Momy mai aikin gyara dakuna ta gyara mata dakinta ta fitar da plate din da ta ci abinci. Tufafinta kawai ta cire ta fada bandaki ta dauki lokaci a bandakin dakin tana Khairy, bata son zafafawa akan negative mind, dan haka take kyautatawa yar’uwarta zato. Ko da fito wanka wani bachi mai dadi ke ziyartarta haka dai ta murje ido ta hana kanta bachin ta shirya cikin ready-made bata damu da daukar jaka ba ganin bata da kudi ko wayar da zata saka a ciki, ta fito tana tafiya a hankali har ta sauko falon. Gaban Momy dake zaune a falon ta fara risinawa ta gaisheta.
“Momy ina kwana?”
“Lafiya kalau”
Ta amsa mata a takaice.
“Zamu fita da Khairy tace na rakata wani gurin”
Nan kam Momy bata ce mata je ko karki je ba, balle ta tambayi inda za su je, a lokacin da Hurriya ta gaji sai ta mike tsaye ta fice daga falon ga bachi ga hawayen da suka cika idonta suna son zubo mata, ba dan komai ba sai dan abin da Momy ta yi mata, ta tabbatar da uwarta ce ba zata bari ta fita ba ba tare da ta tambaye ta me za su je yi ina za su je yaushe za su dawo, ko ma ta hana ta zuwa gaba daya. Amman bata yi ba saboda ita din ba uwarta ba ce
“Na yi marmarinki Amma”
Ta fada tana tsayawa ta kalli bangaren da mahaifinyarta dake zama a da.
“Na yi marmarin rayuwarmu ta baya, a lokacin da kike nan kuma kike cikin koshin lafiya da farinciki, Hamad ma yake nan”
Ta sauke ajiyar zuciya tare da saka hannunsa ta share hawayen da suka zubo mata, sannan ta dauke kai ta shiga bangaren Hajiya Kaltume kamin ta karasa kofar falon Khairy ta bude kofar ta fito da nata shirin tana rike da keys din mota.
“Oh yanzu fa nake cewa zan biya na kiraki na ga kin dade ga garin da hadari”
Hurriya ta daga kai ta kalli sama dake cike da hadari da alama za a iya sako ruwa at any time kuma za a iya yaye hadarin duk cikin ikon Allah ne da abun da ya zo. Ta sauke kai tana hamma.
“Bachi ma nake ji?”
“Bachi yanzu? Ko zaki koma ki kwanta next time sai mu tafi”
“No mu tafi kawai zai sake ni ai”
“Okay”
Suka nufi motar Khairy sai da ta fara shiga ta yi mata key ta juya motar sannan Hurriya ta shiga suka kama hanya. At first Hurriya ta saka ido ne kawai tana sauraren inda Khairy zata kaita duk wani labari da take bata, bata yarda ya dauke mata hankali ba har suka isa gidan dake cike da yan mata suna ganin Khairy suka hau ihu ana rumgume juna irin an dade ba a hadu ba din nan, babu bata lokaci Khairy ta gabatar musu da Hurriya a matsayin kanwarta, Hurriya ta gaishe su sannan ta zauna. Aka kawo abubuwan tabawa ana ci ana hira, ita dai bata yarda ta ci komai ba domin zuciyarta bata natsu da gidan ba, kamar yadda bata gama yarda Khairy ba da sheri take bibiyarta. Tun suna abu tana binsu da kallo har ta kai ta kan yi dariya ko murmushi idan suka fadi wani abun ko suka yi wani abun, daya daga cikin kawayen Khairy ne ta dauko chewing gum ta mikawa kowa ciko har da Hurriya kowa ya karba ya ci, har dayar tana fadar a karo mata daya ba zai isheta ba.