VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Gashi Ethiopian ya ce a baki”

Hurriya ta kalleta, tana tsammanin zata taya ta jimamin korar da Appa yayi mata ko ta tausayawa mata amman bata ga alamar ko daya a fuskarta ba.

“Ki rike na bar miki”

Ta juya ta ja Luggage dinta ta cigaba da tafiyarta, sai da ta fice daga bangaren na Momy sannan ta ci hawaye ya cika idonta duk yadda ta so ta hana su zubowa abun sai ya gagareta, domin bata iko da hawayenta a yanzu hasalima su suke da iko da ita. Har ta isa gate masu gadin suka bude mata suna tambayarta lafiya, bata hararo babban dalilin Appa na korarta a gidan ba. Idan ma mahaifin Husna ya same shi da zancen, be kamata ya koreta saboda wannan ba. Tana tafiya tana karfafawa kanta guiwa hawaye na zubo mata, har ta isa babban titin dake sokoto gusau road, a gurin ta tari napep ta hau zuciyarta bata raya mata zuwa ko’ina ba sai gidan kakarta mai kaunarta Hajiya Binta.

 

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar  MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne  cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai  shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…

Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660

@

1️⃣8⃣

 

Hajiya Binta dake aikin dama shuwaka ta dago ya kalli Hurriya wanda shigowarta kenan da kaya niki niki.

“Subhanallahi Hurriya lafiya”

“Appa ya koreni Hajiya”

“Kora? Kora fa kika ce Hurriya”

Ta daga kai idonta na zubar da hawayen da bata son zubarsu, sai dai kuma bata isa ta hana su zuba ba.

“Me kika masa?”

“Kawata ce ta yi”

“Kuma a gidan aka rasa wanda zai yi wani abu har kika fito?”

“Hajiya Mai Napep yana waje yana jira”

Hajiya ta sauke ajiyar zuciya.

“Shiga dakins ki dauko kudi a jaka ki ba shi”

Hurriya ta nufi dakin, bata dade ba ta fito rike da one thousand ta fice ta sallami mai Napep din sannan ta dawo ta zauna kusa da Hajiya Binta.

“Hajiya yanzu kowa baya so na gidan nan, ban san me na yi ba, kowa ya tsane ni”

Hajiya Binta ta bude robar gishi ta diba kadan ta zuba a cikin shuwakar data dama ta dauka ta sha sannan ta kalli Hurriya ta ce.

“Nasara ce take tare da ke jikata, duk gurin da kika ga tsanani yayi yawa, to wani alherin ne babba zai taho, wata kila nan gaba sai kin zama wata abar kwatance a cikin familynku, duk sai kin fi su daukaka da nasarar rayuwa Hurriya karki ji komai a ranki, kar wannan abun ya dame ki”

A lokacin ne wani kukan shagwaba ya rufe Hurriya ta tabe baki tana kallon kakarta abar kaunarta.

“Hajiya ai yace ba zan yi karatu ba, wai ba da yawun bakinsa ba”

“Idan yana takamar haihuwarki yayi shi ma ai haihuwarsa aka yi! Kuma wanda ya haife shi yana raye, kina can ma nake miki yaki balle kin dawo gurina? Ba dan yana gidan mahaifinki ba ai da sai na ce haka ya fi, daman na yi nayi ya bar min ku na rike ke da Hamad ya ki, yanzu kuma kin ga ya koreki da kansa”

Hurriya ta kwanta jikin Hajiya tana zuba shagwaba kamar ba ita ba.

“Cewa yayi wai na tafi gidansu baban kawata na zauna saboda …”

Hajiya Binta ta girgiza kai cike da takaicin bayan ta gama sauraren dalilin korar da aka yi ma Hurriya.

“Kin yi tunani da baki tafi gidan Iyami a wannan yanayin ba, sai abun ya kara mata yawa a zuciya, idan ma zaki fada mata sai ki ce mata ni na dawo da ke nan gurina”

“Shiyasa na taho nan ai”

“Kim kyauta daman ina neman abokiyar zama, shi kuma Allah ya warware masa duk wani abu da yake cikin kansa, gaba daya an juye masa hankali ya canja kamar ba shi ba, gidan nan ma sai ya dauki wata uku biyu be zo ba, kiran waya kuma sai idan na kira shi, babu ruwansa da kowa sai Kaltume, gaba daya ta dauke masa hankali sai abun da tace yake yi”

“Kuma ni ban ce Babanta yayi masa magana ba fa Hajiya, ni ban yadda aka yi ma Babanta ya ji ba”

“Wata kila tana tausaya miki ne, sai ta aika hakan da kyakkyawar niya, shi kuma ya kasa fahimtar abun, daman kowaye zai ji haushi amman be kamata idonsa ya rufe har haka ba, maraicinki ya kamata ya duba, yanzu da baki da ni ko baki da uwa a raye sai dai ki koma wani gurin rabe gurin yan’uwa ko kuma wadanda baki hada komai da su ba?”

Ta kara gyara kwanciyarta jikin Hajiya.

“Allah ma yasa ina da ke”

Hajiya Binta ta yi murmushin dake kara bayyana tsufanta, ta shafa kan Hurriya.

“Kar Allah ya raba mu har sai na damkaki ga miji mai amana Hurriya”

“Ameen”

Ta amsa tare da rufe idonta tana dariya.

“Ja’irar yarinya wato har da cewa Amin ko?”

Ta saka dariya sosai sannan ta tashi ta dauke kayan ta shiga da su dakin Hajiya.

“Aa daki dabam zamu yi, wake zama da kishiya daki daya”

“Dole ne ki yi hakuri da ni Hajiya daki daya zamu zauna”

“Toh aje kayan ki fito ki ci abinci, na san cikin nan naki yana nan dauke da yunwa”

Kusa da gadon Hajiya Binta Hurriya ta aje luggage dinta sannan ta cire hijab dinta ta jefa saman gado ta juyo ta fito.

“Hajiya me aka dafa miki?”

“Zai wuce tuwo ne Hurriya kin san abincin tsufi ai ba kamar ku ba, idan ma baki son tuwon ki shiga Kitchen ki dafa indomie”

“Toh”

Ta amsa sannan ta nufi hanyar Kitchen din, tun da ta shiga bata fito ba har sai da Indomie dinta ta dahu ta zuba a plate ta dauko ta fito. Aje plate dinta yayi daidai da shigowar Yasir falon hankalinsa a tashe yana ganinta ya dafa zuciyarsa ya nemi guri ya zauna.

“Kin daga mana hankali, na je gidan Amma baki can, na dawo gidansu Husna aka ce baki zo ba, na dauka wani gurin kika tafi”

“Allah yasa dai baka dagawa Iyami hankali ba, domin ba su san abun da ya faru ba”

“No naje gurin ne in a code way, ban fada musu abun da ya faru ba”

“Dadina da kai ai akwai hankali, ka kyauta”

Hurriya ta dube shi.

“Yaya ina wuni?”

“lafiya kalau shi ne kika kama hanya kika taho a madadin ki kirani”

“Yaya ko na kiraka Appa ba zai saurara ba saboda ransa ya bace sosai, kuma ba ni da wayar da zan kiraka ma”

“Duk gidan nan ki rasa wayar da zaki dauka ki kirani?”

Hajiya Binta ta shiga tsakani ganin kamar Yasir yana neman mada abun fitina.

“Aa ba haka ba ne, ita kanta bata cikin hayyacinta a lokacin da ta baro gidan saboda tashin hankali, ta ina zata tsaya neman wayarka ma, kuma kana jin tana fadar cewar yayi fushi ba zai saurara ba”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected