Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Uffan Appa be sake cewa ba ya bata rai sosai, domin sam maganar da Hajiya ta fada masa na abun da Hurriya ta yi be masa dadi ba.
Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660
@
2⃣1️⃣
Appa be raba dayan biyu ba Momy ta turo kofar dalon ta shigo, yadda ta tararda Appa da Hajiya Kaltume a kujera daya ya saka ta daure fuska ta fara wani kallo na uku saura kwata.
“Miye haka Alhaji? Ina ce yau dai girkina ne, ko kuma irin abun da ake yi ma Iyami shi za’ayi min?”
Hajiya Kaltume ta tabe baki, har ta juyar da fuska sai kuma ta juyo ta kalli Momy.
“Magana ce ta kawo ni, maganar da zata taimake ke ki ta taimake ni kuma ta taimaki wanda muke neman aljanna karkashin kafarsa, magana ce akan Hurriya kuma yarki aka aiko da sakon shi nake fadawa Alhaji”
Momy dake tsaye ta dauke kai domin haka be gamsar da ita ba, cikinsu babu wanda yake son ganin abokin zamansa a bangaren mijinsa idan ba girkinsu ba ne, sai dai Iyami suna mata haka, su kam shiga su yi magana da Appa ko da tana ciki wani lokacin har sai Appa da kansa ya nuna musu baya so, ita kuma tana kiyaye yin haka idan ba girkinta ba ne.
“Toh tun da kin fada ai sai ki kama hanya ko kuma maganat bata kare ba ne”
Hajiya Kaltume ta yi murmushi kamar ba ita ba.
“Nafisa… Hajiya Nafisa… Ya fa kamata ace mun aje kishi a yanzu, ya kamata ace mun san girma ya kama mu a yanzu, ni idan ma kina son kwanan idan girkina ya zagayo ai sai na yafe miki, ni dai ina neman mafita ne acikin lamarin nan, domin Hurriya ba ni kadai ta sako a gaba ba har da ke.. Da kuma mahaifinta, wata kila nan gaba kadan idan tana zaune a gidan Hajiya zata iya sakawa ta tsine mana gaba daya, ko kuma ta cilastawa Alhaji rabuwa da mu”
Appa yayi karaf ya ce.
“Aa Hajiya ai tana da hankali da tunani, ba zata yi haka ba”
“Baka da tabbaci kai kanka idan aka fada maka Hurriya zata aikata abun da zai saka ka koreta a gidan nan zaka yarda? Amman da yake butuluce kamar uwarta ai gashi nan ta je ta zage ka a wani gurin ta saka makota suna maka kallon azzalumi, nan gaba kadan kuma baka san abun da zai biyo daga gurin Hajiya ba, kasan dai yadda take son Hurriya take daukar shawararta”
Sai a lokacin Momy ta kai zaune, bayan Hajiya Kaltume ta gama rattaba bayannanta.
“Ni abun da nake gani kawai ka yi hakuri ka dawo da ita gidan nan, idan ba haka ba ma zata iya lalacewa”
Momy ta dubi Hajiya Kaltume ta ce.
“To miye amfanin korarta da Alhaji yayi? Ai sai ta dawo ta cigaba daga inda ta tsaya tana hada mutane”
“To ai mun san halinta yanzu, ko da ta fada ba zamu yarda kuma dole a ja mata kunne”
“To sai dai idan bangarenki zata zauna, ni dai na gaji da zamanta a gurina, balle kuma yanzu”
“Aa ni da take kallon a matsayin makiyiyarta, ta ina ma zata yarda ta zauna a gurina”
Appa ya gyara zama ya kallesu one after the other ya ce
“Kar wanda ya sake bani shawara ko zabin gurin da Hurriya zata zauna, idan har zan dawo da ita cikin gidan nan a inda nake son ta zauna zata zauna, daga gidan har ku da yayanku a karkashin ikona kuke, musamman ke Nafisa na lura da bakinki ba shi da linzami akan irin wannan maganar, kai tsaye kike furtawa, na yi miki kashedi amman baki ji ba, wata kila sai kin ga zahiri… ”
Da mamaki Momy ta kalleshi bakinta a sake ta ce.
“Allah da iko yake, in ba dan ana son a maida laifi gareni ni da aka raina ba, ai Kaltume ma ta yi maganar ba zata zauna a bangarenta ba, amman sai ni kake yi ma radda wato ga ni itace mai dadin hawa, to Allah ya baka hakuri ta zo ta zauna, daman korar ai ba ta Allah da Annabi ba ce, tun da ga shi har kuna son a dawo da ita”
Appa ya dakawa Momy tsawa domin ita kadai ce yake yi ma fada a yanzu, Hajiya Kaltume kuma an saka masa tsoronta ko da ta yi ba daidai ba ba zai iya magana ba, and ba zai iya bijirewa umarninta ba.
“Nafisa… Akan yayana zaki iya janyo wa kanki masifar da zata daukeki daga gidana, bana son ana aibanta min yaya dukansu, ki sani Hurriya ko kisan kai ta aikata Hurriya Haruna Mai Yadi haka za a kirata babu wanda ya isa ya kankare wannan, kin fara kai min hanci kuma ina daf da fyatoki, idan baki rike rike girmaki ba, baki dauke idonki akan Yayana ba za ki sha mamaki”
Hajiya Kaltume dake murmushi cikin rai, ta kalli Appa da ciki wani yanayi dake nuna da gaske take yi ta ce
“Haba Alhaji yanzu saboda Hurriya sai ka ce zaka fadi wani abu marar dadi akan Nafisa, adai yi hakuri shekara nawa ana tare, yanzu ga yaya sun girma ana zancen aure kuma zaka bari shaidan yayi tasiri akanka? Kara dai ayi hakuri duniyar ma duka duka nawa take? Ni ko Iyami ban jidadin rabuwa da ita ba, tun da ga yaya biyu ko da yake yanzu Hurriya ce kadai ta rage, amman dai ba dadi ai, da yanzu tana nan da duk ba zamu samu wannan tsabanin ba, tun da yarta taba hannunta”
Cikin fushi Appa ya ce
“Ko yanzu ai zan iya kai mata ita, ba dole sai ta zauna nan gidan ba”
“Aa kara dai ta dawo nan din, can ga uwa tana jinya abun ai sai ya taru ya zama biyu, wahalar ta yi musu yawa, kana ganin wannan halin da hurriya ta fara idan ba a nan take ba ai kara baci zata yi, ni da kaina zan shirya mu tafi tare a daukota daga gidan Hajiya, ko yanzu ai ta horu”
Momy dai bata sake cewa komai ba, domin bata son Appa ya sake furta mata wata maganar marar dadi a gaban Hajiya Kaltume.
“Ni zan tafi bangarena sai da safe…”
Appa ya mike tsaye ya nufi dakinsa, kama yadda Hajiya Kaltume ma ta fice daga falon bayan ta yi musu sallama. Duk wani damuwa da tunanin tonuwar asirinta ya gushe a zuciyarta saboda farincikin ganin fadan Appa da Momy. Da murmushi ta shigo bangarenta tana maida kofar dakin ta rufe Kulu ta mike tsaye hannunta biyu a hade tana murzawa.
“Hajiya an fito, na ga ita ma Momyn ta fita shiyasa na zo da sauri, sai kuma aka ce min kin shiga bangaren Alhaji shi ne na ce bari na jiraki”
Hajiya Kaltume ta dan yamutsa fuska yayinda ta kawo gurin da Kulu take tsaye da daurin zanenta irin na masu siyar da ganye.
“Zuwanki ai ba shi da wani amfani kulu, kullum babu wani abun da kike kawo wa, tun lokacin da na saka binciken dakin Hurriya baki kawo min komai ba”
Kulu ta shiga rantsuwa.
“Wallahi Hajiya na bincike dakin Hurriya kaf har kayanta sai da na duba amman ban samu komai ba, kin ga kuma dole na fada miki gaskiya ba zan miki karya ba”
“To yanzu me ya kawo ki?”
“Dazun ne ina cikin Kitchen ina wanke kayan da suka ci abinci, kin san Momy bata son a bar kaya ya kwana ba a wanke ba, to ina cikin wankewa sai ga wani bakon Momyn ya shigo, yana ta masifar wai an kori Hurriya Momy bata yi komai ba, har umarni yake bata wai ta dawo da ita, ita kanta Namra da ta saka baki a maganar sai da yayi kamar zai mareta”
“To waye shi?”
“Ina tunanin dan yayanta domin can da yana zuwa gidan sosai kuma danta take kiransa tana nuna masa so sosai, haka suke ce masa kefin”
“Miye alakarsa da Hurriya?”
“Toh nima shi ne ya ba ni mamaki ai, na ce ko sonta yake yi, ya ma daina zuwa an fi shekara uku yanzu sai yanzu ya dawo, amman ita ma kanta Momy da Namra ina jin suna tsinewa Hurriyar suna cewa bata da albarka”