Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Muje ki ganta”
Ta juyo ta kalli gayen. Ta san idan ta je ba mutunta Khairi zata yi ba, wata kila ma zata gwatsale ta ne a gaban mutane.
“Aa ba sai na je ba”
“Okay to muje ki zauna”
Ta kalleshi kamin ta kalli gurin da ya nuna mata. Sannan ta fara takawa da kansa yaja mata kujera ta zauna ta dan jin kunya abun ka da wanda be saba ba, not like bata saba zuwa birthday ba she used to amman ba irin wannan ba, kuma wani namiji be taba ja mata kujera ta zauna ba.
“Thank you”
“You’re welcome kyakkyawa, kina son shan wani abu?”
“Aa na gode”
Ta dauke kai tana kallon yadda kawayen Khairi suke ta takawa MC sai zuba mata kirari yake kamar wata amarya.
“Me yasa kika saka Abaya baki san birthday za’ayi ba?”
Ta juyo ta kalli abayarta.
“Na sani”
“To why do you wear abaya?”
Ta yi masa shiru kamar bata gurin, idonsa na kan wuyanta zuwa kirjinta domin wuyan abayar mai yankan V ne dake bayyana kasan wuyan mutum, wani abokinsa ne ya kai masa duka yana dariya.
“Shegen kaya ashe nan ka boye who’s this?”
Gayen ya kalleshi yana murmushi.
“My new friend i think kawar Khary ce”
“Her Blood Sister”
Hurriya ta amsa masa da kanta sannan ta tashi ta bar taburin ta nufi wanda babu kowa a kai ta zauna tana bawa idonta abinci. Bata ankara ba ta ji ana mata magana dama da ita.
“Sai kuma kika gudu? Tsoron mutane kike ne? Na ga kin kasa sakewa ma what’s wrong”
Ta kalleshi ta dauke kai ba tare da tace komai ba, hannunsa ta ji a fuskarta yana kokarin juyowa da ita, da sauri ta buge hannu ta mike tsaye.
“Miye haka? Akan me zaka taba min fuska?”
Ya daga kafadunsa.
“Fuska ce fa kawai”
Kwafa ta yi ta juya zata bar gurin sai yayi dariya ya mike tsaye da gangan ya riko hannunta, shi dai kam ta masa kyau and as she know friend dinsa Khairy ba zai yarda duk wanda ya zo party ta a yau yace ba a saba rika hannunsa ba, domin kusan rabin yan bikin duka suna rike da hannayen juna ne, saboda wasu are in relationships wasu a dating wasu kuma a new friends to them hugging ko rike hannu is nothing in their team.
“Ya kike yanga yan mata saboda kina da kyau ne?”
Jin ta yi kamar ta tsinka masa mari sai kuma ta ji bata da wannan kuzarin.
“Karka sake taba ni, ni ba irin sauran matan da suke nan ba ne”
“Miya banbanta ki da su? Saboda kina da kyau?”
Ta masa banza, a abu mai muhimmanci ma Hurriya bata cika son amsawa ba balle na banza. Ya dan cize baki yayi murmushi.
“Shikenan zauna ba zan sake ba”
Bata zauna ba ta bar masa gurin tana rabon ido ko zata hango wanda ta sani ta zauna a kusa da shi.
“Wani kike nema?”
Wani ne kuma dabam yayi mata magana har kara wacan gayen da wannan domin wannan kansa ma wani kalar aski ne na yan iska. Shi ma dai bata ce masa na ta nufi gaba gaba ta inda Khairi zata hangota ko zata samu su daga mata kafa. Wani gurin ta nufa ta zauna tana kallon yadda yar’uwarta take rangaji kamar ta sha kwaya, gayen da ya fara yi mata iso ta hango ya isa gurin Khairi yana mata magana a kunne, kamin ya nuna gurin da take zaune har Khairiya ta kalleta ita ma ta mayar masa da maganar a kunne. Sannan ya sauko daga gurin ya nufi gurin MC, before she know sunanta ya cika gaba daya hall din.
“Ina Gimbiyar take, Hurriya ki fito kin yi farar tafiya daya daga cikin kananan matasan mu masu ji da kudi dan gidan Alhaji Buba Sarauta yana nemanki ya ce a kira masa kanwar Hajiyar ta mu wato Khairy domin ta taya yayarta murnar wannan birthday da take da kuma na graduation dinta”
Kowa sai ya fara rabon ido ana ta ga wayw Hurriya wacece Hurriya, Khairi kuma ta kasa boye mamakin dake fuskarsa, tambayarta sunan kanwarta da yayi ta fada masa bayan ya nuna mata ita bata dauka abun da zai yi kenan nan ba. Gaban Hurriya kamar zai fado tsabar bugawar da yake domin bata saba ba, irin haka ma be taba faruwa da ita ba. Kasa tashi ta yi ta rasa me zata yi ba zata iya zuwa gurin da aka bukace ba, bata san ma’anarsa na yin haka ba, so she decided to hide herself, tana kokarin janye kujerar ta boya karkashin teburin, gayen ya nufo inda take MC na biye da shi, hakan ya hanata boya sai kallonsa take ta cikin gilashinta tana jin ta ga abun da zai mata, gaba daya sai hankali ya dawo gurinta ita kanta Khairy sai ta sakar musu ido tana son ganin me ke shirin faruwa. Tun kamin ta karaso gurin da Hurriya take zaune ya cire rapper dollars ya fara bararwar har ya isa gurin da take ya tsaya akanta yana ta zuba mata dollars, idan suka kare sai ya dauko wata a aljihunsa ya cigaba da zuba mata, a take gurin ya dauki ihu aka fara daukarsu da manyan wayoyi wasu yan matan da suke crushing akansa kuma suka kasa boye kishinsu. Gaba daya mantawa aka yi da wani birthday party sai ihu ake ana daukar Hurriya, da gayen dake zuba mata kudin kamar be san zafinsu ba. Hurriya ta mike tsaye da sauri tana kallon Namra da sai a lokacin suka ga juna, bata tsaya komai ba ya nufi kofar fita ta fice daga gurin da gudunta, abun da ta yi ya bawa kowa a gurin mamaki domin at first wasu sun dauka ko budurwarsa ce, sai dai guduwar da tayi ya saka shakku a zukatan mutane. Khairy kan ta cika har tana kusan fashewa domin ta san saboda ita ya zo birthday even though ba saurayinta ba ne he’s just her friend amman ta san kudin da ya zo da su ita ya kamata yayi ma kari da su gashi be yi ba ya karar da su gurin kanwarta.
Hurriya ta fito da sauri ta biyo hanya tsoro duk ya gama cika ta gaba daya ma a firgice take, hankalinta be kara tashi ba sai da ta iso titi, ko’ina tsit yake kamar babu mutane, arzikinta daya rana ce ba dare ba, wannan ya saka ta dan ji sauki. Juyawa ta yi kamar zata koma sai kuma ta ga ba mafita ba ce, tafiya ta fara yi tana rumgume da hannayenta sai ta ji an mata horn, juyowa ta yi ta kalli motar da bakin gilashi ya hana a ga wanda ke ciki. Ta juya ta cigaba da tafiya kamin ta tsake tsayawa kamakon fakawar da mai motar yayi gefenta ya sauke gilashin motar.
“Saboda na miki karin kudi zaki gudu? Idan ni ne ki koma ba zan sake ba”
Ta kalleta ta dauke kai ta cigaba da tafiya, shi ma tafiyar yake slowly cikin motar yana kallonta..
“Idan kuma gida kike son zuwa shigo na kai ki, you’re not safe hare”
Kalmarsa ta karshe ta saka tsoron dake cikinta ya karu, ta dan karkato kadan ta kalleshi sai ya kai hannu ya bude mata front seat. Tsayawa ta yi kamar mai tunani shi ma sai ya tsaya daidai ita.
“Gida zan kai ki, shigo”
Ta kalli abun da ke aje a kasan inda mutum zai dora kafafuwansa idan ya shiga, sai yayi saurin kai hannu ya dauke ya jefata baya.
“Shisha ce please shigo”
Ita dai tun da take bata taba ganin tukunyar shisha a fili ba sai yau, tana dai ganinta a fina fina kuma ta san abun da ake yi da ita domin wadanda ake nunawa rike da ita sha suke suna fitar da hayaki.
“I’m Adam by name, please ki shigo mana Hurriya”
“Na gode zan kira yayana ya zo ya kai ni gida”
“So you get phone please saka min number ki a nan”
Yayi picking latest IPhone dinsa dake cikin motar ya cire key ya mika mata. Ta kalli wayar ta sake kallo sannan ta kai hannu ta karba without saying anything ta saka number yayanta daman daga numbersa sai ta Appa da Ammanta ta haddace a kai. Kara wayar ta yi a kunne
“Hello Yayana.. Ka zo ka dauke ni please ina jin tsoro kuma ina bakin titin gurin Event din ba kowa”