Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Na san shi”
“Marar lafiya ne? Ko yana da wata nakasa ko aibu?”
“Ba shi da shi ko daya Amma, a lokacin da nake gidan idan Momy ta hanani abinci shi yake kawo min wani abu na ci, ko lokacin da Namra ta shake ni shi ya mareta yana da kirki, amman yana da saurin fushi da zuciya kamar Hamad”
Amma ta ji sanyi a ranta jin kadan daga hallaya da siffar mijin da yarta ta aura. Zuciyarta kuma sai ta karkata akan furucin Hurriya cewar Namra ra makureta.
“Me kika yi ma Namra ta makureki?”
Hurriya ta bata labarin abun da ya faru, Amma ta girgiaza kai, ta sani daman jininta ba zai sha da dadin a gidan Momy ko Hajiya Kaltume ba. Ajiyar zuciya ta sauke
“Appanki ya kira yanzu, yace direba zai zo ya dauke ki ya kai ki asibiti ki duba mijinki wai ba shi da lafiya, ki shirya Rukkayya zata rakaki”
“Toh Amma”
Amma ta tashi ta fice daga dakin, Hurriya ta kai hannu tana tana awarwaron da Captain ya saka mata a hannu da sunan wani abokinsa ya bata, tana jin kamar babu dadin jin cewar ba shi da lafiya, ko dai baya son auren ne dole aka masa? Ko kuma wani abu ya faru? Kwantawa ta yi kan tana tunani kala kala a ranta, zuciyarta na raya mata taya mutum kamar Captain zai yarda ya aureta bayan duk abun da ake cewa ta yi? Kuma gashi bata gani a yanzu, wata kila dai dole aka yi masa, amman kuma yadda Momy take jinsa anya zata masa dole? Bayan Namra ta mata gargadi akansa Momy ma ta yi mata. Sai da direban ya shigo sannan Rukayya ta shigo dakin ta saka Hijab dinta ta sakawa Hurriya ta kama hannunta suka fita Amma na Allah ya tsare, Gwaggo kuma na fada mata idan ta shiga ta gaishe da kowa.
CAPTAIN POV.
Idanuwan da ya rufe ne ya sake budewa sakamakon bude kofar dakin da aka yi, Salim ya sake dawowa hannunsa rike da leda ya nufi gurin da aka tana da ya aje ledar sannan ya kalli Captain.
“Sannu Allah ya baka lafiya, ga apple nan na san kana son Apple na siyo a waje ne, anjima zan dawo Allah ya kara afuwa”
Sannan ya kalli Ammy dake zaune.
“Ammy zan tafi sai anjima zan dawo Allah ya ba shi lafiya”
“Amin Salim an gode”
Har ya fice Captain be ce masa komai ba.
“Abun da kake yi wani lokacin baka kyautawa Captain, na san kana da fushi amman danne zuciya ake, ko sai anjima baka cewa yaron nan ba, ba dan kana da aboki kamar Salim ba da yanzu ba ku shirya ba, amman yana mutunkata yana sonka, duk abun da kake masa baya dubawa yana nan tare da kai, duk da yana karkashinka yana baka girma da kulawa na abokantaka ba na aiki ba”
Nan ma be ce komai ba, Ammy zata sake wata maganar wayarta ta yi ringing sai ta mike tsaye ta fice daga dakin. Captain ya sauke ajiyar zuciya ya ya dan dago kadan, ya sake bude wayarsa ya kunna video ya sake kallo.
“Ina fatan hakan ya saka ki farinciki Hurriya, and Sister nan da ta aikata miki wannan abun i hope bakincikin da zata shiga zai ninka wanda ta saka ki”
Ya fita daga whatsapp din ya shiga contact dinsa ya kira Nafi’u. After sun gaisa ya gabatar masa da bukatarsa.
“Asiri na tuno na abun da ya faru da yarinyar nan so zan turo maka video yanzu ina son ka yadashi iya yadda zaka iya, ya karade ko’ina a kafofin sada zumunta Please”
“Za’ayi haka ranka ya dade ka aiko da video”
“Okay, ba zan baka komai ba a yanzu dai na ga yanayin aikinka, idan ka cancanci da yawa zan baka”
“Zaka gani Sir”
Ya sauke wayar ya sake komawa Whatsapp dinsa yayi masa sharing din video. Ya sake kiran wani yayi requesting irin abun da ya bukata a gurin Nafi’u shi ma ya tura masa video sannan ya koma ya kwanta. Bayan kamar minti talatin ya ji an bude kofar dakin sai ya sake bude idonsa Rukkaya ta fara daga kai ta kalli sake kallon kofar dakin domin ta tabbatar nan din ne sannan ta kasara turo kofar dakin tana sallama.
“Sallamu Alaikum”
Be amsa mata ba domin be san ta ba, be kuma san manufar shigowarta ba har sai da Hurriya ta bayyana a bayanta.
“Oh My god”
Ya tashi zaune da sauri farinciki ya cika fuskarsa, hannu ya saka ya kashe ruwan ya cire a hannunsa ya rufe gurin da jinin zai iya biyowa sannan ya mike tsaye ya gyara rigarsa kamar ance masa Hurriya tana ganinsa. A tsakiyar dakin Rukkayya ta ja ta tsaya tana kallonsa.
“Direban Appan Hurriya ne ya ce mana nan zamu shigo, dan Allah ko kai ne Jamal?”
“Yes… Angon Hurriya”
Ya fada yana nufar Hurriyar dake bayanta tana rike da hannun Rukaiyah. Hannunsa ya kai ya kama dantsen hannunta ya rikata yana kokarin fitowa da ita bayan Rukayya.
“Assalamu Alaikum”
Hurriya ta fada tana jin tsoron da wani yanayi na dabam, domin wani be taba kaiwa a jikinta haka ba a take jikinta ya fara rawa. Murmushi Captain yayi Rukaiya ma ta yi murmushi tana mamakin a yadda ta samu Captain domin dukansu ba su saka ran namiji ne mai kyau da tsari da cikar kalama ne ba irin Captain.
“Ban san ya kike da Hurriya ba, dan Allah ce ta sake hannunki ko kuma ke ki sake hannunta”
Ya bukaci haka ne saboda Hurriya ta ki yarda ta saki hannu Mama Rukaiya.
“Ni kanwar Mahaifiyarta ce”
“Oh Ashe mamanmu ce, sorry ban amsa sallamarki ba, a yafe min Momy”
Rakayya ta yi murmushi ta saki hannun Hurriya, Captain ya mika hannunsa ya rika hannun da Rukkaya ta saki ya jata har gurin gadonsa ya zaunar da ita. Sannan ya nunawa Rukkayya kujera.
“Bismillah”
Ta karasa ta zauna tana masa ya jiki.
“Alhamdulillah, ko da aka daura auren ba ni da lafiya shi ya hana ni fita ko’ina balle na je na gaisa da ku mu san juna”
“Idan ka samu lafiya ai sai ka yi Allah ya kara afuwa”
“Amin thank you”
Ya zauna kusa da Hurriya yana kallonta. Baya bukatar tambaya ya san wannan duk shirin mahaifinsa ne, dan haka ya dauki wayarsa yayi ma mahaifinsa text.
“Thank You, you’re the best Dad in the whole world”
Ya aje wayar a gefensa ya maida hannunsa a gurin Hurriya dake matsawa a hankali domin tana jinsa daf da ita.
“Ya jikin?”
A madadin ya amsa mata sai ya kalli dan space din dake tsakaninsu yayi murmushi, wani kalar nishadi da farinciki ne zuciyarsa na ganin matarsa labarin zuciyaa tambayi fuska in ji hausawa, sai yake jin ya warke daga fever ma. Rukayya ta mike tsaye tana rike da wayarta.
“Bari na jira a waje”
“Dama dai kin wuce gida zai fi, domin Hurriya ba yanzu zata koma ba sai dare”
“Gwaggo bata ce na barta ba, cewa aka yi mu zo mu dubaka mu koma, direban ma yana waje”
“Wacecw Gwaggo?”
“Kakar Hurriya mahaifiyata”
Captain ya dariya.
“Ashe ma kaka ce, idan kin koma ki fada mata mijinta ya riketa, daman ya fi Kaka iko da ita”
“Zata min fada”
“Fada kadai zata miki ashe, Wallahi Hurriya ba zata koma yanzu ba, akwai maganar da zan yi da ita so ki tafi kawai karamar uwa madaukar zunubi”
Babu yadda Rukayya ta iya bayan yi masa fatan samun lafiya ta fice daga dakin Hurriya na ji kamar ya ce mata kar ki tafi. Captain ya matsa kusa da Hurriya jikinsa na taba nasa daman ficewar Rykayya kawai yake jira.
“Ni kike gudu?”
Ta yi shiru tana jin kunya na rufe ta, sai ta ji dakin yayi mata girma daga ita sai shi daman tana jin alamar kamar su kadai ne a ciki. Ya saka hannayensa biyu ya zafaye ta ya dora wuyansa a kafadarsa.
“Fada min ya kike?”
“Lafiya kalau”
Ta amsa da sauri, tana kin bashi hadin kan tsuma yatsunsa a cikin nata. Ya sumbanci kuncinta ya kalli gefen fuskarta yana kai dayan hannunsa ya taba Lips dinta
“Ki yi hakuri na mari dukiyata na fasa bakin nan da kaina, ban jidadi ba I’m sorry”