Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Hajiya Binta ta sake fada tana hawaye. Hurriya ta bude ido ta kalleta
“Daman na yi tunanin haka Hajiya, saboda kin fadawa Yaya Namra sakon da zata fada musu, suna ganin kamar kin zafafa sona ne akan na kowa, ita kanta Yaya Namra ta fada min bakar magana, gaba daya a munafuka suke kallona ganin suke kamar zan iya hada ki da Appa ne, Allah kadai ya san fushi da Appa zai yi da ni akan wannan, ni kaina ina tunanin zafafan da Appa yayi ne a kaina ya saka suka raba ni da shi, hawayen nan kuma Hajiya dan Allah ki share su kar wani abu ya sami Appana”
“kin yi tunani kuma na yaba da hankalinki, daman ina masa addu’a kuma zan kara, zan dage, ke ma kuma zan cigaba da yi min kuma ba zan zauna haka nan sai na nemi maganin tsari kala kala na baki, daga kuma karki sake wasa da addu’a Allah ya miki albarka”
Hajiya Binta ta share hawayenta, tare da bawa zuciyarta.
*** *** ***
A mota babu kalar wutar da Hajiya Kaltume bata hurawa Appa a zuciyata akan Hurriya, har tana fadar Hurriya ta hada shi da Hajiya gashi nan har ta yi fushi gashi kuma ta hana Hurriyar komawa.
“Ni daman abun da nake ta ji ma tsoro kenan, nan gaba kuma ba san me zata kulla ba, yarinya karama ta zama munafuka. Ko yanzu karka yarda ka barta a can idan ba haka ba, Hajiya sai ta tsine maka nan gaba, amman karka sake waiwayar gidan sai idan ta huce”
Kwafa kawai Appa yayi be ce komai ba har suka isa gida.
WASHE GARI.
I know littafin nan zai fito, i know zai yi yawo har ya iso gareki. Na fada kuma zan saki repeating Wallahi duk wanda ya karanta min littafi ba tare da ya biya ba, na barshi da mai mafaɗar rana da fitowarta. Daga masu sharing har masu karantawa ba tare da biya ba na barku da Allah…!
Misalin karfe goma sha biyu na rana 12:00pm Captain ya shigo gidan, ya bude tsadadiyar motarsa ya fito ipod a kunnesa yana magana cike da gadata, shi alaka dole ga soja, kuma jinin sarauta ga kuma naira, shigar kananan kaya ce a jikinsa kamar yadda ya saba, domin abu ne mai wahala ka ga Captain Da Shadda sai idan wani abun ya taso. With little strong ya hau entrance din ya murda kofar falon Momy ya shiga, hakan nan dai ya ji yau baya ra’ayin yin sallama even though ba fushi yake ko bacin rai ba, haka kuma ba cikin farinciki yake ba, not happy not sad. Kulu na ganinsa ta mike tsaye ta sauri tana kallonsa bakinta da jikinta suna rawa saboda kwarjinsa, abu mai wahala ka yi arba da shi baka ji tsoro da fargaba ba, musamnan idan haduwar farko ce, ba kuma tsoro na wanda zai maka wani abu, kwarjini da yake da shi da murufa ta tsananin mazantaka da zakantaka ya wuce ka lalleshi baka ji kwarjinsa ba, balle kuma ace ka san yadda yake da saurin fushi da tsananin fada kamar gawurtaccen zaki.
“Sannu da zuwa Sannu da zuwa…”
“Yauwa sannu ya gida ya aiki?”
“Lafiya Kalau Yallabai”
Ya dan juyarta da kai yana kokarin yin murmushi
“No ki kira ni da Captain ko Jameel that’s my name, amman wani Yallabai Yaya ko ranka da ya dade old fashion ne, bana so. Ina Momy?”
“Toh toh na tuba, carpet bari a kirata tana sama”
Ya runtse ido saboda yadda ta sauya masa suna saboda rashin iya pronouncing din. Ta haura sama da sauri, sanin kanta ne ba a shiga dakin Momy kai tsaye idan ba ita ta kira mutum ba, musamman masu aiki, dan haka ta fara ya da zango a dakin Namra ta sanar mata domin ita kuma ta sanar da Momy. Sannan ta sauko da saurinta kamar zata fadi.
“Na fadawa Namra zata fada mata yanzu”
“Na gode”
Ta fice da sauri tana amsawa da babu komai, ai aikinta ne. Namra ce ta fara sauko da far’a jin cewar dan’uwanta ya dawo kamin Momy ta biyo bayansa tana masa lale marhabun.
“Yau kuma an sake ziyararmu, sannu da zuwa dana”
Sai a lokacin ya zauna yana murmushi da murna arba da yar’uwar mahaifinsa kuma mace mai tsakanin kaunarsa fiye da kowa a familynsu.
“Momy ya gida”
“Lafiya kalau, yanzu ka dauki wata bakar dabi’a da ba zaka fada min yaushe zaka zo ba sai dai na gane ka kawai ko? Balle na shirya maka wani abu”
“Ni kaina bana sanin zan biyo ta nan sai dai na biyo kawai, kuma idan ina ra’ayin wani abu ai zan iya kira na fada miki”
“Captain sannu da zuwa”
Namra ta fada sannan ta nufi kitchen.
“Ya aikin? Yanzu ka dawo nan kenan? Yaushe ka dawo kasar wai?”
“Just two days ba, shi ne suka sake kawo ni nan na yi wata biyu zuwa uku sannan na koma gida”
“Kaduna za a maida kai kenan?”
“Yeah na dade ina yawo, so yanzu fitar da na yi waje da kuma sa hannun Daddy, za a bar ni Kaduna na zauna a nan, amman idan aikin ya taso na wasu garuruwa zan tafi mu yi, akwai aikin da ban karasa ba nan Gusau kuma kin san tana ta kokarin a magance matsalar tsaron nan shiyasa aka dage sai na dawo”
“Maa Shaa Allah, Allah ya taimaka gashi nan ka yi Fresh ka kara samun lafiya”
Yayi murmushi tare da kallon Namra data aje masa abun tabawa a mini center table dake gefen kujerar daya zauna.
“Maganar aure dai shi ke nan ka watsar da ita Captain”
“Zan yi aure Momy dolena”
“To na tsorata da lamarinka fa, wacan ma ana daf da daura aure komai ya lalace kuma tun daga lokacin baka sake gabatar mana da kowa ba”
“Bata min rai ta yi da yawa, taya ana daf da daura aurena zaki yi chat da wani saurayi har ya daukeki ku fita, ni fa ina da mugun kishi da zai iya sakawa na kashe mutum, bana iya daukar irin wadannan abubuwan, idan ina son mace ko kallonta bana son ayi”
Ya aje ayar maganar tare da daukar lemun da Namra ta aje masa ta sha. Momy ta yi murmushi.
“Toh Allah ya bada ta gari, yasa kamin ka bar garin nan ka samu wanda kake so, kuma ya rage maka wannan fushi idan ba haka ba zaka yi wahalar zaman aure”
“Amin”
Ya amsa yana dauke fuskarsa da murmushi tare da shan lemun a hankali. Namra ma ta yi murmushi tana taba wayar hannunta kamin ya dago ta kalleshi.
“Yauwa Captain wai a ina ka san Salim?”
Ya juyo ya kalleta.
“Salim Sarauta, abokina ne sosai tun a jami’a muke tare, ke ina kika san shi?”
Ya daga kafada tana dan zare ido kadan kamar wanda ta rasa abun cewa.
“A hanya muka hadu, ya nuna yana so na daga baya kuma ya koma gurin Hurriya, shiyasa na kai shi gidan ma har ka ganshi, amman ban san me ka fada masa ba na ga yanayinsa ya canja kuma har yau be sake kirana ba”
Captain yayi murmushi kasaita murmushin dake kara masa kyauta da haiba
“Ban fada masa komai ba, maybe dai ita ta bata masa rai, na je karbar abu ne na gansu tare, amman karki sake kai shi gurinta, haka yake duk garin da yaje sai yayi budurwa, musamman idan ya ga mai kyau ce just like your sister….”
“Hum himm”
Ya dan kalli Momy kamin ta sake kallonsa dan amsa masa tambayarta.
“Ina yarinyar take ta dawo?”
Momy zata yi magana Namra ta yi karaf ta tari numfashinta ta ce.
“Eh tana dakinta”
Ya maida dubansa gurin Momy fukarsa shimfide da murmushi yayi mata godiya.
“Thank You Momy, ko wace mace ta fi daraja da martaba a gidan iyayenta ko mijinta, kuma a matsayinki na uwa daman haka ya kamata ki yi”
Ya dubansa gurin tsadaden agogon hannunsa sannan ya mike tsaye.
“Ya kamata na tafi kar na bata lokaci”
Momy dake mamaki yadda Namra ta yi masa karya ta ce.
“Nan da nan, baka wani dadewa”
“Yanayin aikin ne a haka, wai Musib har yanzu ba su dawo ba?”
“Suna da daf da dawowa, muna waya da su ai”
“Good”
Ya nufi kofar fita falon, Momyda Namra suka mike tsaye domin yi masa rakiya. Yana bude kofar da zimmar fita Hurriya ta dake rike da kofar tana murdawa da zimmar shigowa, dayan hannunta kuma yana rike da luggage ta sake naushin kirjinsa da kanta daidai saitin zuciyarsa, a karo na biyu by mistake. A take daga hannun sama saitin fuskarta. Kamin hannun ya kai fuskarta ta yi saurin lumshe idanuwanta dake cike da yalwatacce gashin ido ga kuma na gira da ya kara masa kyau a sama, ta dauke numfashinta tana jiran jin tafin hannunsa a fuskarta.