Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
Appa sai kallonsu yake yana shafasu idonsa a raunace kamar mai shirin yin kuka, sai dai be bar hawaye ko alamarsu a idonsa kasancewarsa namiji kuma Uba. Abun da Hurriya ta kasa yi ita kan sai da nata hawayen na farincikin suka zubo, yaran da ba su taba rabar gurin da mahaifinsu yake ba suka ji dumin jikinsa. Yau gasu zaune a cinyarsa yana shafa su. Kusan a lokaci daya kowa ya kalli kofar falon da aka bude har Appa. Captain ne ya shigo cikin shiga ta kananan kaya kamar kullum yana rike da keys dinsa dayan hannunsa kuma yana rike da wani kwali da aka yi rapping. Saitin gurin da Hurriya take tsaye tana share hawaye ya fi maida hankali, kamin ya kalli gurin da Appa yake zaune tare da yaransa yana amsa sallamarsa.
“Sannu da zuwa Captain”
Namra ta fada cikin murna da farinciki ganinsa tare da kyakkyawar tarba kamar kullum, Captain ya aje kayan dake hannunsa a mini glass table dake kusa da inda yake tsaye ya karasa gurin Appa ya risina har kasa ya mika masa hannu biyu ya rika hannun Appa daya.
“Barka da yamma Appa”
“Barka dai yaro ya aikin?”
“Alhamdulillah, ya hakuri Allah yayi mata rahama, mun yi gaisuwa a waje amman ban samu gani ka ba”
“Alhamdulillah, Ameen ya Allah. Ba komai Allah ya bada lada”
Appa ya amsa kana ya kalli Namra dake gabatar masa da Captain.
“Wannan ne ďan Yayan Momy Jameel”
“Na wayance shi ai, Nafisa tana yawan nuna min hotonsa da labarinta, wannan ne karo na uku da muka gaisa i think”
Captain ya amsa da auri.
“Haka ne ranka ya dade”
“Allah ya taimaka”
“Ameen na gode”
Ya amsa yana rankwafawa alamar girmamawa da kunyar da be san ta ina take fito masa ba. Appa ya sauke twins ya mike tsaye ya rika hannunsu ya nufi stairs, sai da ya haura ya shige dakin Momy sannan Captain ya kalli Hurriya da yake zaton ko an kai kararta a gurin Appa ne ya shigo yayi mata fada har take kuka.
“Why are you crying?”
Ya tambaya me take yi ma kuka in a sign language, sai ta girgiza kai ta sauke idonta kasa, ko da wani abun aka yi mata ta ina zata iya fada a gaban idon Namra, ta sake dago kai zulum ta zurma su a idon Captain dake kallonta kamar babu gobe, wannan karon da girar idonsa yake tambayarta.
“Me ya faru?”
Ita kuma da yake bata iya munafurci ba sai ta amsa masa da kai cewar babu komai ta kalli Namra ta yi saurin sauke idonta kasa.
“Na dauka zaka ce ya jikina Captain”
Namra ta tambaya tana kokarin kawarta abun da idanuwanta suke dauka.
“Baki da lafiya ne?”
Ita yake tambaya amman idonsa suna gurin Hurriya dake motsa siraran yatsun hannunta.
“Cizon da kunamu suka min jiya”
Sai a lokacin ya kalleta yayin da yake kokarin rage tsawonsa.
“Oh gaba daya na manta Wallahi, hankalina yana gurin yarinyar nan na shigo na ga tana hawaye na dauka wani abun ne ya faru”
Namra ta kalleshi irin kallon nan na yadda ya fada mata haka kai tsaye ba tare da tsoro ko jin nauyi ba. Shi kuma be yi hakan da wata manufa fa face gaskiya, domin ya ji duk wani takurawa da suke son su yi ma Hurriya, kuma ya ga wasu a idonsa, jiya ma ya shigo ya tarar tana kokarin kasheta, hakan sai ya kara masa tausayinta da kuma son ya taimaka mata.
“Me yasa kake damuwa da abun da ya shafi Hurriya Captain?”
Tambayar ta kutso ta huda makogaronta ta lakanci halshenta ta fito ta bakinta ba tare da ita kanta ta shiryawa hakan ba, sai dan mamakin jin furucin da bata tsammaci jinsa daga bakinsa ba. Sai da ya kalli Hurriya dake kallon Namra sannan ya aika mata da tambaya ba tare da ya amsa tata tambayar ba.
“Saboda Uwata ce. Me ye matsakarki da hakan?”
Ta kalli Hurriya har zata yi doguwar magana sai kuma ta takaita ma kanta wahala.
“Babu”
Ta mike tsaye ta aje remote din hannunta ta nufi stairs har ta haura ta shige dakinta bata juyo ba. Hurriya na ganin haka ita ma ta mike tsaye domin barin falon kamar daga sama ta ji yana bata umarni.
“Shiga Kitchen ki dauko min ruwa”
Ba tare da tace komai ba, ta juya alakar tafiyarta zuwa hanyar Kitchen din gabanta na faduwa, saboda hukuncin da Namra ko Momy za su yi mata na abun da ya faru yau idan Captain baya gidan yana kusantota tun kamin ta san sakamakonta. Ta bude refrigerator din mai kofa biyu ta dauko ruwan dake gefensa murfin ta dago ta rufe sai ta ga mutum tsaye jikin dayan kofar refrigerator din yana hade hannayensa yana kallonta. Ta dan ja baya kamar ta tsorata sai kuma ta nufi kofar fita daga kitchen din tana rike da gorar ruwan.
“Wa zaki kaiwa ruwan?”
Ta juyo ta dawo ta tsaya gabansa ta mika masa ruwan, gaba daya kwarjininsa ya rikitar da ita. Be karba kuma be fasa son sanin dalilin zubar hawayenta ba, ji yake kamar ba shi da natsuwa da sukuni idan be zama silar yayewar damuwarta ba a koyaushe, zuwansa ma a yau na tabbatar da ta ci abinci ne.
“Me kike yi ma kuka?”
Banbancin tambayar dazun da ta yanzu, furuci kawai, dazun yana mata ne in a code way a yanzu kuma kai tsaye ya tambaya, yana kallon da ya fi kama da an hallito idonsa ne domin kyakkyawar fuskarta. Ta karantu kuma ta haddace cewar baya son maimaita tambayar, baya bada umarni sau biyu, gashi fa saurin bacin rai wata kila ma yar karamar bindigarsa nan tana nan tare da shi, wata kila kuma idan bata amsa masa tambayarsa a wannan karon ba zai barta ta fice daga gurin ba.
“Kawai na jidadin yadda Appa yake kula da twins ne ya dora su a jikinsa yana wasa da su, abu ne da be taba yi ba, Twins ba su taba zuwa gidan nan ba sai jiya, ba su taba rike hannun Appa ba, ba su taba zama a jikinsa sai yau shi ne abun ya saka ni farinciki, har na yi hawaye”
_Me yasa ba su taba zuwa gidan ba? Su ba yayansa ba ne? Me yasa be taba wasa da su ba? Me ya faru?_ kusan lokaci daya wadannan tambayoyin suka jero masa, and then he realized be kamata ya tambayeta any of those questions ba, be ma kamata ya wuce gona da iri ba.
“Kwalin dake falo na ki ne ke da twins, kin ci abinci?”
Ta daga masa kai, sannan ta juya zata fice har ta isa kofar kitchen din sai kuma ta juyo, tana tunanin da wani suna zata kirashi, yadda Momy da Namra suke kiransa, a gudun bata masa rai ko rage masa girma ya saka ta raba sunan da sunan da take ganin ya dace.
“Yaya Captain…”
Ya kalleta yana hade ruwan da ya cika bakinsa da su, be amsa ba be kuma fasa kallon idonta da ta kasa dagowa ta kalleshi ba.
“Removed the last sentence”
Ta dago cikin hankali da natsuwa irin nata, ta kalleshi ta cikin gilashin idonta irin kallon dake kashe zuciyar namiji, da muryar dake narkar da zuciyar mai saurarenta ta ce.
“…Ya… Ya… ”
Al’adarsa duk wani wani suna da za a kira shi, idan ya wuce Captain da Jameel kauyanci ne, kalmar Yaya bata masa dadi ko kadan saboda haka ya hana kowa a familynsa yi masa inkiya da Yaya. Sai dai wacan karatun nasa ya kau, dokokin da ya gidanya sun rushe a lokacin da kunnuwansa suka yi kicibus da sautin da ya fito daga bakin Hurriya, she pronounce it so right, so different, so unique, so sweet.