Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Amma gasu nan sun iso, tare da mai hoton amman Gwaggo tace a fara kai masa Hurriya su gaisa kamin mu shirya a fito hoton”
Amma ta kalli yarta dake hawaye har lokacin tana murmushi.
“Amarya tashi tafi ki gaisa da angonki”
Hurriya ta ji gabanta ya fadi, irin faduwar gaban dake samun ko wace amarya a ranar wunin aurenta, daman tun da aka daura auren har zuwa yau ganin take kamar mafarki take ba gaske ba. Kamin ta yi wani yunkuri Gwaggo ta shigo daki tana masifa wai fitowa da amarya ya gagara a bar ango a can yana jira.
“Ai dole ya jira Amaryar ta mu mai tsada ce Amma”
Rukayya ta fada, Gwaggo ta gwatsaleta.
“Dan Allah can rufe min baki marar kunya uwar kawai”
Gwaggo ta kama hannun Hurriya ta fice da ita daga dakin.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
Yana jin kamshi ya doso bakin kofar falon da yake zaune yayi saurin rufe idonsa, yana murmushi, sai da muryar Gwaggo dake rangwado sallama ta karya hanzarinta. A dole ya bude ido daya.
“Haba dai ina zumudin fara ganin Matata sai kawai na yi arba da fuskar tsohuwa…”
Gwaggo ta yi dariya tana mamakinsa.
“Kai daga na maka abun arziki na kawo maka ita na rabaka da jira shi ne zaka watsa min kasa a ido? Daman ai ni ce uwar gidan ba ita ba”
“Aa ni yarinya na aura ba tsohuwa ba”
Gwaggo ta girgiza kai. Ta matso da Hurriya ta gabanta.
“To gata yaran zamani marasa kunya”
Shi dai be ce mata komai ba sai kallon Hurriya yake, har Gwaggo ta fice daga dakin. A inda yake kyautata zaton gabas ne ya maida gaba ya duka kasa yayi sujadar godiya sannan ya dago ya daga kansa sama yana kallon Hurriya dake tsaye gefensa.
“Fatabarakkallahu ahsanal halikin… Tsarki ya tabbata ga ubangijin da ya mallaka min Hurriya a matsayin mata”
Ya mike tsaye ya fuskance ya kama hannayenta masu taushi yana murzawa a hankali.
“My Angel rabin rayuwar Captain Jamal Aliyu Turaki, macen dake harba wuta a zuciyar Captain, macen da zuciya takw muradi rayuwata take tsoron rasawa”
Ya hade goshinsa da nata yana kallon kwayar idon da ta rufe duk kuwa da kasancewar bata iya ganin komai ba dan komai ba sai dan tsananin kunyar Captain da take ji a yanzu. Shi ma rufe idon yayi suna ta musayar Numfashi, slowly ya saki hannunta ya saka hannayensa ya zagaye kwankwasonta.
“Finally…”
Ya rada tare da sumbantar saman fatar bakinta. Ya dago hananyensa yayi sama dasu ya kwantar da ita a kirjinsa dake cike da babbar riga.
“Ina da wata babbar kyau da zan miki, na zabi na fada miki a yau ne saboda yau din nan rana ce ta musamman a garemu amman ba zan baki kyautar ba sai nan da wani dan lokaci kankane, kuma karki tambaye ni minene zaki gani idan lokacin yayi, wannan kyautar ita ce cikar farincikinki a tare da ni”
Ta yi shiru ya labe a jikinta fitinannen kamshin dake tashi a jikinsa yana ratsa hancinta ya rikita lissafin kwakwalwarta.
“My Precious Pearl”
Ya furta mata yana kwanto da kansa kusa da saitin kunnensa. Ta kara lafewa a jikinsa tana jin kamar ta fi ko wace mace sa’arta dacen mijin aure a yanzu.
“Yaya…”
“Uhmmm”
Ya amsa can kasan makoshinsa yana jan numfashi, ruwan turaren da ta yi wanka da su kamshi na rikita masa lissafi.
“Kar wani ya shigo”
Rumgume ta ya yi yana lilo ya daga kansa sama idonsa suka cika da kwalla. yana shakar kamshin dake jikinta.
“Ai ni halalinki ne Hurriya, daga ranar da aka daura mana aure aka musanya komai bawa ya zama halalinki kuma na ki, naki kuma ya zama nawa, yau kin saka ni shiga wani yanayi da ban taba jin kaina a ciki ba”
Wani shauki na angonci da farinciki yake jin kansa a ciki, tun da aka daura auren be taba jin nauyin ya hau kansa ba sai a yau. Dagota yayi daga jikinsa ya daga mayafinta ya sauke shi a bayanta yana kallonta. So now Hurriya dake tsaye a gabansa matarsa ce.
“My dream Girl, i never knew you’re the one waiting for me, Allah ya bar min ke i see the future in you… My soul my heart my blood line my joy…”
Ya sumbanci goshinsa irin sumbantar da sai da yawun da ya jika goshinsa ya saka tsigar jikinta tashi, ya sumbanci gefen fuskaerta hagu da dama sannan ya kwantar da kansa a wuyanta hancinsa ya shakar kamshin dake tashi a gurin, har lumshe ido yake yana jan numfashi.
“Ranar yau kamar mafarki baka ji haka ba?”
Ya bude idon ya kama fuskarta yana yawo da idonsa, ya sumbancin hancinta.
“Na ji, abun dai kamar wasa ace ni din ango ne, kuma angon ma na Hurriya…”
Ta bude idon tana kallon numfashinsa ke fita, sai ya hade goshinsu yana goga mata hancinsa a hankali.
“Bana jin akwai wata macen da ta yi dacen, ango a yau kamar ni, ka kawar da duk wani abu da ka ji, ka runtse ido daga komai ka tsaya ka dage sai ni, ban taba hasahen wannan ba, farkon da ka fara dukana ina maka kallon azzalumin mutum ne marar imani da tausayi ashe ban fahimce ka ba, kai zaka canja rayuwata…”
Yayi murmushi mai sauti.
“To ba dole ba, tun haduwarmu ta farko da kika buge kirjina kika guda zuciyata kika shiga ciki kika zauna abunki, ban san kina ciki ba sai daga baya and i have faith in what i see, a karo a biyu ma haka kika daki kirjina kika kusa kika shiga da karfin tsiya kika yaki duk wata mace dake shirin shiga ciki kika zauna”
“I think i meet a angel in person, ka zama hasken rayuwata ba”
Ya saka hannunsa yaja lips dinta da sha man lebe a hankali yana kallonsa cike da fitina.
“Tukuna dai… Yanzu din ne zan sama hasken rayuwa kuma sanyin idanuwanki Hurriya”
Ya hade bakinsu na wasu dakikun da suka suka kusa hada mintuna daya. Yadda jikinta yake rawa ya kara tabbatar masa da ita din sabo shiga ce da bata saba da irin abubuwan nan ba.
Sai da ya ji alamar shigowa mutana sannan ya natsu ya kyaleta, ba tare da ya dauke ido akanta domin kallonta ne kadai abun da ke kwantar masa da hankali a yanzu, daren ma ya karaga yayi matarsa ta kasance a gefensa. An yi hotuna kamar za a kure camera duk wani hoton da aka dauka da Captain idan Hurriya tana ciki zaka tarar yana satar kallonta ne ko ma yana kallonta gaba daya. A nan ya samu gaisawa da wasu daga cikin yan’uwan Amma aka gabatar da shi a gurinsu suka ganshi shi ma ya gansu sai yaba halinsa da hakittarsa suke suna fadar shi da Hurriya sun dace da juna.
A can gidansu ma hotunan aka sha kala kala daman amsu dauka hoton ba daya ba ne, abinci ma sai kalar wanda kake ra’ayi zaka ci, abu daya ne ya rage armashin bikin shi ne rawa da ba ayi ba, domin babu kamu babu dinner abun da mutane da yawa suka saka ran za’ayi amman ba’ayi ba, saboda lalurar dake tare da Hurriya ta ido, idan aka ce za’ayi zata wahala kuma mutane da yawa za su gane Amaryar makauniya ce.
Da yawa sun zo daga dangin Appa saboda ya sanar musu da kanshi, hakan ya nuna yana son zuwansu bikin kenan, ciki har da Sapna da wasu daga cikin yayanta, amman daga bangaren Hajiya Kaltume har Momy babu su babu yayansu haka kuma babu a wani na su da ya zo. Amma ba ta yi mamaki ba daman ta san ba za su zo yarta ba, balle kuma abun alheri ya sameta kamar wannan na aurar Hurriya da mutumen da kowa ke yaba halinsa da na Iyayensa.