Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Marar kunyar yaro, Momy zaka daka”
Dayan ta doka kamin ta dauke hannunsa Hamad ya fashe da kuka ya zageta da hannu, shi ma ta rikoshi zata dunduma masa dudu a baya, Hurriya na ganin hakan ta shiga tsakani ta tare shi, sai fadan ya koma tsakaninta da Namra.
“Okay hana ni zaki yi na dake shi? Ko baki ga zagina yayi ba?”
“He’s just a child, daukar alhaki ne kawai Yaya Namra”
“Okay to bari ke na dauki alhakinki na lura ganin kike kamar ni din nan sa’arki ce ko?”
Namra ta kama wuyan rigar Hurriya ta shaketa har sai da ta fada baya kan kujera, Hurriya na kokarin kwantar kanta tana kuka saboda karfi ba daya ba
Momy kuma na tsaye ta ki ta raba sai zuga Namra take wai idan ba duka ta yi mata ba zata daina raina ta ba. Hamid da Hamad kuma suka hau kuka suna dukan Namra ta bayanta, dayan ya dauko remote din dake Center table ya jefi Namra da shi.
“Kin ga wadanan berayen babu tarbiya a tare da su sam… ban san me ya saka Yasir ya shigo min da su nan ba”
A tsakanin rufe bakin Momy da turo kofar falon da Captain yayi ba a iya shaidar wanda ya riga wani ba, shigowa yayi cikin falon ya bayan ya rufe kofar yana kallon Namra da ta danne Hurriya har a ganinta.
“Me yake faruwa?”
“Captain”
Momy ta fada, sai Namra ta dago da sauri ta juya ta kalli kofar, hakan ya bawa Hurriya damar silalowa kasa tana tari kamar zata mutu, ba karamin shaka Namra ta yi mata ba, a kokarin ganin ta kece rainin a tsakaninsu ta kusan aikata lahira ba da niya ba. Captain na hango Hurriya ya nufi gurin ya saka hannunsa ya dago kafadunta sai nishi take daker tana tari hawaye na fitowa a idon da bata iya shaidar waye a gabanta saboda babu gilashi a idon nata. Hamid ya dawo gurinsa yana dukansa yana kuka a zatonsa shi ma wani abun zai mata. Captain ya juyo ya kalli Momy.
“Momy kina kallo ana kokarin yin kisan kai?”
“Hurriyar ce bata jin magana Captain rashin kunya take yi ma Namra kamar ba yayarta ba, saboda yaran nan ta kama Namra da kokawa”
Ya saketa ya mike tsaye ransa a bace.
“That’s mean wani abun aka yi da ya kufular da yarinyar nan, idan ba haka ba babu yadda za’ayi ta kama Namra da kokawa, yarinyar da ko yatsa aka saka mata a baki ba zata ciza ba, ban san me ya faru ba amman zan iya shaidar ita ke da gaskiya”
“Captain baka san me ya faru ba, be kamata… ”
Tasss ya wanke fuskar Namra da mari tun kamin ta karasa furucinta. Ya nunata da yatsa wani abu na fisgeshi yana kokarin ninka masa bacin ransa.
“Idan kika sake kai hannunki a jikin yarinyar nan….!”
Sai kuma yayi shiru be karasa ba sai wani mugun kallo yake watsa mata. Namra ta rike fuska daga ita har Momy mamaki ya hana su sake cewa komai. Ya juya ta nufi gurin da gilashin Hurriya yake ya dauka ya kama hannunta da take lalabe da shi ya danka mata gilashin. Sai ta karba ta saka ta kalleshi.
“Na gode, na gode da ka zo…”
Ta furta wasu hawayen na sauko mata, ta san ba dan ya zo in time ba wata kila da yanzu an yi gawa ta biyu a gidan.
“Me ya faru?”
A madadin ta yi magana sai kawai ta fashe da kuka, daman haka take ko a can da idan suka yi fada da Hamad bata iya maida magana saboda kuka, Hurriya irin yaran nan ne da idan aka yi fada basa iya bitar abun da ya faru ko da kuwa su suke da gaskiya saboda kuka. Tausayinta sai ya kara kama shi, daman zuciyarsa ta raya masa tana nan bata ci abincin dare ba, wata kila ma har da rana domin ya lura da yanayinta a dazun shiyasa har ya dawo gidan da dare, ashe da rabon ya tararda wannan fadan ne. Namra ta lumshe ido sai a lokacin kuka ya zo mata, Momy ta kama hannunta suka nufi stairs tana kuka, Momy kuma rai bace an taba mata yar gudaliya gashi babu halin ta yi magana saboda Captain ne, ta san idan ta yi magana zai iya cewa saboda ba ita ta haife shi ba shiyasa ta yi magana dan yi mari Namra, wata kila ma yayi fushi, kuma idan abu yayi zurfi ba zai tsaya iya tsakaninsu ba.
Hurriya ta mike tsaye ta share hawayenta, ta kama hannun kanenta.
“Su waye wadanan?”
“Kanena ne”
Ta amsa tana jansu, shi ma dai ya tambaya ne saboda confirmation amman ya ga kamanin a fuskarsu ai. Hurriya ta haura sama da yaran ta shiga dakinta ta saka Hijab dinta ta sauko tare da su, a lokacin Captain na zaune a sofa yana kallonta har ta sauko tare da su.
“Ina zaki je?”
“Gida zan kai su”
“Cikin dare?”
“Daman Gwaggo bata so su kwana a nan ba, ni ce na takura su kwana a nan, kuma gashi yanzu saboda su ana yin fitina”
“Je dakinki ki kwanta”
Ya bata umarni kai tsaye.
“Daman Amma bata son…”
Bata karasa ba ya daka mata tsawa.
“I thought na fada miki bana maimaita magana”
Ta juya da sauri jikinta na rawa ta nufi stairs, daman tsoronsa take balle yanzu da ya mari Namra a gabanta. Twins na ganin ta nufi stairs suka fashe da kuka suka bi bayanta, Captain ya kallesu.
“Dawo ki zauna a nan”
Kamar umarni take jira ta juyo da sauri ta dawo ta zauna sai suka nufeta suna zauna suma kusa da ita suna kuka.
“Ki rarrashe su mana, ki zubo abinci ku ci”
Ta mike tsaye ta nufi dinning tana waigensa, daman dai bata isa tace masa Momy ta hana ta taba abinci idan bata ci ba, kar yayi mata fada, babba plate ta dauka ta zuba abincin ta dawo tsakiyar falon, ta koma ga dauko ruwa sannan ta zauna ita da kanenta suka fara cin abincin kamar wasu marayu. Hamid sai kallon Captain yake abun da Hurriya ta kasa yi gaba daya tsoronsa ya cika mata zuciya, hantar cikinta sai kadawa take.
“Wuta….”
Little Hamad ya fada yana nuna kitchen din. Gaba dayansu suka dago suka kalli kofar kitchen dake cikin da hayaki, Captain ya mike tsaye da sauri ya nufi kitchen din, hankalin Hurriya ma ya tashi ita ma ta bi bayansa kamin su karasa suka ji ihun Namra, Hurriya ta yi zaton wutar kitchen din ce ta fito da ita daga dakinta har take ihu.
“Kunamu a dakina sun cijeni akan gadona suka har uku wayyo Allah na….”
Sai suka ji wani abun na dabam, sai kuka take tana sosa bayan rigarta kamar zata fita daga hayyacin, har wani tsalle take tana saukowa kai kace ma fadowa zata yi a stairs din. Captain ya kalli Twins din dake ta cin abincinsu, dayan yana kallon Captain dayan kuma yana kallon Namra dake mirgina a stairs tana kiran Momy.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…