Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Amman Ina son Captain, Hurriya me yasa kike min haka? Why?”
Ta fadawa kanta kamin tambayar karshe ta biyo baya. Ajiyar zuciya ta sauke ta share hawayenta ta nufi gadonta ta zauna tana busar da iskar bakinta, zuciyarta na mugun zafi wani fitinannen kishi take ji marar misaltuwa, kamar an fisgeta haka ta tashi ta fice daga dakin.
A kasale Hurriyya ta shiga dakinta bata lura da ledar dake kan gadonta ba saboda hankalinta gaba daya ba a gurin yake ba, ya tafi gurin tunanin rayuwarta ta baya, alamar da Amma ta bar mata na cewar ba zata dawo gidan ba ya saka ta kewar lokacin da take gidan, tana ayyana yadda zata cigaba da fuskantar wahala da kalubale na rashin Amma a gidan. Daf da zata zauna ta yi arba da bakar ledar daman hausawa sun ce hankali ke gani ba ido ba. Hannu ta saka ta lalaba ta juya ta kalli kofar dakin dake rufe tana mamakin waya kawo ledar a dakin. Zaunawa ta yi sannan ta saka hannu biyu ta bude ledar wani dan karamin kati ne a sama dauke da wasu takaitattu kalmomin.
_Tafiya ta kama ni yau din nan, kuma zan yi sati a KD, na san kuma ba ki samu abinci in time na siya miki wannan i hope zai taimaka, karki ci da yawa so that yayi miki sati lol_
_Yaya_
Tana gama karanta sai ta ji kamar an cire mata damuwanta gaba daya, sai murmushi take tana sake karantawa, and the part da yace kar ta ci da yawa ya saka ta nishadi. Ta aje takardar a gefe ta shiga ciro kayan, kwalin dabino ne uku sai chocolate da kilishi da aka busar tare da biscuits kala kala da kuma karamin kwalin cornflakes da madara cube sugar and different varieties of sweet Candy. Chocolate daya ta dauka ta bude ta fara ci tana tuna abun da ya faru a dazun tsakaninsu murmushinta ne ya fadada zuciyarta kuma ta shiga bugawa da mugun karfi kamar zata fasa kirjinta ta fito, numfashinta yana yin sama kamar yadda ta samu kanta a lokacin da ya matso daf da ita yana mata magana.
“Hurriya?”
Ta kalli kofar dakin a zarane tana amsawa Namra dake tsaye rike da kofar.
“Na’am”
“Ina fatan dai ba rokon Captain kika yi ya siya miki wani abu ba?”
Ta girgiza mata kai.
“Good saboda wannan iskancin da karuwanci da kika rika yi ma Salim be kamata ki koma gurin abokinsa ba bayan kuma kin nuna masa baki sonshi, sannan Captain ba sa’arki ba ne zaren ba kalar yadin ba ne, yana da kyau ki yi hankali tun wuri, bana son kina shige masa, karki sake yi masa magana daga yau, saboda ni yake zuwa gidan nan so daga yau bana son na sake ganinki idan yana nan, ban ma rashin hankali irin na ki me Captain zai yi da makauniya”
A nan sai Hurriya ta kasa hade maganar da Namra ta jefe ta da ita.
“Zan kiyaye, ni daman ba ni nake mishi magana ba ni babu wata alaka a tsakanina da shi, wata kila ba ki fahimta ba ne, zancen makanta kuma wannan ba da ni kike ba, da mahallice ma kike ke ma kuma ba ki wuce ya dora miki ba”
“Idan be dora min ba, ke ai zai ki zo ki dora min shashasha kawai”
Taja tsaki sannan ta ja kofar dakin ta rufe da karfi. Hurriya ta ja dogon numfashi ta sauke.
“A haka Amma kike cewa ba zaki dawo ba? Haka zan yi ta zama a gidan nan ina ganin wulakanci kala kala? Idan wannan ya wuce wani zai zo? Tun da kika bar gidan nan ban sake farinciki ba, na koma kamar wata bare kowa taka ni yake yadda ya so”
Ta share hawayenta, ta sake daukar takardar ta karanta, this time around sai ta ji karatun be mata dadi ba kamar dazun ya manta da ita damuwarta ya sauya shafin bakincikin zuwa fari ba, mikewa ta yi tsaye ta nufi gurin da wadacan takardun da ya bata suke ta saka wannan a ciki. Sannan ta dawo ta sauke kayan daga kan gadon ta jerasu a closet dinta ta dawo ta kwanta saman gadon feeling so boring ba tare da dalili ba.
A WEEK LATER…..
Khairy ta cije baki tana jin kamar ta buga wayar a kasa kuma babu dama.
“Haba Adam wani irin careless ne wannan? Na fada maka yau aka sallamo Hajiyata daga asibiti fa, kuma yar’uwata ta rasu ko sati biyu ba ayi ba amman ka kasa daga min kafa wani irin abu ne wannan?”
“Look Khairy na daga miki kafa fa, ki duba tun lokacin da na baki kudin nan, kuma na fada miki nan da 3 weeks zan bar kasar nan, idan na tafi ban samu yarinyar nan ba kin san halin da zan shiga”
“Babu halin da zaka shiga tun da ba tare aka haifo ku ba, kuma ba Hurriya ce kadai yarinya ba, so nawa mutum ke son abu be samu ba kuma ya hakura ni kaina wanda zan aura yanzu ba wani son shi nake yi ba, amman a haka na hakura ba dole abun da mutum ke so yake samu ba”
“Ke dabam ni dabam, and ban ce dole sai na aureta ba since bata so na amman i have to teach her a little lesson ko dan gaba, kuma ki kika kawo wannan bad idea din sai after na saka rai sai kuma ki fara min yawo da hankali”
Ta daga kafadunta kamar yana tsaye a gabanta.
“Amman ai yi aikina na baka kai ya kamata ka yi amfani da damarka ka yi abun da ya dace?”
Ya amsa da karfi.
“How? A kankanen lokaci? Bayan kuma kin san babu yadda za’ayi na iya contacting yarinyar nan”
“Adam ba zaka zo ka tsare ni da fada kamar ubana akan kudin da na fi karfinsa a gidan mu ba, ina cikin nawa tashin hankali da damuwa karka takura min mana idan kudi ne ka zo ka karbi abun ka na huta kai ma ka huta, just because of na kawo idea cewa ba dole sai ka aureta ba zaka iya biyan bukatarka ai na maka hanyar da ya dace ko?”
“Hanyar da kika kawo mummunar hanya ce da zata tana mutunci ni ma, kuma na jawa iyayena zagi, babu wani amfani da za su min”
“Kuma ka yarda ka dauka?”
“Saboda na dauka shawara ce mai kyau da farko, later on kuma na gane bata lokaci ne kawai, yadda zan yi samu magana da ita ma aiki ne”
“Zaka iya zuwa ka saka a sallamo maka ita ka mana ka yi magana da ita”
“Idan kuma na yi haka daga karshe ban zamu biyan bukata ba fa? And i told you ki dauko yarinyar nan ku fito tare kin ki”
“Bata yarda ta fita da ni yanzu, kuma ba zan iya mata dole ba, sannan kuma idan wani abu ya faru a lokacin da muka fita tare ai za a gane cewar ni ce”
“Daman ke kika lalata komai tun farko, kika ce mata ni ba mutumen kirki ba ne and trust me you will regret this Khairy”
“Ka yi duk abun da zaka iya Adam karka fasa, kuma karka sake kirana matukar ba kudinka zaka karba ba”
“Khairy ni zaki fadawa haka?”
Taja tsaki ta yanke wayar ta jefata a kan kujera, cikin wani irin fushi da bacin rai ta ce.
“Hurriya kin haddasa min fitina, ke da uwarki kun hana mu jindadin rayuwar duniya, ban gayyace ki bikin birthday na ba kika je duk shi ne silar, shi kuma ya bi ya haukace sai ka ce ita kadai ce mace a duniya”
Ta zauna da karfi kamar an mata da dole tana jin kamar Hurriya tana kusa da ita ta yi mata shegen duka ko ta rage wannan bacin rai.
“Ban san me yasa ma na karbi kudinsa tun farko ba? Ko zuciyar imani ba shi da ita ji yadda yake takura min kamar be san ayi min mutuwa ba”
Ta sake jan tsaye sai a lokacin tuna da kiran da Hajiya Kaltume take mata, mikewa ta yi tsaye tana fadin
“Gaba daya ya hargitsa min tunani”
Ficewa ta yi daga dakinta nufi dakin mahaifiyarta, ta shiga dakin cikin bacin ran da ya gaga boyuwa a fuskarta.
“Lafiya kike?”
Hajiya Kaltume ta tambaya cikin wani yanayi na rashin kuzari, ta rame kamar ba ita ba bakin fatarka ta karu har ya mata yawa tsabar bakinciki da damuwa. Hajiya Fatee dake zaune gefenta ta tabe baki.