Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
“Ban zan iya fadar wata rana da ka samu matsala da abokinka ba sai yau, duk wannan akan yarinyar da bata kai ta kawo ba ne? Kana kokarin fita hayyacinka, duk wasu abubuw ada ba dabi’unka ba su kake aro ka yafe yanzu! Idan idonka ya rufe ni nawa be rufe ba, ba zan taba karbar yarinyar da duniya ta gama ganin tsiraicin a matsayin suruka ba…”
Be ji zai iya musu da mahaifiyarsa ba, saboda haka ya karasa gurin da take tsaye ya kama hannayenta ya sumbanta yana murmushi.
“Zaki so ta Ammy saboda kina son farincikina, kuma a yanzu farincikina yana tare da yarinyar nan, ba ni da wani buri a yanzu da ya wuce na ga na tsamota daga kogin da aka jefata”
“Wai me yarinyar take da shi ne da babu a sauran mata?”
“Na so wasu matan kamin ita Ammy kin tuna? Har an min baiko da wasu, duka baki ce komai ba ga wannan? Wanda ta fisu komai?”
“Babu wani abun da ta fi su sai tallata tsiraici”
“The more da kike zaginta the more da nake jin kaunarta na karuwa a zuciya, zagin da kike mata ya kara bude min hanyar son taimaka mata”
Kallon rashin fahimtar inda ďanta ya dosa Ammy take masa, cikin bacin rai da daga muryar ta ce.
“Zamu wuce Kaduna gobe”
“Ban samu amincewa daga gurin aikin mu ba”
“I don’t care zamu tafi Kaduna gobe idan hutun da ka rubuta ya kare sai ka dawo”
Yayi murmushi sannan ya wuce ciki, da kallo Ammy ta bi danta, kiyayyar da take yi ma Hurriya a yanzu ba dan tana talaka ne kawai ba, har dan hotunanta sun fita a duniya ne, taya zaka kalli kazantacciya yarinya irin Hurriya a matsayin matar danta guda daya tilo? Duk shekarun nan da ta dade tana jiran zuwan wannan ranar? Ace daga karshe Hurriya ce? Duk matsayinta a idon duniya da yadda mutane suke kallon mahaifinsa? Wai ina kishin danta ne? Taya ya barar da komai idonsa ya rufe akan yarinyar nan? A yanzu ne take ganin ya dace ta yi wani abu saboda haka ta bi bayansa ta shiga dakin da yake, sai ta same shi yana canja riga.
“Captain… We need to talk”
Ya karasa jan rigar kasa ya nufi gefen gadonsa ya zauna yana kallonta. Ta daure ta zauna tana aje numfashi a gurin da ba muhallinsa ba, daga bisani ta saita fushin zuciyarta.
“Magana ce da nake son ka ba ni aron hankalinka kuma ka bude zuciyarka ka karbi abun da nake son fada maka”
Ya daga mata kai yana kara tattara hankalinsa gareta.
“Ba zan hana ka taimakawa yarinyar nan ba idan taimaka mata kake son yi, abu mai kyau amman kar hakan ya saka na manta waye kai, Captain ya kamata ka dawo cikin hayyacinka, ka tsaya ka yi tunani mai kyau yarinyar nan bata dace da kai ba, future dinta ya lalace sanadin haka zai iya taba naka rayuwar, taya zaka shiga taron mutane da fuskar yarinyar da duniya ta gama kallon tsiraicinta? Ni ma ta ya zan kalli kawaye na gabatar musu ita a matsayin suruka?”
Yayi murmushi yana saka hannunsa na dama cikin kishiyarsa wato na hagu.
“Ammy kina so?”
“Wane irin magana ne wannan? Taya zaka tambayi uwa tana son danta musamman uwa irin ni?”
“Dan Allah kin amsa min”
“Ina sonka irin son da babu uwar dake yi ma danta shi”
“Toh dan Allah ki so Hurriya, duk mai so na, kamata yayi ya so abun da nake so, duk wani illarta da zaki ina min a yanzu ba zan gani ba, wata kila sai nan gaba shi ma kuma bana fata”
“Ta ya soyayya zata rufe maka ido, ka kasa yin biyaya ga mahaifiyarka Jamal? Akan yarinyar daka hadu da ita da girmanka? Ka bijirewa mahaifiyar fa ta haife ka ta yi wahala da kai? Ko dan saboda kai kadai Allah ya ba ni shiyasa kake min haka?”
Ta karashe maganar idonta na cika da kwalla. Ya kalleta da fuskar da babu wasa a cikinta.
“Zan hakura da Hurriya Ammy, matukar hakan shi ne zai faranta ranki, na hakura da ita Ammy, soyayya ta yi kadan ta yi min irin wannan rufin, zan hakura da nawa farinciki”
Ta share hawayenta tana murmushi ta dafa shi.
“Allah ya maka albarka, ba zaka gane amfanin abun da na yi maka ba sai nan gaba, yarinyar ba ta dace da kai ba, be kamata ta zo a matsayin surukar mu ba”
Ya daga mata kai yana murmushi kadan, sannan ya sauka daga kan gadon ya zauna a kasa ya kama kafarta ya rike.
“Ina rokon alfarmar ki bar ni na karasa aikin da na dauko, na yi ma yarinyar nan alkwarin zan gyara mata komai, shi wannan karki hana ni Ammy”
Ta kama hannunaa da sauri cikin farinciki.
“Ba zan hana ka ba, na amince ka taimake ta, matukar ba zaka auro min ita a matsayin mata”
“Na gode”
Yayi mata godiya ransa babu dadi, domin a iya gaskiyarsa yayi mata alkawarin hakura da Hurriya saboda bata sonta, ba zai zabi farincikinsa sama da na mahaifiyarsa ba, sai dai yayi ma kansa wani alkawari daya zai taimaki Hurriya zai cireta a damuwa kamar yadda ya fada.
“Daddy yana nema na bari na shiga dakinsa”
“Yana can bangaren mahaifiyarsa, dazun sau biyu Bashir Sarauta na aiko masa da mutane yana neman ka ba shi dansa”
Be ce komai ba ya dauki wayarsa da keys din Nene dake kan gado ya fice daga dakin, gaba daya sai yanayinsa ya sauya, rashin kuzari da walwala sun tattara a fuskarsa da jikinsa. Kamar wanda aka yi ma mutuwa haka ya shiga bangaren kakarsa dake cike da mutane a falon da yaranta da jikokinta cikin ƴaƴanta har da Daddy dake zaune kusa da ita. Kowa zai iya shaidar Captain baya cikin farinciki domin abun a bayyane yake a fuskarsa balle kuma mahaifinsa da ya fi kowa sonsa.
“Ina makullin motata? Ashe fitina zaka je ka tayar shi ne ka karbi motata?”
Nene tana maganar tana kallonsa, sai ya karaso ya mika mata key motar ba tare da yace komai ba, sannan ya nemi gurin ya zauna yana mamakin kansa da ada ne idan aka bata masa rai kadan sai yayi kamar zai tashin kowa balle kuma babban abu kamar wannan, amman a yanzu ya kasa yin komai sai ma sauyin yanayi da ya zo masa.
“Jamal…. Lafiya?”
Nene ta tambaya mahaifinsa kuma sai kallonsa yake yana karantar damuwarsa. Captain ya kalli Nene ya kalli kowa dake falon sannan ya mike tsaye
“Ba komai, Daddy ka ce kana son ganina?”
Momy Ikilima ta ce.
“Captain akwai wata matsala ne?”
Ya girgiza mata kai alamar babu. Daddynsa ya sauke ajiyar zuciya cike da kulawa ya ce
“Shiga ka jirani a falon Hajiyar Maru”
Ya amsawa Daddy da kai sannan ya fice daga dakin.
“Baka tambaye shi ina ya kai yaron mutane ba? Kuma na ga yanayinsa kamar da matsala, Allah yasa ba kashe shi suka yi ba, kasan zuciyar Captain fa idan abun ya motsa baya iya rike kansa”
“Zan yi magana da shi Hajiya zan ji ko minene”
Daddy ya mike tsaye ya fice daga falon, kowa sai mamakin yadda yanayin Captain ya canja. A falon Hajiyar Maru wato step mother dinsa Daddy ya samu Captain zaune ya soke kai kasa yana jiransa.
“Karantawa min abun da ya saka ka cikin damuwa?”
Daddy ya tambaya tun kamin ya zauna. Captain ya dago ya kalli Daddy ya fara magana da muryar da ke kara bayyana damuwarsa.
“Ammy ce….”
Ya fada masa abun da ya faru tsakaninsu ya kuma jadda masa cewar ya hakura da Hurriya saboda mahaifiyarsa. Daddy yayi murmushi ya kawar da kai kamin ya juyo ya dauko masa zancen daukar Adam da aka yi, a nan ma Captain be boyewa mahaifinsa komai ba, har video da ya dauka na Adam sai da ya nuna masa.