VENNETE
Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel

“Munafuntata ka yi Captain? Ka ce min ka hakura kuma sai ka juya ka shirya wani abun da mahaifinka?”

Cikin kuka Ammy take tambayarsa, sai ya bude idonsa da sauri ya kalleta raunace.

“Wallahi Allah ban san komai akai ba Ammy”

Hajiya Turai ta juyar da dubanta gurin Daddy.

“Saboda me? Saboda me zaka aura masa wannan yarinyar? Be fada maka ya hakura ba? Baka duba illar hakan ba a cikin zuri’arka?”

Daddy ya daga mata tsaya uku yana nuna mata daya vayan daya.

“Saboda na isa! Saboda yana sonta!! Saboda Allah be haramta ba!!! Kin ga dalilin nan uku su suka saka na je na nemi auren Hurriya a yau, mahaifinta kuma ya bukaci a daura auren a yau”

“Ikon Allah abu dai kamar a shirin film?”

Cewar Nene, Momy Ikilima ta ce

“A littafi dai wannan ai ya fi karfin shirin film”

Ammy da idonsa ya cika da hawaye har wasu za su zubo ta hau masifa.

“Da alama baka yi bincike ba kamin ka aura masa yarinyar nan, mahaifiyarta aikin gida ta yi fa!, ni ba zan iya karbar ta a matsayin suruka ba, ba zan ina nunawa duniya yarinyar nan a matsayin matar Captain ba”

Daddy nade babbar rigarsa.

“Kin gani Turai ba a daura auren yarinyar da Jamal ba sai da na yi ma mahaifina alkawarin zan rike yarsa da mutunci da amana, kuma a matsayinki na matata idan ba ki taya ki cika alkwarin nan ba, to be kamata ki barar da shi ba, karki zuga kanki da yawa ki kone kanki ta hanyar haramta abun da Allah ya halatta, hargaginki da kumbar baki ba zai saka Jamal ya saki yarinyar nan ba, domin ba je na auro masa yar mutune saboda ya zubar min da mutunci ba, ina ce Alhaji Haruna ma yana da kalar nasa rufin asirin idan kuma kin raina arikin gidansu ne yanzu danki take aure make her a billion naira”

“Wayyo Allah na wannan wane irin abun kunya abun bakinciki ne? Kenan duk abun da Jamal yake so sai mu biye masa mu aikata ko da halaka ce? Yarinyar da kare da mage suka maganin siraicinta, ita zaka hannu biyu mu karba a matsayin in-law?”

“Wannan kuma ďanki kike ci ma mutunci a gaban familynsa, ina jiye miki tsoron ranar da zaki yi nadamar nuna son zuciya fiye da abun da danki yake so, ki shirya da wuri karfe biyar jirgina zai tashi”

Daddy na kaiwa ya kabe rifarsa ya fice daga falon, Hajiya Turai ta kalli Nene da kowa dake falon tana kuka.

“Nene kina gani? Babu wanda zai ce komai ni za a bari da fadan nan?”

“Hajiya Turai me kike son mu ce? Aure ne an riga da an daura, sakawa zamu yi Captain ya sake ta ko kuma mijinki zamu rufe da fada, kowa a nan yayi mamaki amman abun da kaddara ta aiko dole mu karba mu zuba ido mu ga abun da Allah zai yi a gaba”

Cewar Alhaji Munzali, kamin ya mike tsaye ya fice daga falon. Alhaji Sadiq ne kadai yake lallabata.

“Ki yi hakuri Hajiya Turai, ki bi abin da danki da mijinki suke so, ki zuba ido ba fata muke ma amman idan akwai illa a cikin lamarin nan za su gani a gaba kuma su gane sun aikata kuskure, Jamal dai shi yake auren yarinya shi yake jin zai iya daukar komai da ya shafe ta to ke mike naki a ciki? Ki yi hakuri a matsayinki na uwa ki danne duk abun da kike ji dan Allah”

“Ba zan iya ba Alhaji Sadiq, Engr ya nuna min ba ni da muhimmanci a rayuwarsa da ta dansa, shiyasa be duba shawarata ko ra’ayina ba ya aikata abub da ya aikata”

Ta fice daga falon tana kuka, Hajiyar Maru wacce ta kasance abokiyar zaman Nene ta bi bayanta tare da Momy Ikilima, Alhaji Sadiq da Alhaji ya dafa kafadar Captain yace

“Ka dauko wani aiki mai nauyi Jamal, idan baka yi hakuri ka kai zuciya nesa ba ba zaka iya karasa ba, ka bawa kowa hakkinsa matarka da mahaifiyarka, Allah ya bada zaman lafiya ya hada kanku”

Ficewa suka yi daga falon sai ya rage daga Captain sai Nene a falon har jikokin Nene yan matan da kanana duk babu ko daya.

“Ka yi hakuri Jamal kowa ya ce zai iya sai an gwada aka ko zai iya dauka saboda haka ka saka kana’a a zuciyar…. ”

Sakin baki ta yi tana kallon ikon Allah ba tare da ta karasa maganar ba. Gira Captain yake daga masa ya sumbanci goro da dabino da Daddy ya ba shi, sannan ya zuba shi a alijihu ya bude babban rigarsa yana nufar ina da take da rawa. Nene ta rike baki.

“Ah…ah… Ah… Ja’irin yaro? Wato ni ka raina ko? Kake min rawa me yasa baka yi ba a gaban iyayenka”

“Su ai iyayena ne, ke kuma kakata ce my first wife my kalbi”

“Tsohon makiri, amman tsaye ka yi a gabansu ba wani murna ba komai kamar wanda aka yi ma auren dole, ashe kana so….”

Ya kyalkyale da dariya ya sumbanci kumatunta.

“Nene na godiya da kika haifo min gwarzon namiji kamar Daddy, ba dan shi ba da yanzu na rasa yarinyar nan”

Nene ta kai masa duka a fuska.

“ja’irin yaro, amman kai da gaske baka ganin illar abun da yarinyar nan ta yi?”

“Bata aikata ba sheri aka yi mata, kuma asiri zai tonu nan ba da jimawa ba, kowa be wuce kaddara ba hakan zai iya faruwa da ni, ko da wani a cikin jikokinki sheri ne aka yi mata saboda a lalata sunanta”

“Haka ne, abun kam babu dadin ji babu dadin fadi, amman na tausaya mata matuka”

Captain ya daga hannayensa sama fafaren hakoransa na bayyana yayi ma Allah godiya.

“Allah ka ba ni ikon kyautata ma yarinyar da daukar nauyinta yadda ya dace, ka ba ni ikon faranta mata, ka taimaka min gurin tarbiyarta da na yaran da zamu haifa Allah, ya Allah ka karkato da zuciyar mahaifiyata da hankalinta ta fahimce kuma ta so abun da nake so, Allah ya ba mu zaman lafiya ka kawar da shaidan da mahassada a wannan aure”

“Ameen”

Nene ta amsa masa tana kallonsa cike da burgewa.

“Kana da hankali matuka Jamal, ba dan kana jikana ba hakika wannan yarinyar ta yi dacen miji, matukar ba zata fusata ka ba to zaku zauna lafiya da ita”

“In shaa Allah Nene”

Ya kara taka mata rawar sai a lokacin yake jin wani kalar farin ciki da be san a muhalin da zai aje shi ba, a lokacin ne wani shaukin auren da annashuwa da zumudi suka same shi. Hanyar da dakinsa yake ya nufa yana tafe yana gyara babbar rigar abun ka da wanda be saba saka manya kaya irin wannan ba. Agaban madubi ya zauna yana shafa fuskarsa ya dauki ragowar tutaren ya feshe a jikinsa, wani irin yanayi yake jin kansa da be taba samun kansa a ciki ba, yanayi ne dabam da yake zuwa sau daya a rayuwar ko wane saurayi fa budurwa, yanayin da kan canja yanayin ango da Amarya tun daga yanayin gari har zuwa na hallita da mu’amala da kuma na iskar da aka shaka. Hoton da ya dauka na Hurriya ya kama a wayarsa yana kallo yana shafa screen din da hannunsa.

“You’re the only thing i want touch…. Kin kawo ni a wata duniya da ban yi mafarkin zuwanta a kusa ba, kin haska min abubuwa da yawa da duhun watan soyayyarki bata bari na gani ba, zan baki kyauta duniyar dake cike da haske da farinciki sai na dawo miki da abubuwan da kika rasa, bakinciki da kike ciki zan maye miki gurbinsa da farinciki, zan canja shafin rayuwarki har ki bata damuwa baya, zaki gode Allah ki yi alfahari da ya baki ni a matsayin miji…. QURRATUL AYN (meaning
Delights Of The Eye, Darling, sanyin idaniya…)”

Ya sumbanci hoton sannan ya dorashi a kirjinsa ya rumgume ya lumshe ido yana murmushi, a zuciyarsa yake ayyana Hurriya tsaye a gabansa tana kallonsa da murmushi a fuskarsa fararen tufafi sanye a jikinta.

“Ya… Ya… Ya… Na.. ”

Ya ji yana fitowa between her soft lips tana motsa halshenta a hankali.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Adblock Detected

Ad Blocker Detected