Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Hajiya wannan fa ba wasa ba ne, abu ne da na gani da idona, and she’s my friend muna daf da kare karatun nan take suka hadu, tana da va ni labarinsa but ban dauka Appa ba ne sai yau da muka sauka airport”
Hajiya Kaltume ta karkata da kyau tana kallon Salma dake magana with full confidence.
“Motar da ta dauke ta ma daga Airport ta kaita gida, Appa ya kawo, ban kara yarsa shi din ba ne har sai yau da ta fada min cewar shi ne mamallakin Yadi’s Motors”
“Ho… How… How… Comes….”
Cewar Khairy tana kallon yar’uwarta.
“Boye min ta yi, amman ta fada min cewar yana da mata biyu ya saki 3rd wife dinsa yana da yaya maza hudu dayan ya rasu, yana da yan mata bakwai, amman na zama wata sakarai da ban gane ba har sai a yau da ta fada min wai sunan wanda take son ta aura Alhaji Haruna Mai Yadi, and she was telling me shi ya aiko da motar nan a dauke ta”
“Amman baki mareta ba? Ta fa san mahaifinki ne?”
“Ban mareta ba, amman na fada mata zata jefa kanta a matsala ne kawai dan haka ta rabu da mahaifina tun wuri, ni babu abun da ya fi bata min rai ma kamar yadda na zama sha sha ban fahimci mahaifina ba ne har sai da ta fada min, bayan kuma ita din ta sam cewa mahaifina ne domin sunana Salma Haruna Mai Yadi, and the most annoying part is yarinya ce kamar ni sai barikin tsiya”
Hajiya Kaltume ta girgiza kai.
“Aa ni dai ban yarda da wannan ba, ko dai akasi aka samu ko kuma wani abun ya hada su take zaton sonta yake, amman ni na san dalilin da ya saka mahaifinku ba zai kara aure ba, kuma idan har zai kara din zan riga kowa sani”
Salma ta yi dariya.
“Okay idan baki yarda ba, zan baki duka nunbers dinta ki saka a wayar Appa, ko kuma ki kawo ni na saka ko Khairy ko kuma ki yi wata dabara mu duba Instagram chat dinsa dan na fi kyautata zaton nan suka hadu”
Khairy taja tsaki.
“Ni Wallahi wannan auren auren na Appa yana damuna, daman tun da na ga gidan nan da part hudu na san yana da burin karo wata, kuma yanzu Fisabilillahi ace sa’ar yarsa kawarta ma? Haba…!”
“Wannan burin ada ne ba, ba yanzu ba duk wacan rayuwar ta kau, ku kwantar da hankalinku babu wani aure da zai kara, ni ban ma yarda zancen aure ne tsakaninsu ba ko soyayya”
Cewar Hajiya Kaltume tana murmushi, sannan ta mike tsaye yana fadar.
“Yanzu dai an huta yar’uwar shawara ta dawo, sai ku shirya duk abun da kuke ganin ya dace, zan sanarwa Appanku kamin Iyayen Fadeel din su zo”
“Hajiya Fadeel dai? Yana da mata fa? Kuma kin san yadda sherin kishiyoyi suke tun da muna cikinki”
Taku kadan Hajiya Kaltume ta yi ta dafa kafardar Salma fuskarta da murmushi.
“Kyakkyawar makoma ake buri, bana fatar kowa ya sake yin irin auren da Maama ta yi, tana can yana gana mata azaba, matarsa ba matsala ba ce domin Hajiya Fatee bata sonta, kuma saboda matarsa take son ya auri Khairiya saboda Khairiyyah ta share mata hawayenta, fata muke kamin ma ta shiga cikin gidan matarsa ta fice”
“Idan ta fita kina ganin Khairy zata iya rainon yayanta? Kuma yadda Hajiya Fatee ta tsani matarsa zata iya juyowa ta tsani Khairy fa…”
Khairy ta kada kai kamar kadangaruwa domin an taba mota gurin da yake mata kaikaiyi.
“Shi nake kokarin nunawa Hajiya ta gagara ganewa, ni har yanzu Fadeel din nan be kwanta min a rai ba”
“Ku yara ne ba zaku gane ba, gaba nake hango muku Hajiya Fatee kuma bata isa ta tsani Khairy ba har abada, kar ta san kar ne ni da ita, kuma ba ido zan zuba mata ba, tun kamin a tafi ake shiri ba sai an dawo ba, dan haka ki kwantar da hankalinki Khairy ki saki jiki ki saka kaunar Fadeel a ranki”
Salma da Khairy suka kalli juna kamin su kalli Hajiya su saka dariya, ita kuma ta yi murmushi ta fice ta bar musu falon, su suna dariyar ta kasa fahimtarsu kuma duk yadda take ganin abun zai zo da sauki ba zai zo, ita kuma tana murmushin abun da take hango ma Khairy wanda ta kasa ganewa.
“Hajiya ba zata gane ba”
Salma da har lokacin dariya take ta ce.
“Ina fa, kin ga ko maganar Appa musawa take yi, kuma Wallahi gaskiya ne, haka ta yi a auren Maama tana cewa tana hango mata jindadi ne saboda yana da kudi gashi nan yanzu kullum da kalar azabar da yake nuna mata, last week na muna chat take fada min yanzu har mata yake kawo mata a gida idan ta fita”
“Kullum fa iskancinsa gaba yake, ni ba zan ma iya daukar wannan iskancin da yake mata ba, ita kuma kamar an mata magani ta kasa rabuwa da shi”
“Ni kaina ba zan iya ba, kuma wai Hajiya ta kyaleta sai iskanci yake ma mutane yadda ya ga dama”
“To ya za’ayi idan ace za a masa magana ita take shiga ta tare, kar a taba mijinta wata kila sai da ya mallaketa sannan ya aureta”
Salma ta tabe baki ta sauka daga kan kujerar ta zauna a kasa.
“Ke ba ni labari ya aka yi Hurriya ta bar gidan?”
Sai da Khairy ta kalli kofar falon dan tabbatar da Yayansu ba zai shigo ba sannan ta fara bata labaran abubuwan da aka yi bata gidan.
HURRIYA POV.
Jerowa suka yi suna tafiya yana ta yi mata nasiha a matsayinsa na yayanta.
“Wallahi Yaya duk yadda kuke tunanin abun yake ba haka ba ne, ni bana munafurci ko zancen Abban su Husna ni da ita kawai na san na yi magana kuma maganar karatu kawai muka yi sai take ce min lokaci yana kurea na fada mata Appa nake jira, ban san yadda aka canja zancen ba abun har ya kai mahaifinta ya samu Appa da maganar”
“Wacan ya wuce, komai ya wuce yanzu kawai ina jan hankalinki ne akan rayuwa, duk wani abun da kika san zai janyo miki magana ko ya bata tsakaninki da mutane ki daina kuma ki gujeshi, ina yabonki Hurriya shiyasa idan aka fadi cewar kin yi wani abu nake musawa ko na yi mamaki saboda na san ba halinki ba ne, dan Allah ki natsu ki daina duk wani abu da be dace ba”
“Ba zan sake ba Yaya ba zaka sake jin an fadi wani marar dadi kaina ba na maka alkawari”
“Yayi kyau, in kin shiga ciki ki ce ina gaishe da Momy”
“Toh Yayana na gode”
Ta wuce ciki shi kuma ya juyo ya dawo bangarensu sai dai be shiga ciki ba ya shiga motarsa ya bar gidan. Sai da Hurriya ta maida kofar falon ta rufe sannan ta lura da Husna dake zaune akan sofa tana sanye da farar abaya. Da gangan Hurriya ta dauke mata kai zata wuce Husna ta yi saurin riketa tana dariya.
“Fushi kike yi da ni saboda ban zo ba kwana biyu?”
Hurriya ta cire hannunta daga jikinta fuska a daure ta ce.
“Ba saboda haka nake fushi dake ba, ina fushi da ke ne saboda kin hada ni da iyayena, abun da kike yi sam be dace ba Husna saboda na yarda dake na saka nake fada miki sirrina ashe fitarwa kike gashi nan kin yi sanadinyar da Appa ya koreni a gidan nan yau na dawo, kuma kowa a gidan nan yanzu ya tsane ni yana min kallo da munafuka”
“Innalillahi ni kuma, dan Allah ki tsaya mu yi magana ta fahimta Wallahi ban yi miki wani sherin ba, kuma mahaifina be zo gidan nan da wata manufa ba, dan Allah mu tafi dakinki mu yi magana…”
Hurriya ta tsaya kallonta kamin ta gyara tsayuwar gilashin idonta ta nufi stairs, Husna ta rufa mata baya, dakin suka shiga suka rufe sai after sun zauna Hurriya ta fada mata abun da ya faru.
“Innalillahi, Wallahi Hurriya ba ma ni na fadawa mahaifinmu ba, Umma ce ta fada masa kuma ita ma ta yi hakan ne saboda tana tausayinki, su a nufinsu idan Appa ya amince sai su dauki nauyin karatun har ki kallama ganin kamar ba a son ki yi karatun, ni ma kuma ban san suna da wannan manufar ba sai bayan sun aikata Umma take fada min wai Abba ya samu Appanku da maganar be amince ba, sun ma yi rabuwa marar dadi, dan Allah ki yi hakuri kar ki mi dawowa fahimta baibai, ban shigo ba shiyasa ban san abubuwan da suka faru ba”