Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Me ya fito dake to?”
“Ni na gaji ne bana son zama ciki gida nake so, kuma su ba su gama bikin ba babu wanda zai kawo ni”
“Okay ki koma ciki gani nan zuwa”
“Toh Yayana ka yi sauri ance I’m not safe here”
“Waya ce haka?”
Ta kalli mutumen dake jiran ta ba shi wayarta.
“Adam”
“Wane Adam”
“Ni ma ban san shi ba, yanzu na hadu da shi”
“Okay ina kusa da gurin koma ciki zan zo na dauke ki”
“Toh”
Ya kashe ya mika masa wayarsa.
“Thank You”
Ta juya ta cigaba da tafiyarta har ta koma ciki, wannan karon masu gadin ba su hanata ba domin sun gane ita ce ta dazun. Ciki ta koma ta samu gurin inda ba za a ganta ba ta zauna ta zubawa kofar shigowa ido Yayanta kawai take son gani. Tana hango Adam ya shigo ta kara boya kamar ta san ita zai fara nema, sai ko ya hau rabon ido yana neman inda zai ganta, gaba daya ta tafi da shi, a gurinsa duk abun da take tana masa yanga ne saboda ta ga tana da kyau. Ta yi rabin awa a gurin sannan ta tashi ta nufi kofa kamar mai shirin sata ta fice tana duddubawa ko Yayanta ya zo, aikuwa ta yi sa’a tana fitowa motarsa na shigowa harabar da sauri ta nufi shi yana fakawa ta bude front seat ta shiga.
“A tsorace kike Hurriya me ya faru?”
Ya tambaya yana kokarin kashe motar.
“Ba komai ni gida nake so”
“Ina Khairi ita da waye a gurin cikin yan gida?”
“Yaya Namra kawai na gani, sauran duk kawayenta ne ban sansu ba”
Ya duba agogo hannunsa.
“Su ma ai ya kamata ace kowa ya tafi gida yanzu, Je ki kirata”
“Yaya ba zata fito ba, kuma zata ce na bata mata birthday fa”
Ta saka mishi kuka domin ta san halin Khairy ko a banza ta dora mata laifi balle kuma da dalili.
“Karki ce ni nake kiranta, ki ce wani ne yake kiranta, idan ba haka ke ma sai na bata miki rai”
Ta fita motar ba dan ta so ba sai dan Yasir yayi mata dole, ciki ta koma ta isa har gurin da Khairi take tana rawa ana zuba mata kudi ta rikota ta kai bakinta kunneta.
“Wani yana kiranki a waje”
“Waye?”
“Ban san shi ba”
“Je ki ce masa ya shigo ciki”
Hurriya ta juyo, ita dai bata san yadda aka yi masu gadin suka bar Yasir ya shigo ba, sai hangon shi ta yi ya kankance ido yana kallon mutanen dake ta kai da kawo a gurin. Ta nufi shi ma ya nufo gurin Khairy da bata san me ke faruwa ba sai rawarta take ana zuba mata kudi. Galala Hurriya ta yi tana kallonsa ganin ya wuce ta ya nufi gurin Yayarta, yana isa be tsaya komai ba ya dauke Khairy da mari ya fara dukanta kamar an zugoshi.
“Wannan iskacin ne birthday? Kin mai da kanki kamar yar kafirai? Babu mutum daya mai mutumci a nan kim hada maza da mata ana shashanci ki cw birthday? Daman sai na hana Hajiya ta ce sai an yi saboda kawai ku ja mana zagi”
Dukanta yake ta ko’ina wadanda suka san yayanta suka fara ficewa da sauri, wasu suka suka fara kai mata dauki ciki har da ma’aikatan gurin.
HAJIYA KALTUME.
“Hello”
Hajiya Fatee ta amsa daga dayan bangaren.
“Hajiya ina ta kira baki daga ba”
“Yanzu na shigo dakin, kin gan ni garin sauri har faduwa na yi kamar an turo ni”
“Subhanallahi, sannu daman ina ta kira na ce miki Fadeel zai zo”
“Ya ma zo har ya tafi, ya ce wai kin ce ya zo ya kai Khairi bata samu mota ba”
“Eh haka na ce masa saboda na samu ya zo, wato Hajiya akwai abun da nake tunani sai dai gan gama yanke shawara ba sai kin zo, shiyasa da kika fada min zata birthday na fara da wannan”
Hajiya Kaltume ta yi murmushi tana murza kafarta dake zogi.
“Toh Hajiya Fatee kenan wato idan hagu ta ki a koma dama”
“Kwarai kuwa, idan ba zai iya rabuwa da wacan bakar karyar ba da ta dafa ta ba shi ya shanye, to ya karo wata idan ya auro wanda nake so ko da bakinciki ai sai ta bar gidan”
“Wato Hajiya Fatee magana nan ba ta waya ba ce, bari dai sai na zo kawai ko kuma idan kin shigo”
“Toh shikenan Hajiya sai mun hadu”
Ta sauke wayar tana murmushin jindadi, domin an yi tsara akan gaba Khairy ta kamalla karatu daman kuma can tana sha’awar hada jini da aminiyarta ko dan karfafa zumuncinsu.
**** **** ****
Hajiya Fatee ma da murmushi ta sauke wayar, sannan ta fito falo ta zauna tana ta sake saken yadda zata kara bullowa lamarin. Domin ta san ba karamar wahala zata sha ba kamin ta samu kan danta Fadeel ya yarda zai aure, a ganinta mallakar da Afrah ta yi masa ba karama ba ce ta yadda ta hana idonaa ganin ko wace mace sai ita kadai.
“Sallamu Alaikum”
Ta dago tana amsa masa.
“Wa’alaikassalam har ka dawo?”
“Eh ko da na je Already ta wuce ma”
Ta yi tusar baki tana jin rashin dadin bw tarardar Khairy ba.
“Aikin banza, zuwan kawai ka yi kenan”
Ya yi dariya yana saka keys din hannunsa ya taba kunnensa.
“No na sauke kanwarta yar farar nan ita ce bata samu mota ba, sai na kaita”
“Oh yar makauniya? Ko yar wajen Hajiya Nafisa?”
“Tana gani Hajiya fa”
“Amman sai da gilashi ai, ita da makafi duk daya, Allah yasa dai ka shiga ciki”
Ya yi fuskar mamaki.
“No why would i?”
“To wish her happy birthday mana, kuma Allah yasa dai baka je mata hannu sake ba”
Ya zauna yana dariya.
“Hajiya Khairi kanwata ce fa, kuma ban ma san tana birthday ba, sai da kika kira ni kika fada min naje na daukota, ban shirya komai ba”
“Toh sai ka shirya wani abun ka kai nata daga baya, ko tana kanwarka ai tana sin kyautatawa”
“Yanzu kuma ai ya wuce, sai da mu hari gaba kuma”
Ya mike tsaye yana cigaba da wasa da keys din hannunsa.
“Bari na tafi na bar aiki a office”
“Wane irin aiki yanzu da yamma, wai shike nan ba dama na zauna na yi hira da kai sai ka ji kamar kama kan kaya, yar hirar ma sai a hana ka?”
“Waye zai hana ni hira dake duk duniyar nan Hajiya?”
Ta tabe baki ta dauke kai.
“Dan Allah karki ce Afrah bata ma san na zo nan ba, ki daina dora mata laifi kina daukar alhakinta ne kawai”
“Kullum ai ni mai daukar alhakinta ce, daman ta ina Afrah zata yi laifi a gurinka? Yar zinari, ina dai son ka sani ni uwarka ce ko kana so ko baka so, matarka bata fi ni matsayi ba”
“Ai ba za a ma hada ba, babu mai matsayin uwa a duk duniyar nan Hajiya, amman duk da haka tana da nata iyaka mata ma tana da muhallinta, ban san miyasa kika tsani mutanen Afrah ba, yarinyar nan tana mutuntatako daidai gwargwado tana miki biyayya”
“Na ji dan Allah kama hanya ka tafi Allah ya bada sa’ar aiki”
Rokonsa take har da hade hannaye. Ya sauke ajiyar zuciya cikin yanayi na damuwa ya koma ya zauna domin ba zai iya barin gidan ran mahaifiyarsa a bace ba.
Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.
Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo…
“Ka tashi ka yi tafiyarka bana bukatar zaman ka daman ai bana da muhimmanci a gurinka, da ina da muhimmanci ba zaka wulakanta ni ba”