Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
“Miye na yi ma mutane bachi a kujera kin wani takure salon wani ya shigo ace ke ce marar gata a gidan ke ga munafuka, wato kin dawo babu zaman lafiya, mun rabu da Hamad ke kuma zaki kirkiri mugun abu ko?”
Kamar wani mace haka yake fada da ita yana gautsina fuska, gently ta mike tsaye domin ita ma bata san bacci ya dauke ta sai da ya tasheta. Tafiya ta fara yi ta haye sama ta dade a tsaye tana kallon kofar dakin Hamad tana jin kamar idan ta tura zata ganshi kwance ya ba kofar baya kamar yadda ya saba kwanciya. Wani hawayen ya sake cika idonta wani abu mai kama da dutse ya tsaya mata a tsakiyar zuciya ya mata nauyi. Cikin karfin hali ta kai hannu ta tura kofar dakinta ta shiga sai da maida kofar ta rufe ta jingina jikin kofar ta rumgume hannayenta not knowing what to do ita dai ba kuka take ji ba a yanzu, hawaye ne kawai ke mata zuba, tunanin dake mabanbantan duniyoyi ya hade mata guri daya, idan ta tuna Hamad ta tuna Amma, ta tuna Appa. Jin ta yi an yi knocking kofar dakin wani abu mai kama da tsoro ya fisgeta ta tashi tsaye da sauri jikinta na rawa ta yi baya tana kallon kofar, Namra ce ta turo kofar ta shigo da far’arta.
“Hurriya kin dawo”
Kamin ta rufe baki Yasir ya shigo cikin yanayi na damuwa yana kallonta.
“Hurriya”
Ta kasa amsawa Namra balle Yasir da ya shigo bayanta, ta hade yawu da karfi tana kallonsu. Yasir ya nufi gadonta ya zauna ya rasa me zai ce mata shi kansa be jin dawowarta gidan a yanzu mafita ne a gareta, babu yadda be yi ba wajen ganin ya fahintar da Hajiya Kaltume akan ta hana Appa dauko ta amman ta kasa fahimtarshi.
“Hurriya zauna”
Ta zauna a gurin kamar wata wadda tunani ya birkicewa kwakwalwa. Namra dai ta tsaya jikin kofar ita ma tara ran duk babu dadin ganin yar’uwarta cikin damuwa.
“Hurriya ki yi hakuri dan Allah, idan kina kukan nan sai ki saka kanki a damuwa”
Yasir ya daga ma Namra hannu alamar ta daina maganar sai ta yi shuru ta juya ta fice daga dakin, dan zumudin da ta zo da shi na murnar dawowar Hurriya sai ya gushe.
“Hurriya kina son zama nan ko kin fi son zama gurin Amma? Idan gurin Amma kike so zan mu tafi tare da ni dake mu yi ma Appa magana, idan be amince ba sai mu fadawa Hajiya Binta”
Ta girgiza kai alamar bata aa.
“Kina son zama nan din?”
Ta daga masa kai.
“Shi ke nan zo ki kwanta, kin yi sallah ko?”
Ta amsa masa da kai sannan ta nufi gadon ta kwanta shi kuma ta tashi ya fice, kai tsaye bangaren mahaifinsa ya nufa sai dai yayi rashin sa’a be tararda shi ba, domin tuni ya fita after ya kai Hurriya bangaren Momy daman ita kawai yake jiran a dawo da ita gidan ya fita, saboda Hajiya Kaltume ta fada masa idan be yi da gaske ba Amma ba zata ba shi Hurriya ba.
Hurriya bata tabbatar da mahaifinta ya daina yayinta ba sai da ya canja mata makaranta ya saka ta makarantar government, yayinda sauran yan’uwanta da suke ajin karshen a private school suke can suna karatu. Ita kuma aka bata direba daya da zai rika kaita makaranta yana daukota ita kadai, ba karama ta kaddama aka yi ba kamin Appa ya saka ta government school, domin malaman dake karantar da ita a private school suna sonta sosai saboda kokarin da take da shi, ga kuma gasar da suke ta shirye shiryen turata. Har komiti suka hada na manyan makarantar suka zo har gida suka tarardar Appa suka tattauna da shi tare da nuna masa illar cire Hurriya a makarantar amman ya ki saurarensu saboda Hajiya Kaltume ta ba shi shawarar kaita makarantar Government, daga karshe ma sai suka rabu cikin rashin dadin rai domin Appa rufe su yayi da fada ya nuna musu Hurriya yarsa ce shi ke da iko da ita babu wanda ya isa ya fada masa me zai yi akan yarsa hukuncin da ya yanke ke nan kuma babu fashi.
Ta bangaren Hurriya ma hakan ya taba ta sosai domin yin sabin abokai da kuma canja wasu abubuwa na karantu domin malaman ba daya ba be ya zama abu ne marar sauki a gareta, hakan sai ya saka ta zama weak ta yadda bata iya maida hankali ta yi karatun yadda ya dace, gaba daya ta koma kamar ba ita ba, karatun da take ganewa a can bata ganewa yanzu, sai ayi darasi a gama bata fahimci komai ba, tunani da damuwa suka taru suka yi mata yawa, gashi kullum ita ce cikin kebe kanta bata son shiga cikin yan makarantar da bata saba da su ba.
**** **** ****
Hindu ta mika mata jaririn dake kuka.
“Iyami ina ta fada miki banza bata fitar da ke gidan Alhaji, amman kika sa kafa kika yi biris da maganata, yanzu gashin bayan fitar da ke ta dauke hankalinsa daga kan Yayansa, bayan an a kashe miki daya, kuma han karbe dan abun da yake hannunki, ina dadi ka haihu gari daya da miji amma yaki ya tako ya duba yara, ke da da ns yadda Alhaji yake sonki ai kin Allah kadai ya san yadda zai rika dauki yana hauka kin haifa masa yaya biyu kuma maza”
Amma ta Hamid dinta dake shan nono ta ce.
“Hindu ban saba irin abubuwa nan ba, ni Wallahi ban san kowa mai irin wannan aikin ba, kuma ni ina tsoron kauce hanya”
“Babu zancen kauce hanya, ai ba shirka zamu yi ba, kuma ba cewa zamu yi ayi mana na Sherri ba, aa mu dai kawai a karya sihirin da ta yi miki da na yayanki hankalin mijinki ya dawo ki koma gidansa ki rike yayanki, domin nan gaba kadan ma zai iya cewa su ma wadannan karbe su zai yi, tun kina cikin idda na so a nemi taimakon nan kika ki gashi yanzu har sai an sake daura aure”
“Hindu da dai mun hakura, komai fa yana da iyaka wata rana zai karye ko da ba ayi komai ba indai asiri ne.”
“Toh shi ke nan zauna a gurin, kina sakawa zuciyarki bakinciki ki lalace a banza ki zama bar tausayi daman haka suke so, yar ki kuma ta koma yar aikin gidan, idan ma ta yi sa’a kenan ita ma ba su kashe ta ba, nan gaba kadan idan ta girma ki rasa wa zai aureta, domin Wallahi ba zata yarda Hurriya ta yi aure ba ga nata yayan ko da kuwa sun yi aure, yanzu kina kallon yadda aka cireta ko ran mahaifinta, makaranta ma sai ya sakata a jnda karatunta zai lalace ba dan kuma ba shi da hali ba, sai dan an shiga tsakani”
Amma ta kalleta tana nazarin kalamanta ita kanta a yanzu ta yarda ba a banza Appa ya canjawa Hurriya makaranta ba, yarinyar da yake alfahari da basirarta har yana ikirarin fitar da ita waje ta yi karatu amman a yanzu ya cireta daga makarantar kudi ya maida ita makarantar government.
“Tun ina Amarya lokacin da aka hade mu, ta taba ce komai ta dade sai na bar mata mijinta, kuma sai ta saka ni na yi nadamar auren Alhaji, har abada kuma ba zata taba son ko ta so yayana ba, domin kallon da take min na yar aiki be canja ba a idonta, sai ta kakkabe ni kamar yadda ake kabe tabarma a gidan da yardar Allah, tun da na ci amanar ta sai na gani”
Hawaye ya sauko mata.
“Gashi kuma na fara gani, Wallahi da na san zuciyar Hajiya Kaltume ta kai haka da ba zan yarda na auri Alhaji ba duk kuwa da irin magiyar da zai min”
“Oh Allah mai iko, toh wai haka zaku zuba mata ido shikenan ta kashe Hamad ta ci bulus”
“Ba mu da tabbacin ita ta kasheshi, ba Hamad din muka gani ba balle ya fada mana ita ce ko ba ita ba, ko da ma ance yana raye ba lallai ne ya gane ita ta aikata ba, kuma ba jami’an tsaro suka kamata ba, ba mu da wata hujja ta cewar ita ce kawai dai zato muke yi”
Hindu ta sauke ajiyar zuciya ta yi tagumi.
“Toh ni Kam Alhamdulillah ina da kishiya amman Wallahi ba kamar ta ki ba, ba a aure aka aurota miye laifinki wani yace kar ta iya kula da mijinta, ba mai aiki ba namjji ko uwarki aka hallata masa aure Wallahi wani sai ya aureta balle kuma mai aiki, har yaushe zaka dauki hakki ka dorawa kanka”