Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Khairy ta tashi ta shige dakinta da gudu tana kuka, Hajiya Kaltume kuka take sosai kamar yadda kukanta ya saka yar autarta Ruma kuka.
“Hajiya ko zaki ma su Baba Musa da Baba Lawal a bawa Appa hakuri”
“Babu wanda zan yi ma magana Ruma, babu wanda be san abun da ake ciki ba amman ba su yi kokarin sasantawa ba, ba zan kai kukana a gurin kowa ba, Wallahi hakki ba zai taba barin iyami ba ba zata taba ganin daidai a rayuwarta ba”
Ruma ta dubi Mahaifiyarta cikin rashin fahimta inda uwarta ta dora.
“Hajiya Amma bata gidan nan fa, taya wannan issues din ya zama laifinta? Wata kila ma dai kisan da kika saka ka yi ma Hamad ne nake bibiyanmu…!”
Hajiya Kaltume ta kalleta ta sauri ta buge mata baki.
“Kul…. Kul… Kul… Kika sake furta magana irin wannan, kul… Zuciyarki ta sake raya miki wani abu makamancin wannan… Ni ban kashe Hamad ba ban kuma ce a kashe shi ba, su suka aikata a karan kanku dan haka babu zancen bibiyar hakki a nan, Iyami kuma ita ce silar komai tun farko dole na fadi haka, ke yarinya ce ba zaki gane abun da nake nufi ba, kuma ba zan bawa Alhaji Hakuri ba, ba kuma zan nemi kowa ya shiga maganar aurenmu ba, da yardar Allah sai Alhaji ya kawo kansa yana kuka yana rokon na yafe masa”
Ruma ta kalli Hajiya Kaltume domin ta gama fahimtar inda ta dosa, ta san kuma wanda yayi nisa baya jin kira mahaifiyarta ba zata taba fahimtarta a yanzu ba, dan haka ta share hawayenta ta tashi ta bi bayan yar’uwarta.
“Duk yadda za’ayi na gyara al’amurrana sai na yi sai dai na rasa komai amman ba zan zauna na zuba ido ina kallon abubuwa suna tafiya ba daidai ba, ni da mijina shekara da shekaru kuma ace ni zan koma baya?”.
Ta share hawayenta wasu na sauko mata, zuciyarta na da yakinin zata iya wannan yakin kuma ta ci nasara, bin bokaye da yan bori ne take jin yanzu ta fara domin ta gwada ta ga riba.
MOMY POV.
Miwan ya sauko hannunsa daya a aljihu dayan kuma yana rike da wayar da ake yayi yar zamani, daga inda Momy take zaune ta dago kai ta kalli danta cike da farinciki da kuma alfahari.
“Kamar jiya kuka bar kasar nan gashi yanzu har ka dawo Alhamdulillah”
Miwan ya zauna yana murmushi gashin kansa yayi tsiro kamar wani dan kwallo.
“Momy muma muna alhari da ke wannan duk jajircewarki ce, da mun bi ta Appa ba zamu yi masters din nan ba, Namra ma ya kamata ta je ta yi, domin yanzu degree ya zama ruwan dare masters ce ke dan karawa mutum girma”
“Ita ma zata yi ai In Shaa Allah, da zarar abubuwa sun daidaita zata yi”
“Wai me yake damunta ma? Tun da na dawo ban taba ganinta a falon nan ba ba”
Momy ta aje cup din lemu dake hannunta.
“Ina ce shekaranjiya ma mun yi maganar nan da kai?”
Ya dan daga kafadunsa.
“Na ji ni ma ban so Captain ya auri Hurriya ba, amman ya zamu yi? Tun da mai faruwa ta faru? Kuma ba ga ta inda wannan abun zai zame mata abun damuwa ba har da su boye kai a daki”
“Saurayi biyu Namra ta rasa saboda Hurriya, na farko be wani dame ni ba ni ban ma wani san shi ba, amman Captain har yanzu zuciyata ďaci take saboda be auri Namra ba”
“Amman ya nuna yana son Namra ne? Ko kuma dai ke kuke ta hasashenku ne? Wata kila ku kuka saka mata rai ita din ba shi take ra’ayi ba, ko dai yaya ya kamata ta hakura mana tun da mai faruwa ta faru”
“Daman ai dole hakura zamu yi, amman tabbas yayana da Captain sai sun yi nadamar abun da suka aikata, ba dai dangin Iyami ba ne?”
“Ta ji sauki wai?”
“Waya san mata can ita ta sani, ni har yau ban leka gidan ba, ko last time da mahaifinku zai tafi sai da ya ce min ko zan je na ce Allah ya tsare ni da zuwa gidan Iyami, shekaranjiya ma ina jinsa yana zancen zai biya min ummara ni da Sapna na san ba zai wuce dafe dafe ba daga karshe yace albishir din maida Iyami ne”
Miwan ya dan dago ya kalli Momy yana murmushi
“Ni Allah har mantawa nake ina da yar’uwa Sapna wai tana nan dama”
“Da ta mutu ai da ka sani kamar yadda ka sani a lokacin da Salma ta mutu”
“Haka ne kuma, mutuwar Salma ta ba ni mamaki Wallahi haka sidda”
“Babu yadsa mutuwa bata zuwa ga bawa ai, ba a mamakin mutuwa sai dai fatan kyakkyawan karshe”
Ta tabe baki ya cigaba da taba wayarsa. Momy kuma ta kawar da fuska tana wani tunanin na dabam.
CAPTAIN POV.
Abubuwa da yawa be saka ran Ammy zata yi ba zai a auren nan su take ta kokarin shiryawa a kuraren lokaci ciki har da Walima da wanki ango da kamu, mutane da yawa da ta Boyewa zancen auren yanzu su take aikawa da katin gayyata wasu kuma tana sanar musu ta waya yadda za’ayi bikin, tana yin haka ne kawai saboda farinciki danta, so take kallon da yake Mata na macen da bata son aurensa ya tashi zuwa mai son cigabansa ba kuma dan tana son Hurriya ba sai dan haka ya zame mata dole ta aikata a matsayinta na uwa.
Captain kawai ya zauna ne yana kallon yadda abubuwa suke gudana, wasu daga cikin cousins dinsa da friends sai a yanzu suke kiransa suna taya shi murna da yawansu sun fi tambayar yaushe ne dauren auren idan ya fada masu an daura sai su yi ta mamaki wasu kuma su ce ya boye musu wasu su ce be gayyace su ba, haka dai yayi ta fama wani gurin ya samu wanke kansa wani kuma sai dai ya kyalesu su yi ta complain. Ran Momy be kara baci ba sai da ta ga mini iv da Ammy ta saka ayi mata ta raba na gayyatar walima da wunin biki, bakinciki be bar Momy ta leka walima ba balle wunin biki kirkiri ta fitar da hassadarta a fili, daman ta wani bangaren tana ganin kamar har da laifin Ammy na bari Captain ya tare da Hurriya bata bude masa wuta ba, ta bangaren Ammy kuma tana ganin kamar Momy ta zafafa da yawa domin ita ma da take uwa ta hakura ta bar abun a zuciyarta balle Momy da take kanwar uba, a yanzu take kara yarda da zancen Captain ba, Momy ba tana bakinciki auren ne saboda ba Namra ba ce not just because of Hurriya tana yar mijinta.
A family House din Mijinta Ammy ta yi Walima da wunin, ba daga arewa kadai ba har daga kudancin Nigeria da yan’uwanta da na mijinta da suke wajen kasar nan da wasu daga matan abokan kasuwanci Mijinta sai da suka yanke uzuri suka halarci walimar da wunin biki, saboda sun san daga Daddy har Ammy ďa ďaya suke da shi Captain balle su ce idan ba su samu zuwa a wannan ba idan wani bikin ya tashi za su tafi. And ba su taba aurar ba sai akan Captain saboda haka dole ayi musu kara.
Walima aka yi ta gani ta fada, idan baka da gate pass baka isa ka shiga ba, kana shiga kuma za a bude bayan motarka ka a zuba maka gift din Walima da kaza daya da aka soya aka yi package dinta da kyau, idan kuma baka da mota za a baka abun ka a hannuna ne ta inda Ammy ta banbanta abun ta gurin raba abun da yake cikin jakar kayan walimar ne, masu hannu da shuni ta saka musu manyan abubuwa na masu arziki, wadanda aka raina capacity dinsu kuma sai ta saka musu na su kanana, Ammy da kanta ta aika da motoci aka dauko Hurriya da yan gidansu, daman ta saka an sanar musu da abubuwan da ta shirya tun gabani zuwan ranar, Ammy bata son kowa ya gane Hurriya bata gani dan haka ta fada mata ta yi acting smart kar ace ďanta ya auri makauniya. In a code way aka yi komai na walimar sai dai haka be hana wasu noticing something is wrong with Hurriya ba saboda yadda bata respond ma mutane idan aka yi mata murmushi, and bata iya daga kai ta kalli mutane da kyau, team babu ruwanmu da gulma ba su kula ba har ayi aka gama.