Huriyyah Book 1 and 2 Complete Hausa Novel
Ya tsaya daga tafiyar da yake.
“Why are you telling me this Ammy?”
“Bari na tambaye ka tsakaninka da Allah… Shin zaka iya auren yarinyar nan a lokacin nan?”
“Ba zan iya ba, ko a gaba balle a yanzu na jinjinawa Captain yayi kokari kuma yayi jihadin da ba kowa sai iya ba”
“To me yasa ba zaka taya ni fada masa gaskiya ba? Ka lurar da shi ta wani gurin da kurakurai suke mana”
“Idan na yi hakan zai bata alakarmu da shi ne akwai, ba zai fahimta ba kuma sai yi tunanin na zo ne saboda na daga masa hankali na hana shi zaman lafiya da Hurriya ko sonta yadda ya dace”
“Cikin Hikima zaka yi Salim, wannan taimako a gareni da kuma shi kansa abokinka, Wallahi bana son auren”
“Amman an riga an daura ai Ammy meyasa baki hana ba kamin a daura”
“Babu wanda ya sanar min da cewar za’a daura, mahaifinsa ya shigo gida ne kamar haka ya sanar mana sun je jaje kuma yin nemi aurenta an ba su har an daura, yarinyar da bata gani ma amman idonsa ya rufe ya rantsa sai ya zauna da ita”
Salim ya sauke ajiyar zuciya ya saka hannayensa aljihu.
“Yarinyar nan bata cancanci Captain ba ko kadan ko da kuwa bata aikata ba, ya kamata ya lura da yadda duniya take kallonta a yanzu, amman kin san Captain ba a masa daidai, kawai dai mu saka masa ido zai fi”
“Kai ma dai ba zaka iya ba kenan…! Babu wanda yake iya fahimtata”
Ta cige baki tana kallon wani ward din dake facing dinsu, Salim ma gurin yake kallo sai dai kowa da kalar tunaninsa. After Salim ya fice Captain ya tashi zaune
“Ina fatan dai ba wata matsala ta ja rashin lafiyarka ba?”
“Aa rashin lafiya ne kawai babu wata matsala Daddy”
“Ma Sha Allah, daman ina da niyar kira na maka albishir sai kuma Ammynka ta sanar da ni ciwonka a take tawun giwa ya take na rakumi”
“Akan Adam ne?”
“Ka ga video ne?”
“Aa zan sauke kenan ka kira ni, amman Salim ya fada min Adam din ya aikata abun da ake bukarta ya aikata”
“Ya aikata yayi kamar yadda muke bukata, mahaifinsa ya turo min da video, domin ya kara kira bayan ya tafi gurin mahaifin yarinyar be yi nasara saboda na yi waya da shi na fada masa duk irin magiyar da za su masa kar ya aminta da su, sai kuma ya dawo ni ma yana rokona sai dai ban bashi wata amsa ba bayan wanda ka bashi, kuma na tabbatar masa a jibi Monday za a shiga kotu, sai gashi yau ya turo min da video”
“Na jidadin hakan Daddy thank you very much, da goyon bayanka ne na samu wannan nasarar, zan yada video, na san hakan zai wanke yarinyar nan ko da ba gaba daya ba, zata yi farinciki idan ta ji i wish ni zan fada sanar mata ma saboda na mata wannan alkawarin”
Daddy yayi murmushi.
“Yaron ma abun tausayi, kaddarori ne kawai da rashin tunani irin na yaran yanzu, jiya ma na yi waya da Hajiya nake tambayarta zuwa yaushe ne ya kamata ace Hurriya ta tare saboda damuwa a yanzu matsalar idonta ne, ina son ta dawo karkashin ikonmu ne gaba daya sai a nema mata maganin hakan zai fi armashi da ace tana gidansu za’a nema, sai dai Hajiya tace min mu daga kafa zuwa nan da kwana biyu zata tafi ita da Hajiyar Maru sai su yi maganar tarewar domin abun ne da ya danganci mata, kuma na bata sako ta fadawa iyayenta mu dai yarinya muka aura ita muke so, ba dan mun raina arzikin ubanta ba, amman ba ma bukatar komai daga garesu zamu zuba komai daga nan garin da zata zauna har zuwa inda aiki zai kaika”
“You’re best Dad ever samun irinka Daddy sai an tona, Hurriya ta yi sa’ar samunka a matsayin suruki”
“Akan kawo mana neman taimakon auren wasu ma mu yi balle kuma naka? Jamal ba dan kana son yarinyar nan ba no a kashin kaina yarinyar ta ba ni tausayi na halin rayuwar data samu kanta, ina tunanin idan da ace yata ce ya zan ji, yarinya karama an bata mata rayuwa da suna akan abun da bata aikata ba”
“Akwai matukar tausayi Daddy, amman Ammy ta kasa gane haka”
“Zata gane Son.. Zata gane.. Matsalar da aka samu Ammynka mace ce mai matukar son riya da alfahari ba irin wannan auren take son ayi ba, kuma su mata suna da wannan dabi’ar da rike abu balle kuma bata son yarinyar, dole sai ka yi hakuri with time zata fahimceka..”
“Ina fatan haka”
“Bari na barka ka huta, zan aikawa mahaifinta da video yanzu, na san ba zai masa dadin kallo ba, amman ya kamata ya san gaskiya kuma ya san matakin da zai dauka ko dan nan gaba, amman da zaka hakura da yadawar wata kila zai fi, ya zai ji idan aka ce yarsa ce ta aikatawa yarsa haka?”
“Daddy idan video be fita ba taya za a wanke Hurriya? Cikin alkawarin da na yi mata na fada mata cewar sai na yada wanda yayi mata wannan abun fiye da yadda aka yada hotunanta”
“All the best… Get well soon”
“Thank you Daddy”
Ya fita daga video call din ya sauke video da Salim ya turo masa yana kalla, a take ya ji kamar an yaye masa ciwon dake damunsa saboda farincikin yadda Adam ya bada labarin komai a video kamar yadda ya fadawa Captain da iyayensa banbancin wacan video da wannan, wannan video shi ya dora shi da kansa a shafinsa na tiktok kuma yana sanye da tufafi na kamala har da hula kamar mutumen arziki. Bayan ya gama kallo ya jira Ammy a wayar sai ta amsa tana shigo dakin domin tana daf da kofar dakin ne a lokacin da ya kira wayarta.
“Lafiya? Allah yasa ba jikin ba ne”
Ta karaso gurinsa da sauri. Captain dake jin kamar yau ce ranar angoncinsa ya mikawa Ammy wayar yana dariya.
“Ba shi ba ne, duba wannan ki gani”
Ta karbi wayar ta kunna video ta kalla, sai ta tabe baki ta zauna.
“Still dai ba zai goge hoton tsiraicin Hurriya da yake idanuwan mutane ba, kuma hakan ba zai hana ace kasan yarinyar nan da aka yada hotunan ta da wani saurayi ba? To Captain take auren yaron Engr A A Turaki ba”
Far’ar dake fuskar Captain sai ta soma disashewa, doman yayi tunanin hakan zai cire wani abu daga tsanar da Ammy take ma Hurriya.
“Tun farko kina kiyayya da ita ne saboda kina taya Momy kishi ne kawai saboda tana yar mijinta kuma Momy bata son Hurriya, Namra ma bata sonta, da kunnena na ji komai Ammy, kiyayyar da kike yi ma Hurriya ba na abun da ya faru ba ne kawai idan saboda shi ne ai kaddara ce da bata wuce kan kowa ba”
“Haka ne, shiyasa mahaifinka zai yi mata komai ai, da yar wani mai arzikin ka aura kamar mahaifinka, ai ba zai yarda da wannan ba”
“Shi ma ai be riga ya yarda ba, domin ba a taya masa ba kuma babu tabbacin zai amsa ko akasin haka shi ma yana son yarsa…”
Ya koma ya kwanta ya rufe idonsa…
*** *** ***
Cike da girmamawa Appa ya amsar wayar sukirinsa ta bangaren biyu, suka gaisa cikin mutunci da far’a Daddy ya tambaye shi rayuwa da kuma kasuwa suka ya amsa masa da hamdallar Allah.
“Daman na kira ne akan maganar Hurriya…”
Daddy ya dan yi shiru.
“Akan maganar tarewarta ne?”
“Eh to…ba makasudin kenan ba, amman saboda ka fadi hakan bari na ce har da shi da na bar mata su yi wannan aikin ne”
Appa yayi murmushi.
“Daman ina da niyar na yi maka magana akan hakan, saboda ina neman Alfarmar ka daga mana kafa har zuwa ta samu lafiya, yanzu haka na fara shirye shiryen abun da ya dace ayi ne akan idonta, abun ba zai yi kyau ba amarya da makanta…”
Daddy yayi hanzarin tariyar numfashinsa.
“Ka kawar da wannan maganar, yanzu neman lafiyarta da cinta da shanta a abu ne da ya rataya a wuyan mijinta, kusan shi ne makasudin da ya saka nake son ta tare ai, saboda ya zama tana hannunmu mu zamu yi mata komai, ba lafiyarta kadai ba Alhaji Haruna har wata hidima da zaka yi akan Hurriya tun daga kayan daki har koma mun dauke maka”